Makauniyar Kaddara Hausa Novel page 16-20 - Novels Elite

Makauniyar Kaddara Hausa Novel page 16-20 - Novels Elite

 

Makauniyar Kaddara Hausa Novel page 16-20 - Novels Elite

MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_

Page 16

*_INA MATA ƳAN ƘWALISA BA'ABOTA SON GYARA JIKI DA FATA SUYI ƘWANAS TAMKAR WATA ƊAN DAREN SHABIYAR?!_* 

_Ku marmatso kusa maza na kaiku kantin sauƙi na UMMU DUFAIL gidan sauƙi da biyan buƙatar MATA SARAKAN ado harma da MAZA ƴan ƘWALISA._

*_MATA da yawa kanso su koma Taurari ababen kallo da burgewa ga ma'abota kallo sai dai basusan ina zasu sami sinadarin kankaro wannan ƙyawu da mutuncinba._*

_To maza kuzo kusa dan Bilyn Abdull ta lalubo muku kantin sauƙi na Umm Dufail dakeda kaya masu sauƙi da gamsar da maison afani dasu_.

*_UMMU DUFAIL nada kayan gyaran jiki masu rahusa da inganci da gamsar da mai saya cikin ƙanƙanin lokaci kamar haka👇🏻😁_*

*Customers price list By Ummu Dufail FACE AND BODY*

 SCRUB=2500(300ml)

Face and body mango butter=3k (250ml)

Face cream= 1800

Corretor oil/vitamin C oil=2k

Fairness skin lotion= 2500

Hot chocolate skin lotion 2500

Serum (for Nuckles )2k

Nuckles cream (stubborn)3500

Mix fruits Arabian black =soap 1800

Mix fruit glycerine soap =1900

Beetroot=1900

Coconut, milk,egg..face soap=1200

Lavender mix fruit soap =1800

Body wash =1500

cleanser=1600

Hair spray =700

Hair oil =1500

Hair relaxer =700

Hair butter 1700

Shampoo =1500

Breast=oil 2k powder 2k

Strech marks cream= 2k

Beetroot pink lips =700

Baby care soap glycerine=1k

Baby care butter =1500

Shea butter baby soap =700

Tsumin tula =2200

Tsumin zinariya =1200

Sliming tea =1500

Amarya set =25k

Liquid Arabian black soap =1900

Cleansing water =1500

*_Zaku iya bibiyarta domin gani da ido ta Handle ɗinta na istagram da facebook kamar haka_*

Ummu Dufail @ Facebook 

Ummu Dufail @ instagram

Phone no: 07067943479.

_Ƴammata harma da masu auren karku bari ayi babuku. Dan gyara shine mace a wannan ƙarnin😉👍🏻_.

*Page 16*

............Kamar da wasa sai ga ƙaramar magana ta zama babba. Dan kuwa dai Hajiya Iya da gaske take akan amshe Zinneerah daga hannun su Mama. Dan take a wajen ta ɗaga waya tai kiran Alhaji Kabir da dukkan ahalin gidan ke kira da suna Baffah.

     A rayuwa Alhaji Kabir bai haɗa uzirin mahaifiyarsa dana kowaba. Kai bama shi kaɗaiba har sauran ƴan uwansa da jikokin familyn babu mai sakaci da buƙatar Hajiya Iya. Dan ita ko wasan jika da kaka sai taso takeyinsa. 

    A cikin ƙanƙanin lokaci sai gashi a sashen nata. Hannu ya bama Abba suka gaisa yana faɗin, “Ai bansan ka shigo gidanba Alhaji Isma'il, dana fito mun gaisa”.

       Abba yace, “Wlhy yanzuma na shigo Yayanmu, nazo wucewa da ƙannenka ne, sai kuma ƴayanka dana kawo suma suyi gaisuwa su kuma gaida Gwaggo”.

       “Kai kai masha ALLAHU, lallai yau ka farantamin sosai sosai. Kuzo-kuzo ƴaƴan albarka ga babanku da baku saniba ko”.

     A nutse su Sadiq duk suka nufesa harda Zinneerah. Sai dai ita ta durƙusane daga gefensa kaɗan. Saɓanin su Abdul daya jawo jikinsa ya rungime. Sai da su Sadiq suka gama haishesa ya amsa da kulawa da tambayarsu sunyaensu da ajinsu nawa a makaranta kafin ya maida dubansa ga Zinneerah itama.

     “Ikon ALLAH, Inna wannan ai saikace Inno ta haifeta dan kamanninsu. Ɗiyata yaya sunanki?”.

       Zinneerah da kanta ke duƙe tana wasa da yatsun hannuna tace, “Zinneerah”.

“Masha ALLAHU suna mai daɗi kamar yanda kike ƙyaƙyƙyawa ɗiyata. ALLAH yay muku albarka. Ke ajinki nawa a makarantan?”.

     A take murmushi ya subucema Zinneerah tace, “Abba ss1”.

      “Kai-kai, kice Maman nawa bata wasa bace ƴar boko ce”.

      Barkwancin nasa ya saka dariya suɓucema Zinneerah. Yayinda hakan kuma ya sake saka ƙaunarta a zuciyar Alhaji Kabir dan nutsuwar yaran da tarbiyyarsu ya matuƙar birgesa, musamman Zinneerah ɗin da take mace.

    Kallonsa ya maida gasu Mmn Sadiq yana fadin, “You see. Gashi kun fara tara zuri'a amma basusan kowaba suma. Sai dai ko a hanya naci karo da Zinneerah ai nasan jini nace. Idan akaimin gaddama kuma har kotu zan kai dole a bani abata”.

      Sosai maganar tasa ta saka kowa dariya. Hajiya Iya tace, “Aini kiranma danai maka kenan. Dan nikam dai babu mai rabani da mai kama da Inno tazo gida kenan”.

      “Ina bayanki Innata. Dan haka Alhaji Isma'il dan ALLAH a taimakemu badan halinmuba a bamu Zinneerah, bamason a kalli hakan kuma fin ƙarfi roƙo muke gwiwoyinmu a ƙasa. Ƙila hakan ya zama sanadin gyaruwar zumincin dake neman kufce mana. Amma kuje dai kuyi shawara. Idan kuma akwai matsala dan ALLAH karkuji kunya ku sanar mana kanku tsaye zamu fahimceku insha ALLAH. Kunga ko ba'a bamuba sai take zuwa mana hutu ita da sauran ƴan uwanta lokaci-lokaci”.

        Cike da jin kunyar wannan roƙo nasa Abba yace, “Ai kunfi ƙarfin hakan a garemu”. Yay maganar yana duban Mmn Sadiq data duƙar da kai.

       Daga Hajiya Iya har Alhaji Kabir suma idonsu na kanta. Dan haka Alhaji Kabir yay saurin fadin. “To Alhmdllh, yanzu dai kuje kuyi shawaran nan da kwana uku sai muji yaya ake ciki kamar zaifi”.

      Sam Hajiya Iya bataso jin hakan daga bakin ɗan nata ba, dan sotai take yanke su tafi su barta da Zinneerah, saboda wata irin ƙaunar yarinyarce ta musamman ta shigeta lokaci guda. Amma sai tai shiru dan itama taga cancantar barinsu suje su shawarta ɗin. Amma kuma komai zasuyi tasa a ranta sai Zinneerah ta dawo hannunta da zama dan yarinyar ba karamin shiga mata rai tayiba lokaci guda. shi kansa Alhaji Kabir wani irin kaunar yarinyar yaji a ransa batare da yasan dalilin hakanba.


      Alkairi mai tsoka Alhaji Kabir yayma su Aliyu. kamar yadda aka koyar dasu tarbiyyar godiya haka suka shiga masa godiya da addu'ar fatan alkairi a rayuwa. Sosai hakan yay masa daɗi har cikin rai. Ya kuma kara jin girma da darajar su mmn sadiq sosai. Dan a wannan zamanin bama yaro tarbiyya shine mai matuƙar wahala ga iyaye aynun.


★★★★


       Tunda suka baro gidan babu wanda ya iya yin magana, sai da suna gab da shiga anguwarsune ma Gwaggo Maryama tai ƙarfin halin tambayarsu ina suka baro little kuma?.

      “Gwaggo ai baida lafiya an kwantar dasu a asibiti shida Umma”. Abdull ya bata amsa da damuwa a fuskarsa.

      Saurin juyowa Mmn Sadiq tai ta kalli yaron, kamar zatai magana sai kuma tai shiru ta maida kanta. Fahimtar hakan da Abba yayi ya sakashi faɗin, “Ban faɗa muku bane dan banason raba muku hankali biyu, amma jikin nasama Alhmdllh dan yanzu haka sun koma gida ta kirani cewar an sallamesu ga Naziru yaje zai maidasu gida. Bakomai ke damunsaba kuma sai zazzaɓin haƙora”.

     Addu'ar samun ingattacciyar lafiya sukai masa ita da Gwaggo Maryama. Daga haka suka ƙarasa gidan.


        Sai da sukayi sallar magriba suka huta Maman Halima ta shigo gaishesu ɗauke da Little daya rame sosai saboda yasha jiki. danma ALLAH yayisa mai kwaramniya ga karfin hali da akasan duk yaro da shi.

