Rumbun Qaya page 68

Rumbun Qaya page 68

Rumbun Qaya page 68

 **RQ**

     68

***Har ta gama ringing be daga ba, ya sakè kira no answer, sai ya ajiye wayar yana shafa kansa a hankali, ya kamata ya damu da in da take ko kuwa? Ya tambayi kansa, sai wata zuciyar tace kawai ya share ta, bata chanchanci damuwar sa ba, idan ma karya tayi dole zata dawo, idan ta dawo yana da karfin hujjar da zai iya tura ta gidan yari na har abadah. Be kira Lawwalin ba, dan ya gama yanke be kamata yayi wasting time dinsa akanta ba kuma, sai kawai ya cigaba da sabgar gabansa. 

   Washegari ce ranar da za’a yi masa MRI kamar yadda Dr Mahfouz yace, ranar kuma Raihana taje clearance ta gaya ma LGI dinsu akan tafiyar da zatayi, yace ta rubuta letter zuwa ga co-ordinator din ta state, ta zauna ta rubuta yasa hannu sannan yace ta kai chan headquarter su dake gwarzo road. Daga kumbotson ta wuce taje ta kai ta dade tana jiran wanda zata bawa an ce ya fita gashi bata so ta tafi, hakan ya dauke ta lokaci me tsawo.

  Da laasar ta dawo asibitin babu kowa sai Ya nabeela Ammy sun zo da Adda Maimuna har sun tafi sai Abby ma yazo da safe zai wuce Adamawa. Wani kallo yake mata da ta shigo irin kallon kasa kasan nan, tana sanye da nysc khakhi dinta da white medium hijab sai jacket din da ta dora akan white shirt din ta bar botir din kasan a bude saboda ta sakè sosai. Gaishe da Ya nabeela tayi sannan ta dauki Amna da tazo da su yau kasancewar friday ne da wuri suke baro school, ta zauna akan kujerar tana yin kasa da kanta


“Ba zaki kula ni ba?” 


“Laa wai baki masa magana ba? Tun dazu Aryan yake ta faman kallon hanya fa.”


“Bata da gaskiya shiyasa ta ki magana.”


“A ah, kunya ta take ji, kanwata me kunya ce.”


“Me nayi?” Tace tana kallon sa


  Kayan dake jikinta ya nuna da bakin sa, sarai ta gane me yake nufi amma sai taki cewa komai, har Ya nabeela ta fita ta jawo musu kofar.


“A haka kika je?” Yace yana zuba mata shanyayyun idanun sa dake nuna gajiyawar sa.


“Kalli fa, me sukayi?”


“Babu yar afterdress da naga matan aure na sakawa?”


“LGI dinmu baya yarda asa kayan da ma khaki ba, shiyasa kuma jacket din babba ce sannan Hijab din ma…”


“So yake ya dinga kalle matan mutane ko? Sai naje na tsone masa ido.”


Dariya tasa ya cije baki


“Dariya ma kike?”


“Um um, ba ita nake ba, ya jikin?”


“Da sauki…”


“Anyi scan din?”


“Um anyi, sai jiran result.”


“Ok. Allah yasa muga alkhaiiri.”


“Amin ya Allah.”


“Oya tashi kici abinci amma ki fara chanja kayan nan kafin wannan Dr me katon kai ya shigo yana yashe miki baki.”


“Dr Mahfouz?”


“Shi.” Yace yana hararar ta. Gum tayi bata sakè magana ta, tasa key a kofar sannan ta chanja kayan a gefe yana kallon ta duk da kunyar da take ji haka ta daure, sannan ta zuba abincin tace zata je wajen Ya nabeela ta ci, hanata yayi yace ta zauna taci a gabansa yaga iya wanda zataci, zuwa tayi ta cire key din da tasa a kofar sannan ta dawo ta zauna a kujerar gaban nasa ta shiga cin abincin a hankali. 


