Kurkukun Ƙaddara page 11 complete

Kurkukun Ƙaddara page 11 complete

Kurkukun Ƙaddara 11

 💋KURKUKUN ƘADDARA💋


  daga alƙamin Boss Bature 


        Dedicated to Aunty Kubra 

 

E11


Takai ƙarshen maganar a lokacin sun dawo Cikin falon, Hankalin Dco da na sauran jami'an ya dawo kansu, mahaifinta kuwa jikinshi ba ƙaramin sanyi yayi ba, ganin yadda ɗiyar shi ta rame, tamkar ba neelerh ɗinsa ba,


A gefen abie ta zauna tare da kwantar da kanta saman kafaɗar shi, Ramlat Ta kalli dco tace"Sir, bata da koshin lpy, kuma ta sanar dani cewa tun jiya bata Ci komai ba,"


Uncle bash yace"Idan har bata ci abinci ba, ba zamu iya samun bayanan da muke bukata ba awurinta," Yayi maganar eyes dinshi akan Abie, kafin ya mayar dasu kan Ramlat yace"ki duba frigde nasan baza a rasa abunsha ba, Ki ɗauko mata tare da ruwa me sanyi"Amsa mashi tayi"okey sir" kafin ta juya ta nufi fridge ɗin dake A falon"


Hanmu tasa ta buɗe frigde din, Lemuka ne a jere masu sanyi, hada fura da youghurt, fresh milk ta dauko mata tare da ruwa"ta ruƙo bottles din a hannunta ta dawo ta ɗaura su asaman C table din dake agaban sofa din da aneelerh take,


Uncle bash yace"Aneelerh ta shi kisha,"batare da musu ba, Aneelerh ta mike zaune, Takai hannu ta ɗauki milk ɗin ta buɗe ta kwafa abakinta, ta shiga ɗaɗɗakarta, makoshinta har wani sauti yake badawa kwat kwat!!


Abie yace"Ki sha a hankali, kada ki shaƙe" janye bottle din tayi daga bakinta tana faman sauke ajiyar zuciya, lallai ba ƙaramar yunwa take ji ba, bayan ta ajiye milk din Abie ya dauki bottle water me sanyi ya mika mata, hannunta na kerma ta buɗe mufin ta kwafa abakinta, A hankali take shan ruwan harta kammala, Sai gashi ta ɗan samu natsuwa,

 Uncle bash yace"Aneelerh kiyi mana bayanin yadda komai ya faru a daren jiya, muna sauraronki"


Ganin yadda zufa ke keto mata, abie yace ta cire hijabinta"hannu tasa ta ɗebe hijabin, dama akwai Kallabin data ɗaure kanta da shi,


A tsanake ta soma Yi masu Bayani tiryan tiryan

  "Ji wuraren ƙarfe tara, nafarka ban samu uzair a saman gado ba, nayi tsammanin ko ya shiga toilet ne amma ko da na duba baya a ciki, na yanke shawarar zuwa na tambayi megadi,koda naje wurinshi yace mun Yaga lokacin da Uzair ya fita acikin motarshi, kuma har magana sunyi da shi kafin tafiyar shi, koda jin haka na dawo cikin gida na ɗauki wayata na kira layin uzair tana ringing amma uzair bai ɗaga ba, a ruɗe na ajiye wayar na fito na nufi gidan taj, ina zuwa na shiga gidan, A falo nayi mashi sallama, ya fito daga ɗakin shi, harma yayi shirin kwaciya, nake faɗa mashi Game da tafiyar uzair ƙarfe 9 na dare na farka banganshi ba, Nayi tunanin ko ya kirashi awaya, saboda kusancinsu dana sani, Uzair zai iya 6oye mun abun amma bazai iya 6oyema Taj ba, Shiyasa na tambaye shi,A wannan lokacin taj yace na jirashi ,Zaije room dinshi ya kira shi awaya, na tsaya ina jiranshi, koda ya dawo na tambaye shi ya kirashi,yace mun in kwantar da hankalina duk inda yake ayanzu yasan yana akan hanyar dawowa ne, ba don na yadda da kalamanshi ba, na dawo gida zuciyata duk a harmutse na kwanta, Ko a daren sai da taj ya kira layina, ya ƙara kwantar mun da hankalina, a wannan yanayin bacci yayi awon gaba dani,