    Ƙiri-ƙiri sai gashi yana musu ƙyuya. Yaƙi yarda da kowa sai Zinneerah da kunya ta rufe kamar ƙasa ta tsage ta shige. Badan tasoba dole ta amshesa. Aiko ya wani lafe a jikinta yana kallon su Gwaggo Maryama dake jan kafarsa cikin tsokana tana fadin, “Aiko yaro nama fasa auren. Na maka saki goma sha biyu ni da kai baram-baram”.

     Dariya Mman halima tai tana tare masa. Ana cikin haka Maman Sakina ta shigo da yaranta wai zatai musu gaisuwa. duk da bataje can gidanba sai mmn sadiq bata nuna mata komaiba ta amsheta hannu bibbiyu suka gaisa tai musu godiya. 


   ______________,★


      Har washe gari babu wanda ya sake tada maganar komawar Zinneerah gidan hajiya Iya. Dan shi Abba ma ya fice kasuwa abinsa tun safe. 

       Sai bayan sallar la'asar ne Mmn Sadiq da abin keta cin ranta dai ta tunkari ƴar uwarta da maganar. “Maryama nifa inaga kodan matsalar gidan nan zanbar yarinyarnan ta koma wajen Gwaggo, sai dai kuma idan na tuna kar ace dansu masu arziƙi ne mukai haka abin na damuna. Sannan shi kansa Yaya na fahimci baison maganarnan”.

     Murmushi Gwaggo Maryama tayi tana gyara zamanta sosai. “Yaya Hauwa nifa kin ganninan babu abinda ya dameni da cewa ta mutane. Abinda duk ra'ayina ya bani na kuma ji raina ya aminta da shi kuma bai saɓama addinina ko al'adata ba to tabbas yinsa nake dan bama kaina farin ciki. Shi ɗan adam babu wani abu da zakayi a rayuwa ƙyaƙyƙyawa ko mummuna da zai iya gani bakinsa bai tankaba koda kuwa shi a tare dashi akwai abinda yafi naka muni ɗin da ƙyau. Dan haka ajiye batun cewa na mutane muyi abinda ya cancanta. Tun jiya nima cikin nazarin maganar nakeyi da shi Yaya kansa. Shi kawai abinda na fahimta da shi gani yake kamar za'a nuna gazawarsa akan riƙon Zinneerah tunda ba shine ya haifetaba. To amma abinda bai tunaba kuma shine sufa mutanen nan bawai sunsan bama shine ya haifitaba. Sai dai ni har cikin raina na yarda da komawar Zinneerah can gidan kodan wannan fitinanniyar matar tasa dake ganin Yayan ne kawai keda arziƙin da ake zuwa a ci”.

        “Maganganunki duk suna a kan hanya Maryama. Harga ALLAH inason basu ita domin ALLAH da suka roƙa da kuma darajar zumincin da suma sukayi dan shi. sai dai inason tai nesa da su Saude kodan ɓata mata suna da suke a anguwatnan miji zaima Zinneerah wahalar samu. Dan damafa ni ko wannan bata tasoba nayi niyyar ta biki can ku zauna har muga abinda ALLAH zaiyi”.

      “A to tunda hakane a bani abata mu tafi”. Gwaggo Maryama tai saurin faɗa tana dariya. Itama Mmn sadiq dariyar tayi. Haka suka cigaba da tattaunawa har tsawon wani lokaci kafin subar maganar da nufin jiran dawowar Abba yau su tunkaresa da batun.

       Zinneerah da batasan mike faruwaba tana can ɗaki da Little wanda a yanzu yake maƙale mata baya yarda da kowa a gidan sai ita da Gwaggo Halima. Sai su Sadiq idan yaso. Makarantama yau da zata tafi kuka yayta zabgawa sai daga baya ya haƙura bayan yayi barci ya tashi. Wauta da ƙuruciyar dake tattare da ita kuma yasa bata ɗauki hakan komaiba saima tausayin yaron da ƙaunarsa dake ƙara ratsata. Maganar komawa gidan Hajiya Iya kuwa bata damuba ba kuma ta mantaba. Sai dai bata wani ɗaukesa da muhimmanci ba balle taji wani abu a ranta game da hakan.


_________________★


        Koda Abba ya dawo gidan sai da Mmn Sadiq ta bari yaci ya ƙoshi ya nutsu sosai sannan ta tunkaresa da zancen kasancewar yau itace dashi dama. Shiru yay mata tamkar baijitaba. Ita kuma tunanin baiji ɗin bane ya sata sake maimaitawa kai tsaye. Sai dai yanda ya sake tsuke fuska ya saka tasha jinin jikinta kuma.

        Bai kulataba sai da ya mula dan kansa sannan ya fara magana a ƙufule. “Hauwa'u kun shirya hakanne dama saboda abinda ya faru a gidan nan kwanaki shida da suka wuce komi? Shin halin Saude ne baki saniba a gidan nan ne? Da har zaki yanke hukuncin rabani da Zinneerah bayan ni har cikin raina ɗaya na ɗauketa da duk wani yaro dake a gidan nan”.

      “Yaya kayi haƙuri dan ALLAH, sam ba yanda kake tunani baneba. Ni abinda yasama kaji namaka magana saboda mu toshe ɓarakar da dangin mahaifiyarmu ke ganin mahaifinmu ne ya assasata. Su daina ganin tamkar muna gudunsune. Sannan baiwar ALLAHn nan ka duba yanda suka ɗauka Inno, wandama bai saniba zai ɗauka itace ta haifi Hajiya Iyan ai. Wlhy na tabbata da ace banan ta kawo Inno har ALLAH ya ƙaddara rasuwarta ananba da sai munyi kuka bana wasaba akan wannan rasuwar. Yanda zuminci ya taɓarɓare kowa zagayewa zaiyi yabar Buba da gawar Inno, da kuma sun bizneta su kama gabansu su barmu. Amma yanzu kaga yanda suke tururuwar zuwa nan hardama waɗanda bakai zaton ganiban. Amma kayi haƙuri nayi kuskure, dan babu yanda za'ai Zinneerah ta koma can bada yardarkaba”.

      Numfashi Abba ya sauke yana ɗan jinjina kansa. “Maganarki akan hanya take Hauwa'u, ni kaina naji daɗin wannan karamci da suka nuna akan marigayiyar, dan sun nunama sauran dagi su basu manta alkairin Inno ɗinba garesu har yanzun. Badanma ALLAH bai ƙaddaraba kinjifa maganar kaita india da suka fara. Da ace masu kuɗi haka suke daraja zuminci fiye da dukiyarsu dake tsone idonsu lallai da bamu lalace hakaba. Ace dan ALLAH ya baka wani abin jin daɗin duniya kakoma ƙyamar ɗan uwanka baka ƙaunar ya raɓeka. shiko yana gudun raɓar takane saboda karka wulakantashi. Kaiconmu da fifita abinda zai halakamu sama da abinda zai kaimu aljanna”.

       “Amin ya rabbi Yaya. Al'amuran kam sai dai addu'a. Ni kaina halayyar mutanen nan ta zaburar dani wani muhimmin abu insha ALLAH”.

      “Ai haka akeso dama. idan kaga wani ya aikata alkairi kayi ƙoƙarin koyi da shi, ka kuma nisanta kanka ga mai aikata mummuna. Dan masu iya magana kance zama da maɗaukin kanwa shike kawo farin kai”.

         “Sosai kuwa Yaya, ALLAH kai riƙo da hannayenmu”.

    “Amin. To amma nima kuma sai a duba ni dan har cikin raina inason zaman Zinneerah tare damu kodan kansu ya haɗu da sauran ƴan uwanta. Gashi kuma inajin matuƙar kunyar mutanen nan wlhy, yanzu hakamafa ɗazun sai da Alhaji Kabir ɗin ya kirani da kansa akan suna nan dai suna jira”.

       Cike da mamaki Mama tace, “Wai kirafa Yaya?”.

       “Wlhy kuwa, mutanen nanfa mutanen kirkine masu ban mamaki. Toni banda dalilinki ta inama zan ishesu kallo koda a haɗuwar hanyane. Amma ki duba yanda suke da sauƙin kai. Yanzu da wani zaiji nace Alhaji Kabir Shira na kirana a waya ai cazai na zuga ƙarya ko”.. 

     Dariya ta kufcewa Mmn Sadiq, shima Abban ya shiga tayata. “ALLAH kuwa Hauwa'u koni kallon abun nake tamkar mafarki. Ku riƙe bayin ALLAHn da ƙyau bawai dan arziƙin da ALLAH yay musuba, sai don sanin darajar ɗan adam da zuminci da ALLAH ya azurta zukatansu da shi”.

     “Insha ALLAHU Yaya. ALLAH ya bamu ikon gina zuri'armu bisa ƙyaƙyƙyawar tarbiyya muma. Koda sun zama wanu abu a rayuwa sukasance masu sanin mutunci da darajar ɗan adam”.

      “Amin ya rabbi Hauwa'u. To ammafa zan basu Zinneerah ne kawai banda Abdul-Mutallab. Tunda ba wani shayar dashi takeba tabar mana abummu anan. Itama dai su tausaya mana ta dinga ziyararmu akai-akai. dan ɗazun namasa maganar karatunta dan shine babban burina a gareta. Inason rayuwarta ta inganta sosai kodan kaddarar data ziyarci rayuwarta tun tana ƙanƙanuwarta. To shine yake cewa indai karatune sai Zinneerah tace ya isheta da kanta insha ALLAH”.