    ****Kwana biyu tsakani suka shiga shirye shiryen tafiyar, daddy ya matsa dan so yake su taho bayan two days zai dawo ya koma kan business dinsa dan ya samu sauki sosai yanzu kamar bashi ba. Shirye shirye Ya nabeela take musu da taimakon Kamal da khadija ita ta taimaka ma raihana ta hada abinda zata bukata sannan ta hada ma Aryan din nasa tunda Asibitin sun rike shi sai ranar da zasu tafi sannan direct daga chan airport zasu kaishi. 

   Ana gobe zasu tafi Ammy ta tare a gidan da suka samu saboda zuwa wajen malam sannan tana ganin likitan kwakwalwa a asibitin nasarawa, sau biyu Malam yazo shi da Isa da Awais da Asiya suka sake duba ammyn sannan yace zasu dawo idan ta samu gidan nata. 

    Dukkan su sunzo suna nan Lamido, Hamma Hydar da Babbo Sadeeq sun taho ma Dadah da abubuwan da zata bukata, tare suka dawo da Abby da yaje yayi kwana uku. Daga gida take bayan ta gama hada komai waje daya an saka a mota ta iso gidan nasu, dan madaidacin gida ne me kyau da aka kawata shi da furnitures masu kyau da tsada. A falo duk suka baje ana hira ana rawa cikin jin dadi da farin ciki Ya Nabeela ta kirata tace zata zo ta dauke ta akwai in da zata kaita, da kwatance tazo gidan ta shigo tayi musu Allah ya sanya alkhaiiri duk da taso su zauna a gidan su na asali amma tasan ba zasu yarda ba shiyasa ba batayi ma Aryan maganar ba musamman da yake fama shima da kansa Amma da ya san abinda ake ciki ba lallai ya bari ba saboda tsawon lokacin nan ya ajiye gidan ne saboda su. Tare suka fito da raihana tace zata dawo da ita, ita raihana bata san ina zasu ba sai da taga sun dauki hanyar saloon din nan da ta taba kaita.


“Dan Allah kanwata wata alfarma nake nema.”


Tace sanda suka iso daidai saloon din tayi parking tana kallon raihanan da ita ma ita take kallo da alamun go ahead


“Aryan ba zai iya dorar da wata rayuwa me dadi ba, dukkanin rayuwar sa a fadi tashi yayi ta daga wannan sai wannan, ke kanki nasan kin lura da hakan a dan zaman ki dashi, dan Allah Raihana ki taimaki maraicin sa ki zamar masa sanyi zuciya da na idaniya, a yanzu gaba daya hankalin Aryan yana gareki, Kiyi yadda zakiyi dan Allah Kisa ya manta komai da ya faru, nasan zaki iya domin yana sonki har bansan adadin yawan son ba.”


“In sha Allah zanyi iya kar kokarina Ya nabeela.”


“Yawwa, Nagode sosai, Allah ya baku zaman lafiya da zuria dayyiba. Ki taske sosai ki kama mijinki a hannu, karki tsaya wannan kunyar dan Allah, Yanzu ba lokacin da bane ba, ki nunawa mijinki soyayya shine cikakkiyar wayewa, akwai wani e-book da nake dashi, zan tura miki ta whatspp ki daure ki duba ki karanta kinji? Zaki amfana sosai game da rayuwar aure a zaman ance, domin maza yanzu basa son kunbiya kumbuyar nan, sai kin taske kin dage sannan ki hada da addua zaki ga komai yana tafiyar miki yadda Kike so.”


“In sha Allah, Nagode Ya nabeela.”


“Karki damu, ki dauke ni a matsayin babbar yayar ki mace ba wai Yayar Aryan ba, ni dama na dauke ki ne a matsayin kanwa mace da bani da Ita, mu hade kanmu karki dinga jin nauyi ko kunya ta. Duk abinda ya shige miki duhu ki sanar dani in sha Allah zan warware miki komai.”