Shiru ta ɗanyi tana mayar da numfashi, kafin taci gaba da cewa"da safe na farka wuraren ƙarfe tara, still uzair bai dawo ba, Nan ma hankalina ya ƙara tashi, Na yanke shawarar zuwa Wurin taj don inji idan sunyi waya da uzair, koda ace ya kirashi tsakar daren jiya, Ina fita daga gida na nufi gidan taj, tunkafin ma naƙarasa naga baba maigadin gidan atsaye ya jingina bayanshi jikin Gate din gidan fuskarshi da alamun damuwa atattare da ita..............."Komai daya faru saida aneelerh ta sanar dasu, lokacin da aneelerh ta kammala zayyana masu komai, Lamarin yayi matuƙar girgizasu, ipo Yace"akwai matsala, Uzair ya fita gida ƙarfe 9 na dare, Shi kuma taj ya fita tare da ƴarshi ƙarfe ɗaya da rabi nadare? tabbas wani Babban al'amarine ya afku"


Ramlat tace"Kuma dukansu atare da wayoyinsu suka fita"?

Aneelerh tace"Shi uzair da wayarshi ya fita, Amma shi Taj banda masaniya akan hakan"


Dco yace"Aneelerh zaki yi mana jagora zuwa gidan Taj don mu fara gudanar da binciken mu"Amsa mashi tayi"toh" kafin suka miƙe gaba ɗayansu suka ɗunguma zuwa gidan Tajuddeen, A bakin gate Dco Yace ma malam Garba yabi bayansu, Don shima zasu buƙaci jin ƙarin bayani awurin shi, Lokacin da suka ƙaraso bakin gate ɗin gidan Tajo, Baba maigadi Na zaune saman benci cikin zullumi, Dco yace shima Yabiyosu Cikin gidan,Ya miƙe yabi bayansu,


A falon Gida Taj, Abie ya zauna, baba maigadi da malam garba suka zauna saman Carpet suna jiran tambayoyin da za'ayi masu,


Aneelerh ce ta yi masu jagora zuwa bedroom ɗin taj, A bude suka samu ɗakin, Da sallama tashiga ciki, Dco da ic da ipo suka mara mata baya,


A tsakiyar Dakin suka tsaya suna bin ko'ina da kallo, Karaf idanuwan Aneeleeh suka sauka akan wayar Taj dake yashe ƙasan tiles, A ruɗe tace"Uncle ga wayar shi anan" A tare police men din suka kai idanuwansu kan abunda aneelerh ke nuna masu,


Hanky Ic ya curo daga cikin aljihun shi, a hankali ya taka zuwa inda wayar take a ƙasan tiles,ya zuƙunna tare da ɗaukota,Ya dago da ita ya juyo da ita, Screeen ɗin wayar ya fashe, sakamakon Bugun tiles da Tayi,


Juyowa Yayi tare da kallon Dco yace"Sir, A hasashe na, Jiya Bayan aneelerh tabar gidan nan, Tajo Ya dawo Ya kwanta har bacci ya ɗauko shi, Wuraren ƙarfe ɗaya da rabi na dare, An kira wayar shi, kuma ya ɗaga kiran, tabbas an gaya mashi wani abu daya ɗaga mashi hankali, wanda yayi matuƙar razanar da shi, har baisan lokacin da yayi wurgi da wayarshi ba, Ya fito daga ɗakinshi Yaje ya ɗauki ɗiyarshi ya gudu da ita,tabbas anyi mashi barazanane, kuma zai iyayiyuwa anyi amfani da uzair wajen  razanar da shi"


Jinjina kai dco yayi"tabbas akwai wani 6oyayyen Al'amari, daya faru a daren Jiya, taya za'ae mu gano ainihin meya faru?


Ipo yace"Abu na farko daya kamata muyi shine, mu fara tambayar masu gadin gidajensu A wani yanayi sukayi rabuwar ƙarshe dasu, sannan Wayar taj, Yakamata A gyarata, kodan mu samu damar bincikar last Call da yayi recieving awannan daren! Sannan zamu duba messages ɗin wayarshi, koda ace sun tattauna game da wani sirri dake atsakaninsu shida uzair"


Gaba ɗaya sunyi amanna da maganar ipo, aneelerh dae Jikin ta ƙaura yayi la'asar,Tunda taji hasashen Ic gabanta Ya dinga faɗuwa rass rasss! Daurewa kawai take yi,


Cikin falon suka dawo Kowa ya zauna, Ipo Ya kalli ɗan ladi baba maigadi na gidan tajo, yace"lokacin da taj zai fita A daren Jiya! Kaine ka buɗe mashi gate"Da sauri baba maigadi ya girgiza kai"a'a yalla6ai, Wlh ni bansan ma Ya fita ba, Kwatsam Ina Cikin Bacci sama sama Naji alamun buɗe gate, kafin inyi wani yunƙuri in miƙe inzo in duba,Tuni Ya fuce, Babu shi babu alamar shi, har waje na leƙa banga komai ba, na dawo cikin  don in duba wurin ajiye motocin shi anan naga ya fita da ɗaya daga cikin su, Bayan haka kuma na shiga cikin gidan don inga ko ƴar shi angela na nan, sai naga babu ita, nan na gane cewa da ita ya tafi, Wannan shine iya abunda nasani,


Jinjina kai Ipo ya yi kafin Ya mayar da idanuwanshi kan Malam garba me gadin gidan Uzairu,Yace"kaifa?Me ka sani game da tafiyar Uzair"?