       “Yaya ALLAH ya saka da alkairi. Dama nima damuwata akan Abdul ɗinne. To amma kana ganin mu sanar dasu gaskiyar al'amari game da haihuwar tata kenan?”.

      “Eh to, bazance miki a'a ba, bakuma zance e ba. amma inaga muɗan bada lokaci taje gidan muga yanayin zaman nata tukunna, duk da har cikin raina bana tunanin wani abu saɓanin ƙyaƙyƙyawa”.

       Cike da gamsuwa Mmn Sadiq ta gyaɗa masa kai.


___________________★


        Washe gari Gwaggo Maryama ta shirya taje yoma Hajiya Iya sallama dan zata wuce itama. Shatara ta arziƙi aka haɗota dashi, tare da driver na ɗaukar Zinneerah, dan Hajiya Iya tace ta gaji da gafarasa bataga ƙaho ba. Da tarema zasu zo da kanta ta ɗauka Zinneerah ɗin sai akai rashin sa'a tai baƙi. Hakan yasa ta haɗo Gwaggo Maryama da driver tace kafin itama tazo, dan tayi alƙawarin dukkan zuri'arta sai sun tako har gidajensu suma insha ALLAH.

       Wannan al'amari ya bama su Mmn Sadiq Mamaki da dariya. Babu shiri tai kiran Abba ta sanar masa. Dole ya baro kasuwa yazo sukai magana. Gashi su kofa Zinneerah basu zaunar akan batunba dan sun yanke da saita samu hutun makarantane.

       Ganin kar Hajiya Iya taga kamar suna mata yawo da hankali suka yanke shawarar barin Zinneerah taje kamar da nufin yin kwana biyu haka. Dan karsu mata gatsau takuma shiga wani hali musamman akan Little.

      Ilai kuwa da suka kirata aka sanar mata zataje wajen Hajiya Iya ta zauna da ita na kwana biyu saboda batajin daɗi sai bata wani damuba. Hasalima taɗanji daɗin tafiyar kodan taje ta huta daga izgili da ƴaƴan mmn sakina da ita kanta maman sakinar kemata a kwanakin nan musamman a makaranta. Shiru kawai takeyi dan karta tada hankalin mahaifiyarta. Amma abin na damunta, dan takai yau har ihu Sakina ta saka akai mata a aji ana kiranta agola ƴar cin arziƙi. Damuwarta ɗaya karatunta da kuma Little dake nane da ita a kwanakin nan duk da ya ƙara samun sauƙi bakamar daba.

     Bayan Mama da Abba sun mata nasiha akan ta kula da kanta da kuma girmama kowa yanda zasuyi alfahari da ita ta ɗauka kaya kala uku kawai abinta tai musu salama cikin dabara ta fito saboda little. Su Sadiq kuwa suna makaranta sai dai su dawo suga wayam bata nan.


      Motane lafiyayya kuma ƙosashshiya. Dan ƙamshin dake a cikintama kansa na musamman ne. (Abinda bata saniba wannan mota ta mai gayyace mai aiki ce. dan Alhaji Kabir motarsa ya bada musamman domin ɗakkota. Haka kawai yarinyar ta shiga ransa yakejinta tamkar ƴaƴansa daya haifa. Ga kuma son daya fahimci mahaifiyarsa na mata itama). Tana a baya driver na gaba yana tuƙinsa a nutse, tai tagumi kawai tana kallon waje da zurfafa a tunanin yanda rayuwarta keta walagigi. Anya kuwa ita tanada farin jini ga mutane? Duk inda zata rayu bata taɓa samun salama hundred percent sai da matsaloli. A Danya matsalarta Inna, Yaya Karima, Tinene. Bayan ƙaddara ta haɗata da mahaifiyarta gakuma su Maman Sakina da ƴaƴanta yanzu suna neman hanata shan ruwa a gidan data samu gata da kulawa. Anya kuwa idan ta dawo daga inda zata yanzu bazata shawarci mamansu akan a maidata boarding school ba ko zata samu nutsuwar yin karatunta cikin salama?.

      Wannan tunanin yasata jin nutsuwa a ranta taketa sakin murmushi batare data saniba har suka iso gaban katafaren milk color ɗin gate ɗin gidan. Sai da driver yay horn maigadi ya wangale gate ɗin ta dawo hayyacinta. Nannauyan numfashi ta sauke zuciyarta na wani irin tsargawa tamkar waccan ranar da Abba ya kawosu. Addu'a ta shiga karantowa a ranta har driver ya buɗe mata ta fito. Godiya tai masa cikin risinawa. Hakan ya sakashi jin daɗi har cikin ransa. Ya miƙa hannu zai amshi jakkar hannunta amma sai ta hanashi. “Haba Yayana, jakkarma kai zan ba ka ɗauka min, ai babu dacewa a cikin hakan, kaine zan ganka da kaya na amsa bakai zaka ganni dasu ka amsa ba”.

     Murmushi ya mata cike da jin ta kuma birgeshi. Shine da kansa yay mata rakkiya har sashen Hajiya Iya. Inda a tafiyar tasu take samun damar yima gidan mai sassa da yawa kallon tsaf. A ranta kuwa raya irin jin daɗi ta masu hannu da manda takeyi. Shiyyasa akace wasu tun a duniya suke cinye rabonsu na lahira. Wasu kuma sai kaga ALLAH ya haɗa musu duniyar da lahirar duka. Ya ALLAH kasa muna cikin masu samun dukan gaba ɗaya.............✍  

         

        

     

    *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


*_TYPING📲_*



*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*


*Page 17*

____________________


*_INA MATA ƳAN ƘWALISA BA'ABOTA SON GYARA JIKI DA FATA SUYI ƘWANAS TAMKAR WATA ƊAN DAREN SHABIYAR?!_* 


_Ku marmatso kusa maza na kaiku kantin sauƙi na UMMU DUFAIL gidan sauƙi da biyan buƙatar MATA SARAKAN ado harma da MAZA ƴan ƘWALISA._


*_MATA da yawa kanso su koma Taurari ababen kallo da burgewa ga ma'abota kallo sai dai basusan ina zasu sami sinadarin kankaro wannan ƙyawu da mutuncinba._*


_To maza kuzo kusa dan Bilyn Abdull ta lalubo muku kantin sauƙi na Umm Dufail dakeda kaya masu sauƙi da gamsar da maison afani dasu_.


*_UMMU DUFAIL nada kayan gyaran jiki masu rahusa da inganci da gamsar da mai saya cikin ƙanƙanin lokaci kamar haka👇🏻😁_*



*Customers price list By Ummu Dufail FACE AND BODY*


 SCRUB=2500(300ml)

Face and body mango butter=3k (250ml)

Face cream= 1800

Corretor oil/vitamin C oil=2k

Fairness skin lotion= 2500

Hot chocolate skin lotion 2500

Serum (for Nuckles )2k

Nuckles cream (stubborn)3500

Mix fruits Arabian black =soap 1800

Mix fruit glycerine soap =1900

Beetroot=1900

Coconut, milk,egg..face soap=1200

Lavender mix fruit soap =1800

Body wash =1500

cleanser=1600

Hair spray =700

Hair oil =1500

Hair relaxer =700

Hair butter 1700

Shampoo =1500

Breast=oil 2k powder 2k

Strech marks cream= 2k

Beetroot pink lips =700

Baby care soap glycerine=1k

Baby care butter =1500

Shea butter baby soap =700

Tsumin tula =2200

Tsumin zinariya =1200

Sliming tea =1500

Amarya set =25k

Liquid Arabian black soap =1900

Cleansing water =1500


*_Zaku iya bibiyarta domin gani da ido ta Handle ɗinta na istagram da facebook kamar haka_*


Ummu Dufail @ Facebook 

Ummu Dufail @ instagram

Phone no: 07067943479.


_Ƴammata harma da masu auren karku bari ayi babuku. Dan gyara shine mace a wannan ƙarnin😉👍🏻_.


________________________



*Page 17*


...........Tarba mai ban mamaki da tu'ajjibi Zinneerah ta samu daga hajiya iya, harma da wasu daga cikin jikokinta dake gida ta iske a sashen. Duk yanda taso ta takura kanta saboda baƙunta da rashin sabo sunƙi bata damar hakan. Dan sai faman jera mata tambayoyi suke tamkar ƴan jaridu.

      Dolenta ta saki jiki dasu dan su biyun duk sa'anninta ne. Biyu mata, Bahijja da Meenal wadda taci sunan Hajiya Iya kenan. Sai ɗaya Namiji mai suna Jamal.

    Harga ALLAH Zinneerah taji daɗin kasancewa dasu, dan ta fahimci sunada tarbiyya da sauƙin kai sosai, sannan son ɗan uwansu ko yaya yake wannan trianing da akai musu ne tun asali.

      Cikin katsesu Hajiya Iya dake shafa man zafi a ƙafarta tace, “Niko kun isheni da subaɗi Bahijja. Kuma barni nai hira da Innon tawa kunbi kun hana. Sai ku tashi ku kaita wancan ɗakin kuɗan ƙara gyarawa duk da dai ko jiya Rahi ta garasa ta samu taɗan watsa ruwa ta huta dan shine zai zama ɗakinta”.