Godiya tayi mata suka fito suka shiga saloon din, tasa a gyara mata gashin ta sannan a wanke mata kafar ta aka gama suka fito ta kaita wani clothing store ta zabar mata hadaddun sexy kaya masu kyau da tsada na yan gayu sannan suka wuce gidan ta hada su cikin kayanta hade da wani hadadden gel a most have for every married woman wallah(wanda ba’a fadan sunan sa sai an biya 😜😅)lol. Daga nan gidan su ammyn ta maida ta, lokacin magriba ta kusa ta ajiye ta kawai ta wuce gida. Kamal na tare da Aryan ta fada masa dama a wajen ammyn ta zata kwana yau shiyasa bata koma asibitin ba, tayi sallar magriba sannan ta zubo tuwon Dadah me dadi taci ta zauna aka dasa zaman hira tana manne da Ammyn kamar zata shige jikinta. Sallar ishai ce ta sakè tashin su akayi sallah sannan aka zo aka sake zama Dadah ta tambayi Lamido akan case din Muhammad be ce komai va saboda ba hurumin sa bane ba kuma aikin sa be bashi dama ba amma yasan sai an ladaftar dasu idan ma zaa kyale su tunda Aryan din Allah ya takaita babu wani abu da ya faru. 


***Yana tare da Kamal amma rabin hankalin sa na ga tunanin Raihanan, ya rasa dalilin da yasa yake jin ta sosai a yan kwanakin nan ko tafiya tayi sai yayi ta tunani ya gaza sukuni har sai ta dawo, ya samu saukin fushin nan nasa sosai dan ya lura kamar yanzu ma babu abinda yake tunzura shi shiyasa yayi zeroing mind dinsa daga tunanin duk wani abu da zai hana mishi farin ciki. Shi yasa ko maganar zainab da muhd bata wani dad’a shi da kasa ba dan ko da Ammy suka zo masa da maganar kin bari yayi tayi tsawo yace babu komai ya wuce, shi da Kamal din ma zai yadda da sakin su yasa akyi suje su karata da halin su.


“Nasan be kamata nayi maka maganar nan ba, kuma nasan be kamata nayi bincike akai ba, amma har yanzu babu labarin Hajiya zeenat fa.” Yace yana son karanta wani abu a fuskar Aryan din wanda zai zame masa cikar aikin da yake akai.  Dage kafada Aryan yayi, ya sa hannu a gefensa ya dauki envelope din dake ajiye da yasa Hashim kawo masa ya mikawa kamal din


“Nine na dauke ta na kaita wani kauye, sannan nayi amfani da hakan na samu enough evidence din da duk balain su basu isa su wanke ta ba.”


“Wait what? Ka dauke ta?”


“Yes of course.”


“Kana da hankali kuwa Aryan? Kana son saka kanka a matsala ne ko me? Kasan irin neman da ake mata Yanzu haka? Sannan kasan dama kaine prime suspect nasu?”


“I don’t care, na samu abinda nake so ai, kuma ta riga ma ta gudu, bansan ina take currently ba, but duk abinda na samu yana cikin envelope din nan.”


“Baka bi hanya me kyau ba ta samu information din.” Yace yana ajiye envelope din a gefen Aryan din


A dan kufule Aryan din yace


“What ever, na dai samu.”


“I can’t use it, ba zan iya amfani dashi ba gaskia.”


“Ok fine, don’t use it. It’s your choice after all. Ni dai ka sani nayi abinda zanyi, kana tunanin idan kabi right way din zaka samu abinda kake so?”


“Idan kuma tayi denying fa, lawyer ta yace an matsa mata ne ko an firgita ta. Duk abinda ta fada din zasu ce ta fada ne under duress, kana tunanin alkali zai karbi shaidar?”


