Tabarmar Ƙashi page 7 by H U G U M A

Tabarmar Ƙashi page 7 by H U G U M A

 

Tabarmar Ƙashi page 7 by H U G U M A

*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔

             Page 07

*Arewabooks:huguma*

https://arewabooks.com/u/huguma

         "yayanki ya saka hope da yawa a kanki,ya kambamaki da yawa,Allah yasa dai zaki fishsheshi" sãahar dake tsakiyar duniyar tunani ta tsinciki maganar farheen kaman daga sama. Kadan ta waiwayo ta dubi farheen,kamar zatace wani abu sai kuma ta fasa,ta sake maida kanta ga tuqin,wanda har suka isa asibitin bata kuma cewa uffan ba.


            Tunda suka shiga dakin suka gaisa da mara lafiyan da relatives na anty farheen,sai ta kama hannun khalifa suka fita a dakin,saboda idanun mutum biyu da suka fara uzzura mata,zata iya cewa tasan daya,saboda tana ganin pictures dinsa cikin hotunan farheen,dayan ne batasan daga ina yake ba,amma tana kyautata zaton dan uwan mijin thurayya me haihuwar ne.


             Ta bayan asibitin suka bi ta fara shawagi cikin asibitin,dukka guraren da take bi din gurare ne da babu yawaitar mutane sosai,sai majinyata jifa jifa,abinda ya sake karya mata zuciya,tana sake godewa ubangiji da ya barta da lafiyarta bata salwanta ha,tabbas inda burin ADAM yakai ga cimma gaci,tayi imani dari bisa dari cewa har kamar wannan lokacin itama tana cikin jerin sahun wadanda zasu qulla kyakkyawar alaqa da asibiti,idan ma bata samu gurbin zama a cikinsa ba,zaman da ba wanda yasan ranar yankewarsa da ubangijin daya qaddara mata komai.


           Tafi tafi sai gata ta bulla ta bangaren 'yan haihuwa,cikin jiki da zuciyarta taji tana mararin shiga ta basu gudunmawa,don ta tabbatara akwai tarin mata masu raunin gaske a wajen,saidai ta manta cewar yau din bata riqo koda purse ba bare ta fito da kudi. HIBBA HASHIM ta tuna,wata qawa ga afifa dinta,idan bata manta ba kamar ta taba jin afifa na maganar anan take aiki,saita koma gefe daya ta tsaya,ta kunna wayarta wadda tun daren jiya take a kashe. Bata gama daidaita ba saqonnin kar ta kwana suka fara turereniyar shigowa da baquwar number da bata sani ba. Qaramin tsaki taja ta share saqonnin ba tare data duba ba,ta kira afifan. 

 

          Ta bata tabbacin a nan take,kuma ana samunta a yau din,cikin minti biyu ta kira mata ita,sai gata a bakin gurin,fuskarta fal fara'a. Tanason sãahar,tana masifar burgeta,gayunta kyanta da kuma iliminta,macace me ajin da jerawar mutum kadai da ita ya isa ya sake siya maka daraja da aji,don haka cikin girmamawa ta yiwa sãahar jagoranci zuwa gurin.


           A hankali take takawa,jiki da zuciyarta gaba daya sun raunana,tsohon ciwon dake danqare a zuciyarta ya fara balle kansa,wannan ya qaranta walwala sosai daga fuskarta.


            Muryar wata nurse shine abu na farko daya fara dukan dodon kunnenta,fada take sosai kamar me shirin antayawa matar dake tsaye a gabanta dauke da tulelen ciki zagi,ba abinda jikin matar keyi sai rawa,tana kuma share hawayen dake zarto mata


"Nidai don girman Allah malama kiyi haquri,ki bani gado,idan na haihu koma meye sai ayi,amma yanzu inajin haihuwata a kusa,koda yaushe zan iya haihuwa"


"To ina ruwan wani?,ki haihu din mana,wanda yayi miki cikinma bai damu ba bare mu da rana tsaka muka ganki dashi" saita juya tana niyyar wuce matar.


           Cak sãahar tayi a wajen,ta gagara zama samam kujerar da hibba ke mata tayin zaman,a nutse ta dauke manyan fararen idanunta daga kan matar zuwa kan hibba


"Me ya samu waccan matar" baki hibba ta tabe


"Kin ganta nan,ta kawo kanta asibiti da sunan haihuwa,amma ko pant din da za'a sakawa jariri babu,bare ayi maganar katin da tayi awo kudin gado da sauran abubuwan da ba gwamnati ce take biya ba,da aka tambayeta ina mijin sai tace ta baroshi gida yana bacci,muka ce lallai sai yazo,saboda yaronta breach ne,zamuyi qoqarin gyara masa kwanciyarsa,idan an samu nasara shikenan,idan ba'a samu ba dole sai ya biya kudi anyi mata C.S. Dajin haka hankalinta ya tashi,muka bata aron waya ta saka numbers dinsa ta kirashi,wallahi sai data kusa kiransa sau goma kafin ya daga,da gasken kuma baccin yakeyi abun mamakin,daya daga yaji itace sai cewa yayi 'dalla malama meye?' tayi masa bayanin komai,amma budar bakinsa cewa yayi,kada ta dameshi,idan ya gama baccin zaizo,idan zata iya jiransa ta jirashi,idan ba zata jirashi ba tayi duk yadda taga zata iya,sai ya kashe wayarsa.....kinsan abun takaicin?" Kasa cewa komai sãahar tayi bare ta amsa mata ba,duk da hakan hibba bata damu ba ta dora