Malam Garba yace"Naga lokacin da uzair ya fita, har magana mun yi da shi, Abunda ya faru ina zaune saman benci ina sauraron  radio, Sai ga Uzair ya fito daga Cikin gidan, Sai faman sauri yake yi, Ya buɗe mota ya shiga yayi mata key,Ya ƙaraso da motar Yana yi mun hon in buɗe mashi gate, Na taso Na buɗe mashi, har ina tambayarshi ko lafiya, naga zai fita a lokacin da bansaba ganin ya fita ba, ya ce mun babu komai, bazai jimaba yanzu zai dawo, Nayi ma shi Allah ya kiyaye hanya, wannan shine maganarmu ta ƙarshe da shi,'


Jinjina kai ipo yayi"bayan wannan ko akwai Wani wanda ke yawan zuwa gidajensu?

Har suna haɗa baki wurin cewa a'a,


Dco yace"Yanzu Idan munason ganawa da iyayen kowannansu taya zamu same su"? ya yi tambayar yana kallon aneelerh,


Cikin sanyin murya tace"surukaina basa ƙasar nan tun da jimawa suka tafi suwa south korea amma kwanan nan zasu dawo, Shi kuma taj Iyayen shi Suna zaune a Buzaye, Sun tsufa sosai, Ni aganina baikamata asanar dasu ba, Hankalin su zai tashi sosai,'


"Bazamu sanar dasu ba, Amma Shi taj ina matar shi? Ipo ne yayi mata tambayar,


Abie yace"ae shi Taj tunda  matarshi ta haifi ƴarshi ta fari, ta gudu tabar gidan, Kamar yadda aneelerh ta sanar dani, Acikin bathtub tabar mashi jinjirar,Itace ANGEL yarinyarshi,"


Dco yace"Okey, Shine Yake auran ƴar gidan tsohon gomna, Alhaji Ubaid Sani wadata" Jinjina kai abie yayi eh shine,


Ipo yace"Abunda za'ae yanzu, zamu fara bincikar wayar taj, wata'ƙil asamu wata shaida, Sannan zuwa gobe in Allah yakai mu, Zamu Kira Surukanki, don yakamata asanar dasu halin da ake Ciki, Shima Alhaji ubaid Zamu tuntu6e shi, Sannan Zamu Je gidan Radion da suke aiki, Dole mu binciki kowa dake atare dasu, idan Akayi sati ɗaya ba'aji ɗuriyarsu ba,Za'a Yaɗa labarin 6acewar su ta kafafan sada zumunta, Wata'ƙil adace"


Sun jima suna tattaunawa Da ƴan sandan kafin su tashi tafiya, Sai da suka ƙara kwantarma Aneelerh hankalinta, Sukayi mata alkawarin zasuyi iyakar bakin ƙoƙarinsu, sosai suka bata baki, kafin Ƴan sandan suka tafi, Ya rage gidan daga ita sai Abie sai su baba maigadi, Umarni abie Ya basu dasu Cigaba da kula da gidajen, Kafin a ƙare Binciken,


Ita kuma aneelerh yace Ta tashi su tafi gida, don bazai barta ita kaɗai agidan ba, ba don taso ba tabi bayanshi, A motarshi suka tafi,drivern gidansu ne ke tukasu,


Tsawon One Week Ƴan sanda suna Bincike akan case ɗin, Basu samu komai ba,Har gidan radion su taj sukaje,Ɗaya bayan ɗaya Aka fiddo da ma'aikatan gidan radion suka yi masu tambayoyi,


A Ƙarshen Satin Cikin Weekend Uncle abdallah Ya dawo ƙasar tare da Hajiya adama, duk arana ɗaya Suka shigo garin tare da Alhaji ubaid,


Sun girgiza da jin abunda ya faru na 6acewar Su tajudeen Hajiya adama tasha kuka tamkar ranta zaifita, Haka Alhaji ubaid ya shiga matsananciyar damuwa Musamma da ya ji cewa tare da jikar shi Taj ya tafi adaren Ranar, yarinyar da yake gani tamkar ƴarsa benazir data gudu tabarshi tsawon shekaru, kasancewar shi babban mutun Wanda yasan mutane da dama, tun ranar daya shigo ƙasar Ya kira Cp(Commisioner Of Police)Sukayi zama na musamman Akan case ɗin 6acewar Su tajo,