“I don’t care anymore kamal, ya karba ko kar ya karba. All I know shine nayi abinda nake ganin shine daidai, duk wanda be yarda ba ban damu ba.”  Yace a hasale ganin kamar Kamal din yana son nuna masa abinda yayi ya tashi a tutar babu.


“Iya gaskiya ta na fada maka, wannan shine abinda ya kamata ka sani before putting your self in to this mess.”


“Then leave me with my mess, ka barni nayi duk abinda naga dama, it’s my life and my choice.”


Sai ya dafe kansa da yaji ya sara masa, ya runtse idonsa ransa na masifar baci. Turowa da condition din nasa Kamal yayi, sai kuma yaji nadamar abinda ya farun ya tashi da sauri ya rike hannun Aryan din


“Are you ok?” Yace yana leka fuskar sa. Be yi magana ba sai rike kan da yake yana runtse idon sa. 


“Let me call the Dr .”


Ya juya ya fita, suka dawo tare da Dr din ya duba shi sannan yace


“A daina dawo masa da duk abinda zai bata mishi rai, jinin sa zai iya sake hawa ko yaushe, bama so mu dora shi akan drug na bp din Shiyasa ma tun farko bamu fara ba, please a kiyaye.”


“In sha Allahu dr, za’a kiyaye.”


Fita yayi ya ja musu kofar, da kallo kamal ya bishi yana jin rashin kyautawa abinda yayi.


“I’m sorry.” Yace yana daga tsaye


“It’s ok, I’m sorry for acting rude.”


“No nine me laifi, ba haka ya kamata nayi ba, in sha Allah zan duba zan kuma san me yakamata, I will handle da case.”


“Thank you.” Yace yana juya kansa zuwa dayan side din. 


Wayar sa ce tayi kara, yana ji yaki juyowa har sai da Kamal din ya duba sannan yace masa


“Raihana ce.”


Hannu yasa ya karba ya daga shi kuma Kamal din ya fita.


   Da safe suka tashi kamar babu abinda ya faru, da kansa yaje toilet yayi alwala hade da wanka yazo ya saka kayansa sannan yayi sallah. Ya nabeela ce ta fara zuwa dauke da breakfast, zuwan ta yasa Kamal tafiya gida yayi wanka sannan suka dawo tare da Khadija itama dauke da breakfast din, tare suka ci dukkan su a dakin sannan Ya nabeela da khadija suka hau kwashe kayan dakin suna hade su waje daya, komawa yayi kan gadon ya dauki wayar sa ya kirata lokacin ta fito daga wanka tana shafa mai, gaishe shi tayi ya amsa yana tambayar ta su Ammy sannan yace mata malam Yahya zaizo ya dauke ta. Sallama sukayi ta karasa shiryawa a gaggauce ta dan sha tea da cake Malam Yahya yazo ya dauke su dukkan su ita da Dada da Ammy su kuma yan mazan suka hau mota daya tare da Abby. Suna zuwa sun gama shiryawa har sun kai kaya mota Kamal yaje yayi clearing komai an yi discharging nasa. Motar Ya nabeela suka shiga Kamal din ya tuka su khadija na gaba Aryan da Ya nabeela na baya suka nufi airport din dan sai sun fara zuwa Abuja sannan zasu tashi ta chan. Karfe goma jirgi zai tashi dan haka sanda suka je tara ma har da rabi a gaggauce sukayi komai, raihana ta rungume Ammy sai kuka. Duk sai ta basu tausayi, Abby ne ya korata ta dole tabi Aryan din tare da Kamal da zai wuce Abujan shima.