"Dukka kudin matar nan idan tayi aikin tayi wahalar mijin take bawa wai a taru a rufawa juna asiri,wallahi duk da abinda yayi matan nan muna ta masifa amma bashi kariya takeyi a fakaice,abinda ya bamu haushi kenan mu duka,har yanzu kuma in gaya miki baizo ba,maganar da nake miki tun jiya fa abun nan ya faru,kudin data tara inda a hannunta ta ajjiye ba yaro daya ba ko biyar zata haifa zai mata komai ba" idanunta sãahar ta mayar ta rufe tana jin wani radadi tun daga cikin idanuwan nata har zuwa zuciyarta


"Allah ya tsinema makahon so" kalmar ta subuce daga bakinta ta fita da wani irin zafi da amo me motsa rai da zuciya.


"Wallahi kam" hibba ta amsata ba tare data lura bada ita take ba


"Kuyi mata komai ni zan biya,ku bani number wayar mijin nata,he must pay na duk neglect dinsa akan matarsa,ba baiwa bace d'iya ce kamar yadda yake d'a ga wasu" ta fada a mugun zafafe. Har yanzu maza suna bautar da mata?,har yanzu maza suna amfani da raunin 'ya'ya mata suna cutar dasu,suna illata su,wadda ke kan wani doro mai matuqar hatsari ga dukka rayuwar kowacce d'iya mace na mutuwa ko rayuwa ma basu barta ba bare me lafiya?. Ta daga idanunta da suka canza launi daga inda take zaune tana duban inda matar ke tsaye,kallo daya zakayi mata ka tabbatar tana cikin tsananin tashin hankali,kuka kawai takeyi,bata ko duba da cewa ita din ba qaramar yarinya bace,taimako da agaji kawai take nema,ya manna mata abinda zai iya zama ajalinta ya kuma gaza bata kulawa a sanda tafi buqatar hakan,koda da kudinta ne wanda ta hada da guminta da qarfin jiki dana zuciya,ba tare datayi la'akari da nauyinta yana bisa wuyansa ba


"Ina danginta?"


"Ba 'yar nan qasar bace,aurota yayi,kamar nijer naji tace" daidai sanda hibba ta gama bawa sãahar information matar ta kama qugunta ta durqushe tana murqususun dake nuna ciwonta ya fara kankama da gaske. Sãahar din na tsaye sanda nurses din suka kamata bisa jagorancin hibba suka shiga labor room din da ita. Kasa zama tayi,wani tsumammen bacin rai yana taso mata kamar zai shaqeta,wasu abubuwa da suka shude mata cikin rayuwarta a yau suka fara motsawa,suna son dawo mata da abinda ya shude a baya, situation din da matar ke ciki yayi mata baban famin data kasa shanyewa,saida wasu hawaye masu zafi suka sauko mata,ta saka tissue din data riqo a hannunta saboda khalifa ta daukesu a mugun sanyaye.


           Muryar farheen ce ta katseta,ta waiwaya daga sashen da takejin amon muryar tata


"Nayita nemanku ban ganku ba,inason nace ku dawo ciki,dakin babu kowa" farheen ta fada tana karantar wasu abubuwa masu zafi dake fita daga qwayar idanun sãahar. Kai ta girgiza


"Zan shigo,amma saina gama wani dan aiki a nan"


"Patient dinki ta sauka fa,ta samu baby girl" muryar hibba dake qarasowa gurin da hanzari ta katse tambayar da farheen ke shirin jefawa sãahar


"Alhamdulillah" sãahar ta fada tana lumshe idanunta,har cikin ranta tana jin bacin ranta yana raguwa,wanne irin sa'a akayi haka komai ya daidaita cikin hukuncin ubangiji?,ba tare da ankai ruwa rana ba duk da babyn ba'a dai dai take ba?. 


        Tun kafin farheen ta jefa tambayarta ta gama karantar komai, saita harde hannuwa tana saurarensu ita da hibba har suka gama maganganunsu,hibba ta koma dakin ta gani idan an gama gyara babyn ta dauko musu ita.


"Amma......daga haka ba wani abun zaki sake aiwatarwa ba?" Farheen ta tambayi sãahar sanda taga tana latsa wayarta. Karamin murmushi kawai ta fidda ba tare da tacewa farheen komai ba,ta riga ta qudirta a ranta,sai kuma ta aiwatar. Bugu biyu aka daga wayar daga can bangaren,suka kuma fara magana da matar dake riqe da wayar a daya sashen.


           A nutse farheen ta dauke dubanta daga kan sãahar dake shigar da qorafi tamkar aleena ko afifa aka yiwa hakan ta juya ga bayanta,inda muryar magidancin da duka duka bazai wuce shekara arba'in ba a duniya ke tashi cike da hayaniya da kuma hargowa,cikin nuna zallar gogewa a rashin mutunci.



FURAR DANKO

Billyn Abdul


-ZAFIN KAI

Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo


Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400


Pay at👇


1487616276 

Access Bank

Bilkisa Ibrahim

Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇

09033181070


VIP🔥💯

Zafin kai 3k

Furar danko 3k

Tabarmar kashi 3k

Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post