Wanda ya tafi aikin Hajji da Kafa a Pakistan

Wanda ya tafi aikin Hajji da Kafa a Pakistan

Wanda ya tafi aikin Hajji da Kafa a Pakistan
Reuters/BBC Hausa
Yayin da maniyyata sama da miliyan ɗaya da 300,000 da suka je Saudiyya daga sassa daban-daban na duniya suka fara gudanar da ibadar Aikin Hajji a bana, maimakon hanyar da aka saba bi, wani ɗalibi daga Pakistan ya je hajjin ne a ƙafa.

Ya shafe tsawon wata shida yana tattaki kafin ya isa ƙasar Saudiyya daga bisani.

Usman Arshad a yanzu yana cikin miliyoyin mahajjatan da ke gudanar da wannan ibada wadda duk Musulmi yake fatan zuwa idan ya samu iko.

Ya tafi Makka da ƙafa, ya bar Pakistan, ya wuce Iran zuwa Hadaddiyar Daular Larabawa kafin ya isa Saudiyya.

Tafiyar ba ta zo da sauƙi ba ga Arshad, ya fuskanci ƙalubale da dama musamman ta fuskar yanayi.

"Kowane musulmi yana da burin zuwa Makka wata rana, domin ziyartar dakin Ka'aba," in ji Osman.

Ya kara da cewa, “A lokacin tafiyata, na kan kwana a duk wani masallaci ko otal da na gani, amma yawanci ina kwana a kan tanti".


nBC Hausa


Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post