       Wani irin waro idanu Jamal yayi tare da zabura. Haka Meenal da Bahijja ma duk sai da suka zaro idanun. Jamal yace, “Granny kina nufin ɗakin Yayanmu fa kenan?”.

      Harara sosai Hajiya iya ta watso musu tana ƙyaɓe fuska. “Eh shi dinfa nake nufi ba waniba. Zuwa yake ƙasar ne da har za'a wani cigaba da faman barin ɗaki haka aljanu na dubulwa a cikinsa? Ubansama dana haifa bai tuna inda nakeba shekara guda balleshi da ke neman haɗa kusan uku”.

       Yanda ta ƙare maganar cikin ɗacin rai ya saka jikinsu duk yay sanyi. A sanyaye Meenal tace, “Kiyi haƙuri Granny, mu dama zaki yarda sai mu tafi da ita sashenmu, kinga saita zauna a ɗakinmu dan ALLAH”.

        “Hakan zaifimin daɗi kuwa Amina. Sai dai kuyi haƙuri nafison zamanta kusa dani akoda yaushe. Koba komai zanga fuskar Innota naji sanyi”.

      Kansu kawai suka iya kaɗa mata, dan tunda ta faɗi haka basu isa jayayya da ita ba. Ko min roƙon da zasu mata kuma bazata canja ra'ayintaba. Zinneerah dai najinsu kanta a ƙasa, sai dai babu abinda ta fahimta a zancen nasu kuma. Amma ganin yanda fara'ar fuskar Hajiya iyan ta ɓace tun daga maganar ne ya saka jikinta yin sanyi itama......

      “Taso muje kiga ɗakinki Sister”. Bahijja ta katse tunanin Zinneerah tana kama hannunta cikin nata. Babu musu ta miƙe tabi bayanta, Meenal da Jamal ma suka mike suka biyosu.

     Kallo Hajiya Iya ta bisu dashi idanunta na cika da ƙwalla. Dan maganar nan ta tado mata da wani babban miki dake zuciyarta tsahon shekaru, wanda a shekarin can da suka shuɗe kusan biyar sun fara ganin haske, amma a wannan karon al'amarin na neman komawa baya. Dan inhar lissafinta bai ƙwace mataba kusan shekararsa ɗaya kenan rabonsa da Nigeria. A take wasu hawaye masu zafi suka fara gangaro mata. Saurin saka hannu tai ta sharesu tare da miƙewa ta nufi hanyar ɗakinta tana ɗan ɗingisa ƙafarta dake mata ciwo tinda safe.


        “Sister Zinneerah lallai keɗin mai sa'a ce”. Meenal ta faɗa tana tura ƙofar ɗakin da suka iso a ɗan lungun corridor ɗin dake facing jikin ɗakin Hajiya Iya. Kafin Zinneerah ta iya cewa wani abu Jamal ya karɓe da cewa “Mai sa'a kuwa ta gasken gaske. Dan kece ta farko a tarihin gidannan kaf da zaki rayu a wannan ɗakin na Yayanmu bayan shi kaɗai dake rayuwa a cikin kayansa idan yazo ƙasar”.

      Haka kawai gaban Zinneerah ya faɗi batare da tasan daliliba. Har suka shige ɗakin ita tama kasa motsawa balle ɗaga ƙafarta. Ganin hakan yasa Jamal dawowa da baya yaja hannunta suka shige ciki, duk da taso ƙoƙarin ƙwace hannun nata amma yaƙi bata dama sai da suka shigo tsakkiyar ƙaton ɗakin da batamasan yanda zata fasaltashi ba a fahimceta.

           Sakin hannunta da Jamal yayi ya bata damar ɗago idanu tanabin ɗakin da kallo. Yayinda hancinta ke shaƙar mata wani irin mayataccen ƙamshi mai sanya zuciya salama. Wani irin saki gaɓɓanta sukai a lokaci ɗaya, ta zubama su Bahijja daketa yaye fararan ƙyallayen da aka lulluɓe komai na cikin ɗakin dasu saboda gudun ƙura ta hausu.

         Sai da suka gama yaye komai ya bayyana Meenal ke faɗin, “Bara na ɗakko kayan shara mu tayaki ɗan ƙara gyarawan baƙunta. Kuma mufa kibar mana wannan ɗari-ɗarin Madam”.

     Cikin tsokana Jamal yace, “Barta sotake mu kirata baƙauya maybe. Gwarama ki sake damu kafin su Yah Haneef su dawo gidannan gobe idan ALLAH ya kaimu, dan zasu cinyeki da bakine”.

       “Kaji munafiki, saina faɗa musu yasin”. Bahijja dake hararsa ta faɗa.

    Yanda Jamal yay da fuskane ya saka dariya kufcema Zinneerah batare data shiryaba. Hakan yay dai-dai da dawowar Meenal ɗauke da kayan shara ɗakin. “Oh ALLAH, kokefa ƴar uwa. Ni kuwa an taɓa faɗa miki keɗin ƙyaƙyƙyawa ce musamman idan kina dariya?”.

          Kasa bata amsa Zinneerah tayi, sai dariyar tatace ta koma murmushi kawai. Hakan datai ya saka su Jamal kwashewa da dariya a tare. Bahijja tace, “Kinga kinsatama ta haɗiye abinta da wannan bakin naki da bai gani ya ƙyale”.......

       “Wai nikan sharar zakuyi ko damuna da shegen surutu?”. Suka jiyo muryar Hajiya Iya dake tunkaro ɗakin.

       A take kowa ya nutsu suka fara ƙoƙarin sharar. Shigowa tai har yanzu fuskarta a dagule da ɓacin ran ɗazun. Tabi ɗakin da kallo da ƙyau kamar mai nazari. A ƙarshe ta sauke idonta akan Zinneerah dake ƙoƙarin tayasu itama. Haka kawai kuma sai taji ɓacin ran nata ya sassauta. Ta sauke ajiyar zuciya da juyawa ta fice a ɗakin.


      Tsaf suka gyara komai dan an horar dasu aiki tuni. Cikin kanƙanin lokaci ƙyawu da tsaruwar ɗakin ya ƙara bayyana a idon mai kallo. Musamman da suka cire labulayen ɗakin duk suka sake canja wasu fararen tas dan dama fararen suka cire. Kaso mafi yawa dake a ɗakin kalar blue and white ne. Sai wasu colors ɗin ɗai-ɗai da ba'a rasaba. Da yawansu kuma an ɓaɓɓoyesu ma.

      Idanu ta lumshe a hankali tana maijin wani abu mai nauyi dake a ƙirjinta yana narkewa sannu-sannu zuwa cikinta. Nannauyar ajiyar zuciyar da bata shirya fitartaba ta kufce mata a karon farko. Kusan a tare Meenal, Bahijja, Jamal suka dubeta. Sai dai babu wanda ya iya cewa komai a cikinsu, dan sun fahimci Zinneerah bata da sakewa da mutane, gata kuma da alama akwai miskilanci tattare da ita.


★★


       Ƙarfe bakwai da wasu mintuna Alhaji Kabir ya iso katafaren family House ɗin nasu. Bayan samun wajen fakin da direba yayi ya tsaya aka buɗe masa ya fito riƙe da leda a hannunsa wadda kowa yasan mai ita. Dan babu fashi kullum sai ya shigo da irin wannan ledar domin mahaifiyarsa koda iyalansa basu samu hakanba. Sanin baya bama kowa dakon ɗaukarta, shi yasa babu wanda ya tunkaresa domin karɓa. Sai dai sauran kayansa da ɗallami driver ya kwasa zuwa sashensa shi da iyalansa. Shi kuma ya nufi sashen Hajiya Iya kansa tsaye.

        Ɗauke da cikkakkiyar sallama a bakinsa ya shigo falon duk da yasan a irin wannan lokacin Hajiya iya na ƙuryar ɗakinta. dan idan tai sallar magriba bata fitowa sai isha'i. Amma yanada tabbacin baza'a rasa wasu daga cikin ƴaƴansaba da basa rabo da sashen a koda yaushe.

    Ilai kuwa yana shiga da fuskar Zinneerah da Meenal ya fara tozali dan sune ke facing ƙofa. A take falon yay tsit kowa ya ƙara nutsuwa. Sai Meenal ce datai saurin miƙewa ta nufesa domin amsar ledar hannun nasa. “Baffah sannu da zuwa?”.

      “Yauwa uwata kune anan?”.

“Eh Baffah, munzo tarbar Sister Zinneerah ne tun ɗazun”.

     Murmushi Alhaji Kabir yayi yana maida kallonsa ga Zinneerah data risinar da kanta ƙasa tun bayan amsa sallamarsa. Ya ƙaraso cikin falon sosai su Bahijja ma na masa barka da dawowa. A hankali Zinneerah ta zamo ƙasa tana faɗin, “Sannu da zuwa Baffah. Ina wuni”.

     Murmushinsa ya sake faɗaɗawa da faɗin, “Yauwa ɗiyata. Welcome to Shira's family”.

       “Thanks you Baffah”. Ta faɗa a hankali cike dajin kunya. 

       Ya cigaba da faɗin, “Yaya kika barmin ƙanwata da ƙannanki da Abbanki?”.

      “Lafiya lau Baffah, sunce suna gaisheka”.

     “Ina amsawa. Alkairin ALLAH yakai garesu. Tashi ki zauna”.