Gaba ɗaya Cp ya tattara Jami'an da suke akan aikin Binciken case ɗin, don yaji bayani daga garesu, Bakomai yafi ɗaure ma kowa kaiba, face Yadda aka rasa samun wata hujja da zata tona asirin abunda ya faru dasu adaren ranar,


Wayar Taj da suke tunanin zasu samu Wata shaida atare da ita, koda Akaba me gyaran waya ya canza screen ɗin, Cikin rashin sa'a suka samu komai na wayar Ya goge, Duk zurfin binciken da Jami'an sukayi, Basu samu koda motocinsu ba, Saƙo da lungu na garin da bayan garin dare da rana haka sukayi binciken amma basu samu wata shaida ba, A ƙarshe binciken ya koma CID, 


Labarin 6acewar Su taj ya karaɗe social media, Ta ko'ina zancen 6acewarsu a keyi, Mafi rinjayen mutane sunfi tunanin An kashesu ne a 6oye, Tunda kowa yasan su da son fiddo da gaskiya, kota halin ƙaƙa, Wannan yasa mutane su ke Hasashen kodai an kashesu a 6oye ne Allah shine mafi sanin dai dai!!!


Rayuwar Aneelerh gwanin ban tausayi baiwar Allah, Ta jigata sosai, ta shiga mawuyacin hali na rayuwa, ta rame sosai ta ƙanjame hatta aiki Abie ya hanata zuwa tunda ba ƙoshin lafiya gareta ba, Rashin Uzair da taj da kuma ANGEL ba ƙaramin nakasa rayuwarta yayi ba,Tayi kewarsu sosai,a kullum addu'arta Allah ya bayyanar dasu aduk inda suke, saboda su takan tashi tsakar dare tayi nafilfili, tayi masu addu'a Tana kuka,Haka rayuwarta taci gaba da kasancewa, Abinci kanshi sai abie da mami sun tasata gaba tukunna take Cinshi, a karshe da ciwon nata yayi yawa, Dr ya duba ta, Ashe hada laulayin Ciki, Allahu akhbar Abunda suka jima suna rokon Allah ya basu ita da uzair, Ga shi Yau Allah ya kar6i addu'arsu a lokacin da shi uzair ɗin Bayanan, Allah sarki rayuwa kenan.


A 6angarensu Hajiya adama kuwa, basu koma south korea ba, Anan suka Ci gaba da zama, saboda halin da ake Ciki na 6atan Ya'yansu ,kullum Cikin zullumi suke,


Akwana Atashi Yau wata ɗaya cuff da 6atansu tajuddeen, A lokacin Kowa ya fara sarewa, Tuni ƴan sanda sun sallami su baba maigadi, makullan  gidajensu Yana a hannun jami'an CID, sun ruƙe su har zuwa lokacin da zasu kammala bincikensu,


Tun Uncle abdallah Yana 6oye wa Mutanan Buzaye game da 6atansu Tajo, harya yanke shawarar zuwa buzaye don ya sanar dasu halin da ake Ciki,


A ranar da suka shirya tafiya tare da hajiya adama suka Bi jirgin asubahi zuwa katsina state, A hotel suka sauka, A washe gari su ka wuce zuwa buzaye, Lokacin da suka isa garin da safe, a ƙopar gidansu Malam zahiru  suka risƙi  mutane zazzaune saman tabarma, nan fa hankalinsu ya tashi, Sunzo da mummunan labari Sun riski labarin dayafi nasu ɗaga hankali .


Mutanan da suka samu a ƙopar gidan, Ƴan zaman makoki ne, Allah ya yi ma iyayen tajuddeen rasuwa su duka Biyun, Malam Zahiru ne Ya fara Rasuwa sakamakon Hatsarin Da yayi, Yana Cikin tafiya gefen titi ya dawo daga gona zashi gida, Wata mota ƙirar dab,Ta biyo ta titin  da gudun gaske kaitsaye tabi takanshi, Ashe burkin motar ne Ya samu matsala, Duk yadda drivern dake tuƙa ta yaso Ya yi control ɗinta abun Yaci tura,Gaba ɗayansu suka mutu a wannan lokacin,


Tunda labarin mutuwar shi ta riski Yahanasu mahaifiyar tajuddeen taji mummunar mutuwar da Mijinta yayi,nan take Zuciyarta ta buga ko shurawa batayi ba, innalallahi'wa'inna ilahirraji'un!!!Uncle abdallah yaji mutuwar ɗan uwansa,duk yadda yaso ya jure hakan ya faskara tamkar ƙaramin yaro haka ya dinga kuka,mutane suna lallashinshi,


