An tabbatar da mutuwar mutum daya sanadiyyar Mashako.

An tabbatar da mutuwar mutum daya sanadiyyar Mashako.

 

An tabbatar da mutuwar mutum daya sanadiyyar Mashako.
BBC/Getty Images

Hukumar kula da babban birnin tarayya, Abuja ta sanar da bullar cutar mashaƙo ko kuma diphtheria a wasu sassan birnin.

Jaridar Punch ta ruwaito daraktan sashen kula da lafiyar jama'a a hukumar, Dakta Sadiq Abdulrahman yana sanar da ɓullar cutar.

Abdulrahman ya ce tuni cutar ta kashe wani yaro ɗan shekara hudu, inda ya kara da cewa ɓullar ta tun farko a jihohin Legas da Ondo da kuma Kano a watan Janairu, cutar ta sanya cibiyar yaƙi da cutuka (NCDC) ta Najeriya kai ɗauki a matakin ƙasa gaba ɗaya.

Diphtheria, cuta ce da ke janyo ƙwayoyin cuta masu guba kuma suna sarƙe numfashi, da janyo matsalolin bugun zuciya, har ma suna iya kaiwa ga mutuwa.

Daraktan ya ce an tabbatar da bullar cutar ne bayan gwaje-gwajen da aka yi wa samfuran wadanda ake zargin sun kamu a wani yanki da ke kusa da Dei-Dei.

“Makonni biyu da suka wuce, mun samu bayanai daga wani yanki na birnin Abuja inda aka yi zargin mutum takwas na ɗauke da alamomin cutar kuma hakan ya sa hukumarmu ta dauki samfuran wasu mutane.

Ya buƙaci mazauna yankin su bayar da rahoton duk wani baƙon alamu, musamman kalubalen numfashi ga hukumomin da abin ya shafa kuma ya shawarci su kula da tsaftar jiki da ta muhalli.

Abdulrahman ya ce hukumarsu na hada kai da jihohi makwabta, domin daƙile yaɗuwar cutar ta hanyar sanya ido kan iyakoki.

Haka kuma, babban sakataren hukumar lafiya matakin farko na Abuja, Dokta Yahaya Vatsa, ya yi gargadin cewa mutanen da ba a yi musu alluran riga-kafi ba wadanda ke zaune a wurare masu cunkoso da rashin tsafta na cikin hatsarin kamuwa da cutar mashaƙon.

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post