    Babu musu Zinneerah ta miƙe ta koma kusa da Meenal data kaima Hajiya Iya leda ta dawo ta zauna. Shikuma ya wuce bedroom ɗin Hajiya iyan domin gaisheta.


       Tunda yay sallama a yanda ta amsa masa ya saka gabansa faɗuwa. Cikin ƴar ruɗewa ya ƙaraso ƙaton ɗakin nata itama da sassarfa. Gabanta ya zube jikinsa na rawa. “Innata mike faruwa naji muryarki tamkar baƙyajin daɗi?”.

       Ɗago kyawawan idanunta da mafi yawan ƴaƴa da jikokin gidan suka gada a wajenta tai tana kallonsa. A take hawayen da taketa maƙalewa tun ɗazun suka silalo mata tare da murmushi a lokaci guda. Sake ruɗewa Alhaji Kabir yayi idanunsa shima na kawo ruwan hawaye.

     Kanta ta girgiza masa a hankali tana share nata. “Hawayena basu zuba domin kai ba Kabir. Dan kai ɗa ne tamkar da dubu ga kowaɗanne irin iyaye. Nagodema ALLAH domin yayimin ni'imomi masu yawa a rayuwa da har wanda ke a nesa dani bazai ɗauka inada wata damuwa ko jarabawa nima tattare dani ba, kuma har da samunka matsayin ɗa a cikin ni'imomin. Kabir tabbas ɗan uwanka shine jarabawata. Dan ALLAH ka tayani addu'a ALLAH ya bani ikon cinyewa. A lissafin danai yau shekarar Ahmad ɗaya da watanni biyu kenan rabonsa da ƙasarnan. Yanzu ace Kabir har Inno ta rasu Ahmad ya gagara ɗakko iyalansa suzo sumin ta'aziyya. Idanma ita data nisantani dashi bazatazo ba shi bazai iya zuwaba koda shi da Modibbo ne?. Moddibo fa kansa shekararsa uku kenan rabonsa da ƙasarnan. Tunda nai maganar yay auren nan bai sake zuwaba, uwarsa kuma ta hana wannan ƙoɗaɗɗiyar yarinyar zuwa nan ɗin koda ta haihunma. To kosai na mutune zata barsu suzo su raɓi gawata......”

      Ta kasa ƙarasa maganarta saboda kuka daya kufce mata.

      “Innata dan girman ALLAH ki daina kuka. Kiyi haƙuri dan ALLAH, addu'arki da tamu Ahmad yafi buƙata. Kuma insha ALLAH namiki alƙawarin a wannan karon zanbi duk hanyar data dace domin maido ɗan uwana gida. Har ita ɗin da shaiɗancinta dole ta biyosa. inko taƙi wlhy sai dai ta kama gabanta inda ta fito. Amma dan ALLAH kibar kuka Inna”.

      “Kayya Kabir. A baya fa kayi irin wannan namijin ƙoƙarin amma kaga ta sake sabon shiri, harshi Moddibo ɗinma da ada bayabin ra'ayinta yanzu ta sake janyesa. A zatonmu kusancin da Khalipha ya samu dasu zai kawo wani canjin sai gashi ba hakaba”.

       “Insha ALLAH Inna komai zai wuce. Ai duk abinda ya saka kuka wataran zai saka dariya. Duk kuma abinda ya saka dariya wataran sai ya saka kuka. Itama ai gasunan ta haifa indai ƴaƴane ko. kuma Alhmdllh sai ya bata mafi rinjayensu maza. Itama kukan da zatayi akansu sai ya ninka naki sau dubu. Amma dan ALLAH ki daina masa kuka Inna dan shima ba laifinsa bane, anfi ƙarfinsa ne kawai”.

      “Humm ko anfi ƙarfinsa kam da halima. Dan shima kaidin macen yana iske haline. Kai miyasa matan naka basu rabani da kai ba”.

     Kasa cemata komai yayi sai ban haƙuri dai. Sai da yaga hankalinta ya kwanta sanann ya miƙe ya fice domin zuwa gabatar da sallar isha'i tunda ya cinye lokacin zuwa yay wankan anan.

     Bai iske su Zinneerah a falonba yanzu. Da alama sun shige gabatar da sallar suma.


______________★


      Duk yanda Alhaji Kabir yaso rintsawa a daren yau hakan ya gagara. Ba komai ke masa kai kawoba a rai sai tattanawarsa da Mahaifiyarsu akan ɗan uwansa.

       Su uku kacal mahaifiyarsu Hajiya Iya ta haifa a duniya. Shine babba, sai ƙaninsa Ahmad, sai autarsu Bilkisu da ayanzu haka tana Lagos tana aure. Rana ɗaya aka ɗaura masa aure da ɗan uwansa Ahmad, wanda mafi yawan mutane sukafi sani da suna AK Shira. Ba komai yasa ake kiransa da suna AK ba sai tsanain soyayyar da sukema juna tun ƙuruciya. Kasancewar boarding school sukayi acan ake kiransa da suna Ahmad ɗin Kabir. A hankali kuma sai abokai suka koma kiransa a takaice da suna AK Shira. Mai makon Ahmad Abdul-Mutallab Shira kamar yanda shi ake kiransa Kabir Abdul-Mutallab Shira. Bayan sun kammala secondary tare suka wuce ƙasar Turkey ƙaro karatu. Cikin amincin ALLAH suka haɗa digiri ɗinsu na farko dana biyu duk a tare. Tun suna farkon fara digiri na biyu Ahmad ya haɗu da matarsa ta yanzu mai suna Hindatu. Asalin Hindatu ƴar ƙasan Nigeria yace. dan mahaifinta ɗan nanne. Sai dai mahaifiyarta ƴar asalin ƙasar Morocco ce. Amma suna zaune a ƙasar Turkey tun tanada ƙuruciya, acan ta girma tamafi sanin can matsayin ƙasarta fiye da Nigeria dan sukan jima basuzoba. Ƙyaƙyƙyawa ce itaɗin sosai kasancewarta halfcast ce. Sai ALLAH ya bata wani irin usilin ƙyau mai ɗaukar hankalin mai kallonta.

     Duk da yasan ba wannan ƙyawun bane ya ruɗi ɗan uwansa ga sonta, amma shima ya taka rawar gani wajen jan hankalinsa gareta. Bayan sun kammala digirinsu na biyu suka dawo Nigeria kamar yanda mahaifinsu ya buƙata. Dan yana bukatar suzo suyi aure. Koda suka iso suka huta babu wani jan rai iyayensu suka gabatar musu da matan aure. Shi Alhaji Kabir ya amsa da hannu biyu yay godiya dan dama baida ko budurwar. Amma Ahmad ƙiri-ƙiri yace shifa yanada matar aure. Hajiya iya ce ta fara nuna rashin yardarta akan hakan amma ya nuna bamai rabasa da Hindatu dan yana mata so mai zafin gaske. Gudun samun ɓaraka yasa Marigayi Alhaji Abdul-Mutallab zaunar da Hajiya Iya yaymata nasiha harta amince badan ranta yasoba.

       A take aka hau shirin biki, cikin kanƙanin lokaci komai ya kammala dan ana zuwa nemawa Ahmad auren Haindatu babu wani ja'inja aka bashi. Ansha biki na nunawa sa'a lokacin, dan Alhaji Abdul-Mutallab ya tara musu. Bayan biki duk aka kai amare garin Bauchi, harda Hindatu. Ƙyawawan halin Hindatu yasa Hajiya Iya ta fara sonta, sai kuma akazo dandanan ta samu ciki. Duk da Hindatu na karatu a jami'ar Turkey bata taɓa nuna ƙorafinta nason komawa makarantaba. Tai shiru abinta har ALLAH ya sauketa lafiya ta haihu ɗanta namiji da yaci suna Abdul-Mutallab. Amma saboda alkunya suke masa laƙani da suna Adnan, Hajiya Iya kuma na kiransa Moddibo.

     Bayan haihuwarsa da kusan  watanni huɗu Ahmad ya buƙaci sake komawa ƙasar Turkey dan cigaba da karatunsa. Sai dai a baɗini wannan shirin Hindatu ne. Basu kawo komai a ransuba suka amince Ahmad ya ɗauka Hindatu da dansu suka tafi Turkey saboda kowa yasanshi da matuƙar son zurfi a karatu, shi kuma a lokacin matar Kabir ta fara laulayin nata cikin ita.

        Kamar wasa tun daga wannan tafiyar ganin Ahmad ya fara musu wahala. Dan ya samu aiki acanma ta dalilin mahaifin Hindatu. Sannu-sannu ƴaƴa suka fara yawaita a wannan family, yayinda ALLAH yayma Alhaji Abdul-Mutallab rasuwa. Akan wannan rasuwa kuwa saida sukai yaƙi na gaske Ahmad yazo Nigeria. Inda a wannan zuwan nasane Hajiya Iya ta amshe Moddibo ko hakan zaisa Ahmad ya ringa tunawa dasu.