*_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_*



*ZAFAFA BIYAR BACTH A*



1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350

 *(Bilyn Abdul)*



2.. _KAI MIN HALACCI_ 350

*(Miss xoxo)*



3.. _BURI DAYA_ 350

 *(Mamu gee)*


4... _DAURIN BOYE_ 350

*(Huguma)*


5... _SAUYIN KADDARA_ 350

*(Hafsat Rano)*


_Duka biyar 1500_


*___________________________*

    


*_ZAFAFA BIYAR BATCH B_*



1... _DAURIN GORO_ 350

*(Hafsat Rano)*


2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350

*(Huguma)*


3... _QAUNAR MU_ 350

*(Mamu gee)*


4... _IGIYAR ZATO_ 350 

*(Miss xoxo)*


5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350

*(Bilyn Abdull)*



_Duk biyar 1500_


*_____________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BATCH C_*


1... _MIN QALB_ 350

*(Mamu gee)*


2... _SARAN ƁOYE_ 350

*(Bilyn Abdull)*


3... _KIBIYAR AJALI_. 350

*(Miss xoxo)*


4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350

*(Hafsat Rano)*


5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350

*(Huguma)*


_Duk biyar 1500_


*____________________________*



*_ZAFAFA BIYAR BACTH D_*


1... _ALKIBLA_ 350

*(Huguma)*


2... _DALAAL_  350

*(Miss xoxo)*


3... _UBAYD MALEEK_ 350

*(Mamu gee)*


4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350

*(Hafsat Rano)*


5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350

*(Bilyn Abdull)*



_Duk biyar 1500_


*____________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BATCH E_*


1... _SO DA ZUCIYA_ 350

*(Mss xoxo)*


2... _TAKUN SAAKA_ 350

*(Bilyn Abdull)*


3... _HALIN GIRMA_ 350

*(Hafsat Rano)*


4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350

*(Huguma)*


5... _DEEN MARSHALL_ 350

*(Mamu gee)*



_Duk biyar 1500_


*______________________________*



*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*


1... _BAKAR INUWA_ 350

   *(Bilyn Abdull)*


2... _RAYUWAR MACE_ 350

    *(Hafsat Rano)*


3... _NOOR ALB_ 350

     *(Mamu gee)* 


4... _MASARAUTA_ 350

    *(Mss xoxo)*


5... _KUFAN WUTA_ 350

    *(Huguma)*


_Duk biyar 1500_


*_____________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (COMPLETE )_*


1... _FARHATAL QALB_

*(mss xoxo)* 400


2... _GURBIN IDO_

*(Huguma)* 400


3... _SANADIN LABARINA_

*(Hafsat Rano)* 400


4... _INAYAH_

*(Mamu gee)* 400


5... _BABU SO_

*(Bilyn Abdull)* 400


_Kuɗinsu a yanzu 2k duk biyar_


*BATCH F



*RUMBUN QAYA🔥


*DAUDAR GORA*🔥


*IDON NERA*🔥


*A RUBUCE TAKE*🔥


*KI KULANI*🔥


*_uhmmmm_*😊😊😊😊😊😊😊😊😊😊


*Nasan zakuce ya da murmushi haka?*


*Wanda bai shigo ba bazai gane ba*


*Sai kin shigo daga ciki zaki gane me nake nufi*☺️☺️


*KE DAGA JIN SUNAYEN LITATTAFAN MA KADAI KASAN CEWA AKWAI WANI BABBAN ABU MAI MATUQAR JAN HAKALI TATTARE DASU*


*KINA NEMAN INDA ZAKI HUTAR DA KWANYARKI?*


*KI SAMU ZUNZURUTUN NISHADI DA ILIMI?*


Littafi daya---400

Biyu---600

Uku----800

Hudu-----1k

Biyar din duka----1200


IDAN AN GAMA SU DOCUMENTS DINSU DUK DAYA 400 NE GUDA BIYAR DIN 2k 


*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*🔥🔥🔥🔥🔥


0022419171

Maryam sani

Access bank


*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*


09166221261


🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪

*Ina yan uwa 'yan nijer?*

*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*


+227 90 16 59 91


Littafi daya---450CFA

biyu---650CFA

uku----850CFA

hudu----1050 CFA

Biyar----1250CFA


*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*


*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*


*Thanks for choosing us*🔥

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post