 Hajiya adama saboda tsabar kiɗima  har suma saida tayi, Ciwo gadan gadan Ya taso mata, A nan gidan deeje suka xauna mahaifiyarsu Uncle abdallah, ita kanta deeje batasan inda kanta yake ba Tun bayan rasuwar malam Zahiru Ta kamu da ciwon paralyse, Laraba ƙanwar yahana su Ce ke yin jinyarta, da wasu daga cikin ƴan uwansu na nan buzayen, Kafin Barin su uncle abdallah buzaye, Itama deeje Allah yayi mata rasu wa, Wa'iyazubillah Babu wanda bai tausaya ma Uncle abdallah ba, lokaci ɗaya ya rasa ya'yan shi da suka 6ace,Ya rasa ya'yan shi da matar sa yanzu kuma Yayi babban rashi na mahaifiyarsu deeje, Lamarin dai babu daɗin ji!


Kusan wata ɗaya su ka yi A buzaye kafin suka tattara yanasu yanasu suka koma Jos,

Zaman ƙasar gaba ɗaya ya gagaresu, Babu wani Labari me daɗi, a ƙarshe suka tattara suka koma south korea, Cike da zullumin Me zai biyo baya, Don sunyi magana da Ipo, ya yi masu alƙwarin duk halin da ake Ciki game da bincikensu taj zai kira su awaya ya sanar dasu, Shima Alhaji Ubaid, Sun ƙare magana da Jami'an dake bincike a kan case ɗinsu Tajuddeen, sun yi mashi alƙwarin zasu yi iyakar bakin ƙoƙarinsu,wurin Bincikar ainihin abunda ya faru da su,kuma zasu binciko su aduk inda suke muddin suna a doron duniyar nan!,kuma duk halin da ake aciki zasu dunga tuntu6arshi akai kai,


A 6angaren Aneelerh kuwa,Komai Ya hargitse mata baiwar Allah, Ga rashin da ta yi  Ga kuma Laulayin Ciki da take fama dashi, kullum cikin yin kuka take, tsananin tausayinta ya kama su Abie, Kowa lallashinta yake yi, Akan tayi hakuri tabarma Allah komai, tun daga wannan lokacin ta hana idonta bacci,Takan tashi tsakar dare tayi nafilfili duk don saboda su Angel,idan tafara nafilfili har sai kafafunta sun fara yi mata zogi tukunna take dakatawa, idan kaga aneelerh tayi bacci to da rana ne, domin kuwa ta maida dare lokacin yin ibadarta, kullum rana ta Allah sai ta yi masu sadaka, bayan haka ta yi magana da abie akan A nemo manyan malamai su taya su da addu'a kuma ayi masu sauka, batare da 6ata lokaci ba, Abie Ya aiwatar da duk wani abu da Aneelerh ta bashi shawara akai,

   Ƴan sanda Sun Dage damtse wurin Yin Bincike,Yayin da malamai suka Bada himma Wurin taya su addu'a da kuma yi masu sauka, Haka zalika su aneelerh Sun taka rawa wurin Yi masu addu'a, da sadaka, akan Allah ya bayyanar dasu,wannan kenan..

 

Shin ya rayuwar Angel ta ƙare a cikin ruwan da mahaifinta ya jefa ta? Ta rayu ko ta mutu?


Bayan wasu ƴan kwanaki da Tajuddeen ya jefa ta a cikin ruwa, hadari ne Ya haɗu bakikkirin a sararin samaniya, kafin wani lokaci yayyafi Ya soma sauka a doran ƙasa. Daji ne mai manya manyan bishiyoyi da tsirrai, kowane ganye ka kalla yayi kore shar da shi, gwanin ban sha'awa, musamman ciyayin da ke cikin dajin masu tsayi da cukowa, a daidai wannan lokacin garken shanu suka shigo cikin dajin. Aƙalla sun kai talatin da biyar, suna tafe suna Cin ciyawa.