      Hakan kuwa yaso fara tasiri akan Ahmad ɗin, saboda tsananin so da sukema Moddibo daga shi har Hindatu. Sai dai kuma yana kammala secondary daga tafiya karatu ƙasar London aka sake samun matsala suka sake ƙwace abinsu. Ɗan dawowa da Ahmad ɗin ya farayi garesu ta ƙara lalacewa. Sai dai Alhmdllh duk hutun duniya a Nigeria Moddibo keyinsa. Wannan ne ya ɗan sanyaya ran Hajiya Iya. Amma duk da haka basu daina yaƙin son maido Ahmad jikinsu ba. A dalilin Adnan da shima rashin zuwan mahaifin nasa gida ke cin ransa suka sake dawo dashi cikinsu a shekarun nan, sai dai kuma suna murna an samu waraka shima sai Adnan ɗin ya ɗauke tasa ƙafar gaba ɗaya a dalilin aure da Hajiya iya ta matsa masayi.......

         Nannauyan numfashi Baffah ya sauke mai haɗe da ajiyar zuciya saboda fahimtar da yay tunaninsa yayi zurfi. A yanzu haka kuma ba tunanin abinda ya shuɗe bane mai muhimmanci garesa, a'a abinda zaizo shi ya kamata yay tunanin gyarawa kodan farin cikin mahaifiyarsa ma dasu kansu shi da ƴar uwarsa da zuri'arsu. Dan haka ya sake zurfafa a wani dogon tunanin da bai dawo hayyacinsaba sai a wani tsahon lokaci daya samo mafitar da yaji har a cikin ransa ya gamsu da ita sannan.


         ★★★★


   Washe gari daga sallar asuba ya zarto sashen Hajiya iya. Bayan ya zauna sun gaisa ya zayyane mata shawarar da ya yanke a wannan karon. Cikin jimami tace, “Amma Kabiru baka gani wannan shawarar tana kamanceceniya data baya kuwa?”.

        “Eh to Inna tana kama da ita. Sai dai akwai ɗan banbanci da waccan ɗin. Ki dai tayani addu'a, kuma ki ƙara nazari kema akan hakan mugani”. 

      “To shilenan. Ai ba'aƙi ta mutumba inji masu iya magana. ALLAH ya shige mana gaba”.

      “Amin ya rabbi Inna nagode. Ina mutuniyar takine banji motsintaba?”.

      “Oh kana maganar Zinneerah ne? Tana ɗakin Moddibo tunda ba zuwa yakeba ita ai saita zauna. Dan nace ja'iran nan suzo su rinƙa tayata kwana harta saba wai tsoro sukeji sudai. taya zasu iya kwana ɗakin Yayansu bayan kowa yasan dokarsa ba'a shigar masa ɗaki sai da dalili mai ƙarfi”.

       Dariya Baffah yayi yana faɗin, “Inna sunsan halinsa ba wasa yake dasuba ai Babana. Itama Zinneerah ɗin dai gara a gyara mata wani karki haɗa rikici Inna”.

       “Oh to nima tsoron nasa nakeji kenanma ashe?. To yaci ƙaniyarsa shida dokar tasa babu inda zataje. Idan yazo ni basai ya dakeniba mai bauɗaɗɗen halin tsiya irin na uwarsa”.

      Dariya Baffah ya mike yanayi shidai da faɗin, “Ai kunfi kusa Innata.  Wazai yarda ya shiga tsakaninki da Adnan da Khalipha a gidan nan”.

       “Aikam ni yanzu bana yayin wani Moddibo can. Garama Khalipha ɗin duk da shima ja'irin kansane, daka ɗakko laifin takwaran nasa zai fara karewa da yayansu kaza-kaza, saikace akansa aka fara ɗan uwa”.

     Shi dai Baffah dariyarsa yaketa sha harya samu ya gudu domin zuwa yay shirin fita kasuwa.


       Lokacin da Hajiya iya kenan suna maganarsu da Baffah Zinneerah datai kwanan baƙunta a ɗakin data fahinci mai shi mutum ne mai matuƙar daraja da girma ga jama'ar gidan, dan su Meenal ƙiri-ƙiri sunƙi zaman ko mintuna goma a ciki, nacan ta shige cikin masu aikin Hajiya Iya tana tayasu aikin gyaran sashen. Lokacin da Baffah ya fito ya fice suna Kitchen domin haɗa breakfast kasancewar kullum anan Baffah ke karin kumallon safe tare da mahaifiyar tasa.

    Masu aikin sunso hanatayi amma taƙi. Dole suka barta saboda sunsan yaran gidan dama kan shiga ai aiki dasu suma bisa dokar Hajiya Iya. Amma da dan ta iyayensu matane kam da ba hakaba. Itako Hajiya Iya ta tsaya tsayin dakane domin taimakonsu tunda tasan gidan wani zasuje.

     Bayan sun kammala komai tsaf Baba Rahi tace taje tai wanka kafin Hajiya Iya ta fito dan batason ƙazanta ko kaɗan. Shiyyasa kosu kansu idan baka saniba bazaka taɓa ɗauka ƴan aiki bane a gidanma sai an faɗa.............✍


      

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


*_TYPING📲_*



*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*



*Page 18*

____________________


*_INA MATA ƳAN ƘWALISA BA'ABOTA SON GYARA JIKI DA FATA SUYI ƘWANAS TAMKAR WATA ƊAN DAREN SHABIYAR?!_* 


_Ku marmatso kusa maza na kaiku kantin sauƙi na UMMU DUFAIL gidan sauƙi da biyan buƙatar MATA SARAKAN ado harma da MAZA ƴan ƘWALISA._


*_MATA da yawa kanso su koma Taurari ababen kallo da burgewa ga ma'abota kallo sai dai basusan ina zasu sami sinadarin kankaro wannan ƙyawu da mutuncinba._*


_To maza kuzo kusa dan Bilyn Abdull ta lalubo muku kantin sauƙi na Umm Dufail dakeda kaya masu sauƙi da gamsar da maison afani dasu_.


*_UMMU DUFAIL nada kayan gyaran jiki masu rahusa da inganci da gamsar da mai saya cikin ƙanƙanin lokaci kamar haka👇🏻😁_*



*Customers price list By Ummu Dufail FACE AND BODY*


 SCRUB=2500(300ml)

Face and body mango butter=3k (250ml)

Face cream= 1800

Corretor oil/vitamin C oil=2k

Fairness skin lotion= 2500

Hot chocolate skin lotion 2500

Serum (for Nuckles )2k

Nuckles cream (stubborn)3500

Mix fruits Arabian black =soap 1800

Mix fruit glycerine soap =1900

Beetroot=1900

Coconut, milk,egg..face soap=1200

Lavender mix fruit soap =1800

Body wash =1500

cleanser=1600

Hair spray =700

Hair oil =1500

Hair relaxer =700

Hair butter 1700

Shampoo =1500

Breast=oil 2k powder 2k

Strech marks cream= 2k

Beetroot pink lips =700

Baby care soap glycerine=1k

Baby care butter =1500

Shea butter baby soap =700

Tsumin tula =2200

Tsumin zinariya =1200

Sliming tea =1500

Amarya set =25k

Liquid Arabian black soap =1900

Cleansing water =1500


*_Zaku iya bibiyarta domin gani da ido ta Handle ɗinta na istagram da facebook kamar haka_*


Ummu Dufail @ Facebook 

Ummu Dufail @ instagram

Phone no: 07067943479.


_Ƴammata harma da masu auren karku bari ayi babuku. Dan gyara shine mace a wannan ƙarnin😉👍🏻_.


______________________


*Page 18*


...........Washe gari daga sallar asuba Baffah ya zarto sashen Hajiya iya. Bayan ya zauna sun gaisa ya zayyane mata shawarar da ya yanke a wannan karon. Cikin jimami tace, “Amma Kabiru baka gani wannan shawarar tana kamanceceniya data baya kuwa?”.

        “Eh to Inna tana kama da ita. Sai dai akwai ɗan banbanci da waccan ɗin. Ki dai tayani addu'a, kuma ki ƙara nazari kema akan hakan mugani”. 

      “To shilenan. Ai ba'aƙi ta mutumba inji masu iya magana. ALLAH ya shige mana gaba”.

      “Amin ya rabbi Inna nagode. Ina mutuniyar takine banji motsintaba?”.

      “Oh kana maganar Zinneerah ne? Tana ɗakin Moddibo tunda ba zuwa yakeba ita ai saita zauna. Dan nace ja'iran nan suzo su rinƙa tayata kwana harta saba wai tsoro sukeji sudai. taya zasu iya kwana ɗakin Yayansu bayan kowa yasan dokarsa ba'a shigar masa ɗaki sai da dalili mai ƙarfi”.

       Dariya Baffah yayi yana faɗin, “Inna sunsan halinsa ba wasa yake dasuba ai. Itama Zinneerah ɗin dai gara a gyara mata wani karki haɗa rikici Inna”.

       “Oh to nima tsoron nasa nakeji kenanma ashe?. To yaci ƙaniyarsa shida dokar tasa babu inda zataje. Idan yazo ni basai ya dakeniba mai bauɗaɗɗen halin tsiya irin na uwarsa”.

      Dariya Baffah ya mike yanayi shidai da faɗin, “Ai kunfi kusa Innata.  Wazai yarda ya shiga tsakaninki da Adnan da Khalipha a gidan nan”.

       “Aikam ni yanzu bana yayin wani Moddibo can. Garama Khalipha ɗin duk da shima ja'irin kansane, daka ɗakko laifin takwaran nasa zai fara karewa da yayansu kaza-kaza, saikace akansa aka fara ɗan uwa”.

     Shi dai Baffah dariyarsa yaketa sha harya samu ya gudu domin zuwa yay shirin fita kasuwa.


       Lokacin da Hajiya iya kenan suna maganarsu da Baffah Zinneerah datai kwanan baƙunta a ɗakin data fahinci mai shi mutum ne mai matuƙar daraja da girma ga jama'ar gidan, dan su Meenal ƙiri-ƙiri sunƙi zaman ko mintuna goma a ciki, tana can ta shige cikin masu aikin Hajiya Iya tana tayasu aikin gyaran sashen. Lokacin da Baffah ya fito ya fice suna Kitchen domin haɗa breakfast kasancewar kullum anan Baffah ke karin kumallon safe tare da mahaifiyar tasa, weekend ne kawai bayayi anan.

    Masu aikin sunso hanatayi amma taƙi. Dole suka barta saboda sunsan yaran gidan dama kan shiga ai aiki dasu suma bisa dokar Hajiya Iya. Amma da dan ta iyayensu matane kam da ba hakaba. Itako Hajiya Iya ta tsaya tsayin dakane domin taimakonsu tunda tasan gidan wani zasuje.

     Bayan sun kammala komai tsaf Baba Rahi tace taje tai wanka kafin Hajiya Iya ta fito dan batason ƙazanta ko kaɗan. Shiyyasa kosu kansu idan baka saniba bazaka taɓa ɗauka ƴan aiki bane a gidan ma, sai an faɗa.

         Babu musu ta nufi komawa ɗakin data kwana. Ɗakin da kallonsa kawai saka mata wani shakkar zama a cikinsa take shiga. Dan har cikin ranta tanaji cewar matsayinta bai kai na ta zauna wannan ɗakinba da take ƙyautata zaton na musamman ne.

       Kamar yanda ta kasance a ɗarare daren jiya yanzunma a ɗararen tai komai. ALLAH ya taimaketa ma hatta da soson wanka da kayan shafarta ta taho da abinta. Komai na ɗakin bata yarda tai amfani da shiba bayan ruwa, sai bargo data saka a ƙasa ta kwanta a daren jiya.

     Tsaf ta kammala shirinta cikin riga da skirt na atanfa ruwan bula da ratsin fari, sai ɗan baƙi-baƙi kaɗan. Hijjab ƙarami data taho dashi saboda zaman gida ta ɗauka ta saka sannan ta fita. karo suka kusanci da Jamal tai baya da sauri.

     “Oh sorry Sister, dama Granny tace ki fito ke kaɗai ake jira cin abinci”.  Kallonsa tai kamar zatai magana sai kuma tai shiru saboda tinawa da nasihar mahaifiyarta data tuno akan zaman gidan. Tai ɗan murmushi da faɗin, “Ina kwana”.

      Dariya yayi yana susan kai. “Uhm su Jamal an girma. Wai ni kike gaidawa ma kowa?”.

     Karon farko tai dariya da fara tafiya, har cikin rai yanda suke da barkwanci na birgeta. Shima sai ya biyota yana rawa wai an gaishesa, bayan kaf gidan shike gaida kowa. Koda suka iso ƙaton dining ɗin karaɗinsane ya saka kowa maido hankalinsa kansu. Ya ƙaraso garesu yana basu labarin yau an gaisheshi shima ya tashi daga autan gidan nan yanada ƙanwa.

        Babu wandama yaji miya faɗa dan duk hankalinsu nakan Zinneerah da duk ta daburce saboda idanunsu. Ƙasa takai tsugunne dai-dai tana isowa gabansu tace, “Hajiya ina kwana?”.

       Fuskar Hajiya Iya ɗauke da fara'a da kulawa ta amsa mata, tare da tambayarta baƙunta. Kan Zinneerah a ƙasa take amsawa. kafin ta juya ga Baffah shima ta gaidashi da girmamawa. Amsa mata yay shima cikin kulawa da faɗin, “Kinga taso ga abinci, ga kuma ƴan uwanki nan dake gida duka”.

       Kanta ta jinjina masa jikinta na ƙara saki saboda jin idanunsu duk a kanta. batare data miƙe ɗinba tace, “Ina kwanan ku?”.

     Moos'ab ne ya fara sauke numfashi da amsa mata. “Lafiya lau ƴar ƙyaƙyƙyawa, Granny ina kika samo mai kama da Inno haka?”.

      Kafin Hajiya Iya ta bashi amsa Haneef ya amshe da cewa, “Masha ALLAH ko itace ƙanwar tamune?”. Saifudden zaiyi magana shima Baffah da ke shirin fara cin abincin da Abidah ta haɗa masa yace, “Wai ni gidan nan halan duk ƴan jarida muka tarane? Indai kune yanzu sai kowa yace sai ya mata tambaya anan. Ɗiyata taso kinji”.

       Cikin jin kunya ta taso ta zauna kujerar da Ni'ima ta gyara mata. Kallonsu Baffah yayi su duka, danya fahimci har yanzu duk hankulansu naga Zinneerah musamman ƴan samarin ƴaƴan nasa. Yay ɗan murmushin manya yana lumshe ido da buɗewa. “Wannan itace Zinneerah ƙanwarku. Wadda tun kafin zuwanta an sanarma kowa dake gidan nan. Muna fatan zaku karɓeta da hannu biyu ku kuma ɗauke babu wani banbanci daku”.

      Insha ALLAHU Baffah.

Suka haɗa baki wajen faɗa su duka.

    Kansa ya jinjina cike da gamsuwa yana maida dubansa ga Zinneerah da kanta ke ƙasa. “Ɗiyata Zinneerah ɗago ki kalli kowa danki haddace fuskokinsu da sunayensu”.

       Duk da tana cikin yanayin jin nauyi bin umarnin Baffah dolene a gareta. Hakan yasa ta ɗago a hankali. Da wanda ke kusa da Hajiya Iya ya fara. “Wannan sunansa Mas'ood, ƴan biyu ne shi da Moos'ab gashinan. Wannan kuma Saifudden, wannan Haneef, wannan Abidah, wannan Safiyya, wannan Ni'ima. Sai Jamal, Meenal, Bahijja. Akwai yayunki kusan goma da babusu anan. Koda yake ba duka bane yayun naki a cikinsu dan kin girma wasu. Insha ALLAH duk zaki sansu su sanki suma a hankali. Waɗan nan dai sune yanzu tare dake anan gida, zaki kuma kasance da kusan dukansu yanzu a gida insha ALLAH”.

        Fuskarta daɗan murmushi tace, “Nagode Baffah”.

      Murmushin shima yay mata yana jinjina kansa. Yayinda su Haneef suka haɗa baki wajen, “Welcome to Shira's family ƙanwarmu”.

       “Na gode Yayuna”.

Ta faɗa ita cikin son aro jarumtar son sakewa da su. Dan taji daɗin yanda duk suka nuna jin daɗin kasancewarta a cikinsu. 

    Ƴar gajeruwar nasiha Hajiya iya tai musu akan zuminci kafin su fara cin abincinsu a tsanake. Wajen yayi shiru bakajin ko ƙwaƙwƙwaran tarin wani saboda dokace a garesu ba'acin abinci ana magana musamman idan Hajiya Iya da Baffah na waje. Uwa uba kuma Babban Yaya mai gayya mai aiki dashi ko ƙara cokalinka ya cikayi sai kasha uwar harara.


         Koda duk suka kammala duk ficewa sukai, dan dukansu karatu sukeyi a mabanbanta makarantu jami'oi. Wasunsu na gab da kammalawa, wasu kuma yanzu suka fara musamman ƴammatan. Wasu kuma na tsakkiya. Sai su Bahijja dake secondary sun wuce Zinneerah da aji daya, dan suna ss2. Sai dai yau bazasujeba dan suna wani ɗan hutun kwana biyu a gida.

      Bayan wucewar kowa ita dasu Meenal ɗin ne suka gyara dining ɗin. Hajiya Iya kuma ta nufi ɗaki gabatar da sallarta ta walha tana bar musu saƙon raka Zinneerah wajen iyayensu ta gaishesu.

     Suna kuwa kammala gyara wajen suka jata. Meenal ce taja birki lokacin da suke gab da kaiwa tsakkiyar ƙaton harabar gidan nasu. “Kunga ku tsaya a fara da nunama sister kowanne sashe first”.

       “To uwar tsari”. Cewar Jamal da shaƙiyanci.

     Hararsa Meenal tayi sai dai batace komaiba. Bahijja tace, “Da gaskiyar sister ai, a fara da waje”.

      “Naji karku cinyeni da baki malamai. Sister Zinneerah nan inda muka fito shine sashen Granny nasan kin sani ai?”.

    Jamal ya faɗa idonsa a kanta. Batare da jiran amsarta ba ya cigaba. “Wannan na kusa da shi shine sashen Daddy Ahmad ne. Sai dai basa nan suna ƙasar Turkey lokaci-lokaci suke zuwa. Yaransa biyar shima. Yah Ibrahim, Yah Sadiq, Yah Hafeez. Aunty Zuhrah. Sai Aneesa dan bazance mata Aunty ba, kwana tara kawai ta bani a duniya kamar wannan yarinyar”. Ya nuna Meenal.

      “Shashasha ai dai na girmekan ko?”.

        “Oho a banza dai tunda kammu ɗaya”. Ya bata amsa yana mata gwalo.