Wucewarsu keda wuya cikin dajin,Wata kyakkyawar bafullatanar daji, fara tass Jawur da ita, sanye cikin kayansu na al'ada, Ta bayyana hannunta ruƙe da sanda, siririyace Bata da ƙiba ko misƙala zarratin gata doguwa sam6al, Amma akwai dukiyar fulani cike tab da ƙirjinta, ga yalwataccen gashin kai dake gareta mai tsayin gaske, anyi mata kitson kalaba,Wanda yasha ado da duwatsu,wutsiyoyin gashin sun sauka har tsakiyar bayanta, ga wasu da suka zubo ta gefe da gefe na fuskarta,


Tabarakallahu ahsanul khaliqin,Wasu dara daran idanuwa gareta Farare Ƙal kamar fatar farin Cikin kwai, Launin Idon nata Brown Colour ce, tana da kwarin ido sosai,Ga ziraran Eyelashes, Jagirarta tamkar anzanata saboda tsaruwarta, Ga wani dogon hanci da Allah yayi mata, siraran la66anta jawur dasu, Akwai kwalliyar ɗige ɗige asaman fuskarta har goshinta, Wuyanta na sanye da sarkoki, Haka hannunta ma akwai awarwaro,Tana da hujen hanci mai shegen kyau, idan tayi dariya kuwa wayyo Allah madarar kyau, Kai kace gonar audugace, Saboda kyan fararen hakoranta masu tsari, wani ƙarin kyan dimple biyu gareta wanda ko magana take yi, sai sun lotsa,A ƙalla Bazata Wuce shekara Goma sha Shida ba,


Tafiya take Yi a bayan shanayen tana Korasu da sandar hannunta, Wani Lokacin Har rawa take Yi tana jujjuya Jikinta, Da alama ba ƙaramin daɗin yanayin garin take ji ba, ko kusa bata jin Sanyi, Burinta A ruwan sama ya sauka sosai don tayi rawa acikinsa, kamar yadda ta saba,


Fararen kafafuwanta na sanye Cikin takalma, Cikin harshen fulatanci ta soma raira waƙa,


Tana cikin yin waƙar ruwan sama ya soma sauka tamkar da bakin kwarya, Wani irin farin Cikine Ya lullu6eta, Cikin harshen fulatanci tace"Ni ɗin Jinin nasara ce, Mai nema mai samu,Mai nasara mai sa'a, Daga Yin magana Gashi ruwa ya sauka wuhuhu Sai ni DANEJO"


Rawa Tashiga Yi acikin ruwan Yayin da shayenta suka duƙufa Cikin dajin suna kiwo,


Juyi ta dinga yi  tana karkaɗa qugu, ruwan saman duk ya jiƙe kayan jikinta sharkaf, sun manne mata,Ƴar rigar jikinta bata rufe Cibinta ba, Sai ɗan zanin data ɗaura, kallabin kuma taci ɗamara dashi,


Tana Cikin Yin rawar nan Cikin rashin sa'a ta ɗaura ƙafarta saman wani dutse dake a bakin Ramin da wannan tafkeken ruwan yake, Gaba ɗaya Dutse ya jirkice, A gigice Ta fasa Uwar ƙara, duk yadda taso Ta hana kanta faɗawa Cikin ramin amma hakan ya faskara, Domin kuwa gaba ɗaya Ta rufza Cikin Ramin, Tsulum Ta nutse Cikin ruwan,


Within Seconds Ta fiddo da kanta daga Cikin ruwan Tana faman haki kamar wadda tasha gudu, Gaba ɗaya gangar jikinta tana acikin ruwan, Iya kafaɗarta Ya tsaya, Idanuwanta sunyi luhu luhu dasu, Ƴan hanjin cikinta sun kaɗa, Hankalinta ya ɗunguzuma, Ba ruwan bane damuwarta, don tun tana ƴar ƙarama Baffanta Ya koya mata Ruwa, Babbar damuwarta shine taya za'ae Ta fito daga Cikin Ramin?


Rushewa tayi da kuka cikin harshen fulatanci ta soma Kiraye Kirayen Sunayen Ƴan uwanta donsu kawo mata ɗauki,

  "Inna wuro,Adda!Nanne!bawuro!Wayyo Allah Na babu wani akusa da zai kawo mun ɗauki"? tana Cikin wannan yanayin Shanayen ta Suka Leƙo Cikin Ramin Kamar sunji abunda take cewa, sun kewaye ramin suna ta kuka Emmoh !emmoh!

  Nuna su Tayi da yatsan hannunta"Banga amfaninku ba, Ciyawa kaɗai kuka Iyaci,"cike da takaici tayi maganar,Tana Cikin sambatun nan, Aka kwatsa Tsawa mai sautin gaske a gigice Ta nutsar da kanta Cikin ruwan don ba ƙaramin tsorata tayi ba 

sosai ruwan saman Ke safka da ƙarfinshi,

Lokacin da danejo ta nutsa kanta Cikin ruwan a tsorace sakamakon Tsawar da aka kwatsa, Ba zato Ba tsammani idanuwanta suka sauka akan Kyakkyawar Yarinyar dake kwance saman dutsen dake a ƙasan ruwan mai girma da faɗi, sumar kanta duk ta rufe fuskarta, rigar Jikinta duk ta nannaɗe ta manne mata, biji biji take iya hangenta saboda ƙasan Ruwane


Waro ido waje daneju tayi a matuƙar tsorace take kallon Yarinyar, Shin mutunce ko aljan, Abunda ta fara sakawa aranta kenan, tunawa da wata tatsuniya da Nannensu ke basu, Akan macen kifi, nan da nan tsoro ya ɗarsu acikin zuciyarta, A gaggauce ta fiddo da kanta daga Cikin ruwan Tana faman Mayar da numfashi,


Waswasi ta shiga yi acikin zuciyarta,Anya Yarinyar data gani Acikin Ruwan Mutunce? kodai ta macen  kifi ce ko ɗan ruwa? ta jima tana wannan zancen Zucin Kafin Ta kuma nutsa kanta Cikin ruwan, Cike da fargaba ta nufi inda Yarinyar take saman dutse har Allah ya kawota Saitin Inda yarinyar take, Hannu biyu tasa Ta ɗaukota, Sama tadinga yi Har ta fiddo da kanta daga Cikin ruwan, Natsuwa tayi tana kallon kyakkyawar yarinyar, Daga gani ba ƙaramin Jiki taji ba, Allah kaɗai yasan Tun wani lokaci take kwance a ƙasan ruwan, Cikinta yayi 6ul6ul dashi,Da alama Ta shaƙi ruwa sosai,


At first sight da Danejo ta kalli fuskar yarinyar, sai taji tsananin tausayinta, Kuma nan take taji tana son ta taimaki rayuwarta.


Tunda ta ayyana hakan azuciyarta sai taji ta daina Jin tsoron tafkeken ramin Ramin, kodan saboda Yarinyar zata yi iyakar bakin ƙoƙarinta wurin ganin ta ceci rayuwarta.


Dabarace ta fado mata aranta, Da sauri ta sanya hannu ɗaya, ta Kwance kallabinta data ɗaura ɗamara dashi, Ɗayan hannun kuma na dafe da yarinyar,


a saman bayanta ta goyata, kafin a hankali ta cigaba da matsawa cikin ruwan harta ƙaraso jikin gwamagwaman duwatsunan dake kewaye da wurin, jikinsu akwai hudoji, tsaf mutun zai iya daddafawa ya haura sama, Sai dai yana da matuƙar hatsari idan Duwatsunan Jiki suka 6allo, mutun zai iya jin mummunan rauni  ga shi ita harda goyo.


Cike da fargaba danejo ta sanya hannayenta, ta dafa jikin dutsen A haka tadin ta tafiya tana bin jikinsu, Har Allah ya taimaketa ta hauro sama, tana faman Mayar da numfashi, da sauri ta sanya hannayen ta tare da warware goyon da tayi mata, ta sauko da ita a hankali ta kwantar da ita saman ciyayin, ɗagowa tayi tare da kallon shanayenta dake ta kuka, Ta wurga masu harara don ba ƙaramin  haushin su take ji, daga gani dai akwai ƙuruciya atattare da ita.


Mayar da idanuwanta ta yi  akan fuskar yarinyar, ta sanya hannu tana yaye sumar kanta data rufe fuskarta.


Tayi wani irin haske, ƙananun la66anta sunyi  pink sosai suka ciza, duk irin kyan danejo saida tayi mamakin Tsantsar kyawun yarinyar data tsinto acikin ruwa.


Hannayenta ta ɗaura Asaman ƙirjinta tashiga dannashi, Nan take ruwa ya sona fesowa Ta bakinta da hancinta, cigaba da dannawa tayi har saida ruwa Ya daina zubowa, natsuwa Tayi tana kallonta, ta yi tunanin zata farka amma sai taga ko motsi ba ta yi ba, Da sauri ta jogana kunnanta saitin Zuciyarta don taji, idan tana harbawa a razane ta ɗago, ranta duk ajagule fargabarta kada ace yarinyar tarasa ranta.


Tunawa tayi da saman dutsen da ta ganta akwance, hannu tasa ta juyo da bayanta, ta cusa yatsun hannunta acikin sumar kanta data cukurkuɗe, har saida ta taddo fatar kanta fara sol, Anan taga Raunin data ji, ashe kantane ya ɗan fashe daga baya, sakamakon buguwa da kanta yayi jikin dutsen, A ruɗe danejo ta miƙe tare da daukarta, ta sa6eta saman kafadarta, Sam ta manta da shanayensu, hankalinta na akan Yarinyar dake Cikin mawuyacin Hali, Watsawa Tayi da gudun gaske tamkar zata tashi sama, 


Tana Cikin gudun nan, wani bafullatanin Sanye cikin kayan fulani, da ƴar hularshi, Hannunshi ruƙe da sanda zai gifta, Karaf idanuwan shi sauka sauka a kan danejo dake ta tsala gudu,


Mamaki ne ya kama shi, ɗaga murya ya yi tare da kwala mata kira, har cikin kanta tajiyo kiran da ya yi mata, Batare da ta juyo ta kalleshi ba ta amsa mashi da na'am,


Cikin harshen fulatanci Yace inata baro masu shanayen su kuma menene ta dauko a hannunta, tace ma shi suna can suna kiwo, Yaje ya cigaba da kula dasu,"daga haka bata ƙara cewa uffan ba,


Girgiza kai Bawuro yayi a ranshi yace bazata ta6a canzawa ba, daga haka ya nufi Cikin dajin inda shanayen su suke,


Danejo kuwa bata nufi ko'ina ba, Sai wuraren wasu Bukkoki rukuni rukuni a ƙalla sunyi Shida, A gefen ɗaya daga Cikin bukkokin wani tsohone tukuf zaune cikin kayan fulani, daga gefe kuma Wasu Manyan matane, Sun kwan biyu aduniya, Sai sussukar gero sukeyi, ga wasu kuma Ƴan mata su biyu matasa Suna 6arar masara,


Tundaga nesa Tsohon Ya hangota, da ƙarfi ya ambaci sunanta DANEJO, lokaci ɗaya sauran Mutanan suka ɗago suna kallonta, Ganin yadda take ta gudu yasa duk sukayi tunanin ko wani mugun abunne yabiyo ta, aikuwa aguje Suka nufi Cikin bukkokinsu kowa ya ɗauko makaminshi, Shima tsohon ya miƙe yana ɗangyale ƙafa ya shige cikin bukkar gefen shi, Sai ga shi ya fito hannun shi ruƙe da Ma shi, (to fa yaƙi ya ta shi)


Ƙarasowa tayi tana ta faman haki, lokacin da suka lura da abinda ke ruke a hannunta sai kowa ya ajiye makaman yaƙinsa, suka tattara hankulansu akan yarinyar data ɗauko, A saman Shimfiɗar kakansu ta sauke yarinyar, tare da ɗagowa ta kalli kakansu cikin harshen fulatanci tayi mashi bayanin inda ta tsinceta, koda jin hakan Jiki Na rawa Ya koma Cikin bukkarshi, Sai ga shi ya fito hannun shi ruƙe da ƴar jakkar fata, a gefen shimfiɗar ya sauke jakkar, Yace ma danejo ta nuna mashi inda taji ciwon, rubda ciki ta kwantar da ita, tasa hannu ta yaye sumar kanta, nan suka ga raunin da taji, Bude jakar yayi ya curo wasu magunguna nasu na gargajiya, wanda suke Yi ma mutun treatment dasu idan yaji ciwo,


Matsowa sauran Fulanin sukayi Gaba daya sukayi masu Danejo ƙawanya, Duk sun baza idanuwansu akan yarinyar, Cikin ƙanƙanin Lokaci ya kammala Yi mata treatment ɗin Raunin nata, Sannan Ya kalli Danejo yace ta dauketa takaita Cikin bukkarsu, ta kar6o bargunan da suke lullu6a dasu, A rufa mata ajikinta, sannan a hado garwashin wuta, A sanya mata a cikin ɗakin don ya ɗumama.


Bayan danejo ta dauketa, takaita Cikin bukkar su Saman shimfidar da suke kwana ta kwantar da ita, ta fita zuwa sauran bukkokin ta kar6o bargunansu, da zannuwa duka Ta haɗosu a hannunta, ta shigo cikin bukkar ta lullu6a mata su, kamar yadda kakansu yace ta yi mata, tana Cikin nannaɗeta cikin bargunan, Adda ta shigo hannunta ruƙe da murfi na karfe, Garwashin wutane jawur a saman shi, A gefe ɗaya ta ajiye garwashin wutar,


(Mu haɗu a next page In Allah yakaimu da rai da lafiya, Like dinku da comment sunyi ƙaranci, yau zan zuba ido in gani, indai bai kai adadin daya dace ba, nima zan daina wahala saboda lokaci nake fiddawa inyi typing in kuma yi maku typing saboda farin cikin ku, amma wasu basa gani just ko second bazaici ba mutun yayi liking da comment😏 Alhamdulillah An bani admin a group din nan, zan sanya maku ido sosai🤣 Allah ya taya mu ruƙo

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post