    Dariya abin nasu keba Zinneerah. Dan haka yanzuma tai murmushi mai faɗi.

       “Yauwa sai nan kuma Sashen Gwaggo Bilkisu ne idan tazo nan take sauka itama. Tana Lagos da yaranta huɗu itama, kada lissafin yay miki yawa zakisan sunayensu suma nan gaba. Sai nan shine sashen su Yah Saifudden. Nan kuma sashen baƙine. Wannan da zamu shiga shine sashenmu, iyalan Baffah kenan”.

    Murmushi Zinneerah tai cike da gamsuwa dajin birgewar tsarin nasu. Batare da tayi maganaba suka nufi sashen Baffah ɗin da yafi na kowa girma a gidan kasancewar yafi kowa yawan iyalai.

      Sun fara shiga katafaren falo da yaji kayan more rayuwa da ƙawa, wanda har suka fice daga cikinsa Zinneerah bata gama kammala kallon daular dake shimfiɗe a cikinsaba. Basu tsaya anan ba suka isa falo na biyu wanda shima ƙatone na gaske harma zai iya ɗara na farko kayan alatu. A tunaninta an gama kenan, sai taga sun shigo wani falon a hannunsu na dama, sai dai shikam madaidaicine bakai na baya girmaba amma ya fisu tsaruwa.

      Hamshaƙiyar mace ƙyaƙyƙyawa dake zaune da waya a kunne ta ɗago tana kallonsu. Fuskarta a sake take sai dai ba murmushi takeba. Zama su Bahijja sukai a kujera suna faɗin, “Barka da safiya Momie”.

      Kasancewar waya take bata amsa musu ba. Tadai ɗaga musu hannu kawai idonta akan Zinneerah data kai zaune ƙasa zuciyarta na harbawa da ganin kamanin matar da Khalipha sosai. Bayan ta kammala ta ajiye wayar tana faɗin, “Masha ALLAH ɗiyata sai yanzu muke ganinki?”.

       “Kuyi haƙuri Momie”. Zinneerah ta faɗa kamar yanda taji su Meenal na kiranta.

      Cikin ƴar dariya tace, “A'a aiba laifi kikaiba ƴata. muna miki maraba da shigowa cikinmu”. 

       Gaba ɗaya kan Zinneerah a kulle yake. Tadai daure ta amsa mata da godiya tana gaisheta cikin girmamawa. Hakan yasaka Hajiya Nafisa jin daɗi har ranta dajin ƙaunar Zinneerah. Sun ɗanja lokaci a sashen Hajiya Nafisa da suke kira Momie nata mata ƴan tambayiyi jefi-jefi da janta da hira. 

       Hajiya Nafisa itace Baffah ya aura bayan rabuwarsa da Hindatu. Itace mahaifiyar Khadija da a yanzu haka tayi aure itada ƴar uwarta Hafsat. Sai Khalifa, Saifudden, da auta Bahijja. Sunɗan jima Kafin su miƙe su fito dan itama wajen aiki zata fita.

    Daga nan sai sashen Hajiya Halima mahaifiyar su Meenal. Wadda suke kira Ummi. Itace ta haifi Mas'ood, Moos'ab, Ni'ima, Meenal auta. Itama ɗin dai ta tarbesu da kulawa da sakewa. Dan tamafi Momie fara'a gata da barkwanci. Yanda Zinneerah ta lura su Jamal sunfi sakewa sosai anan. Nanma sun jima sosai kafin su fito zuwa sashen Hajiya Ai'sha amaryar Baffan da suke kira da suna Ammi. Itace mahaifiyar su Haneef Safiyya, Abidah Jamal auta.

       Mahaifiyar su Jamal ba mace bace mai yawan fara'a. Amma tanada son mutane itama. Dan ta tarbi Zinneerah ɗin da kulawa sosai, harma takai hirarsu tafiyin tsaho anan fiye da kowanne sashe. Basu fitoba sai da akai kiran sallar zuhur suka koma sashen Hajiya Iya data gaji da zuba idon dawowar tasu ma.


★★★


        Lallai da gaske Shira's Family yayma Zinneerah daɗi. A cikin kwanaki huɗu kacal sai gashi ta saki jikinta da kowa, musamman ma su Bahijja dake ɗorata a hanya waɗanda bata da aminai sama dasu a gidan. Zata iya cewa shine gidan zama na farko data shigo bata fuskanci ƙiyayyar waniba a zahiri. Dan inma akwai masu ƙin nata sun danne a zukatansu basu taɓa nuna mataba.

       Daɗin zama cikinsu ya matar da ita batun kwana biyu da akace zatayi ta koma. Abinda kawai ta kasa sakewa da shi shine kwana ɗakin da aka bata matsayin nata. Komai take a cikinsa a ɗararene. Gashi su Meenal basa shiga ɗakin sam. Ko zuwa sukai tana ciki sunfi yarda su jirata a falo harta fito..    

      A randa ta cika kwana na biyar suka koma makaranta. Ranar duk sai taji kuma babu daɗi. Amma janta a jiki da Hajiya iya keyi yay matuƙar ɗebe mata kewar su Little da ke damunta a rai tun zuwanta gidan. Tamkar kuma Hajiya iya ta shiga ranta sai gashima ta kira mata Mama a waya suka gaisa. sai dai su Sadiq duk sun wuce makaranta. Gwarancin Little dake wasa kawai take jiyowa. Tanason tambayar lafiyarsa tanajin kunyar maman Sadiq. Dan haka tai shiru tunda dai ALLAH yasa ta jisa ɗin.


         Zinneerah na zuba ido taji ance ta shirya ta koma gida kodan karatunta sai taji tsit. A ranada ta cika kwanaki tara a gidanma Baffah yasa ta shirya Yah Saifudden ya kaita makarantar su Meenal da sunan sabuwar ɗaliba. Hakan ya bata mamaki dan babu wanda yay mata bayanin za'a canja mata makarantane. Garama Hajiya iya ta mata nasiha akan ta dage sosai karta bari su maidata baya. Tafi son karatunta da nasu Bahijja ya tafi dai-dai.

     Zinneerah ba ƙoƙarine da itaba. Sai dai tanada naci akan abinda takeso. wannan ne ya taimaka mata matuƙa wajen amsa interview da akai mata duk da dai karatun da tayi a gidan Abba ya matuƙar taimaka mata. Da ace sanda ta baro Danya ne to lallai wannan haɗaɗɗiyar makarantar babu fashi aji ɗaya zasu maidata kuwa.

      A yanzunma sunyi batun sai da ta koma js3. Saifudden ne ya roƙa alfarmar barinta a ss2 ɗin da alƙawarin zata dage insha ALLAH. Da yake maganace ta kuɗi kuma su ɗin sunada babban matsayi a makarantar yasa suka bar Zinneerah ɗin Ss2. cikin amincin ALLAH kuma aka kaita ajinsu Meenal. Zokaga farin ciki da murna lokacin da aka rakata ajin a zuwan sabuwar ɗaliba. Malamin na fita Jamal ya fita gaban aji ya sake gabatar musu da Zinneerah matsayin sister ɗinsu ce. Hakan yasa ta samu tarba mai ƙyau daga ƴan ajin dansu Jamal ƙurayene sosai akan ƙoƙari.

      A ranar kam dai babu abinda Zinneerah ta fahimta a wannan aji. Sai ma neman ruɗewa da tsorata da tayi ganin yanda tsarin karatun nasu yake. Sam babu maganar hausa a ajin ma balle ga malami. Turancine da larabci kawai ke tashi. 

    Fahimtar yanda ta shiga ruɗanine ya saka su Bahijja kwantar mata da hankali akan karta damu zata iya itama ai wataran. Badan ta yarda da hakanba tai shiru, amma har cikin ranta a tsorace take kam. Sai dai kuma tana fatan iyawar kodan wasu abubuwa masu yawa dake cimata rai da zuciya a tarihin rayuwarta. Itama tanason ta zama wani abu kodan wani dalili nata dake ɓoye mata a cikin rai game da samuwar ɗan da batasan wanene ubansa ko yanda aka samar da shi ba.


     Bayan tasowarsu ne Hajiya iya ta kira mata Mama a waya suka gaisa. A take ta labartama Maman komai har tana hawayen farin ciki dana kewarsu. Dan tasan dai tunda har aka sakata a makaranta da wahala ace zata koma zama wajen Mamanta sai dai idan anyi hutu. To koba komai dai ai tamayi nesa dasu Sakina iyayen gorin gida dana arziƙi. Kuma karatunta zaifi inganci anan fiye dacan duk da shima Abba bazata taɓa gajiya da yaba masaba a rayuwarta har ƙarahen numfashinta kuwa.


★★★


     Kamar da wasa sai ga rayuwa ta fara canjama Zinneerah alƙibla. Dan kuwa dai da alama *_MAKAUNIYAR ƘADDARA_* data barota da Danya na neman zame mata ƙyaƙyƙyawar nasara mai abubuwan fata ga duk wanda ya tsinci kansa koda a makamancin irin tata rayuwarne. Yau ita Zinneerah mai tallar riɗi da gyaɗa da ɗanwake ce a wanann matsayin. Ita da kashin gidansu ma ya fita matsayi da daraja wajen Inna dasu Yaya Karima. Lallai ta yarda da yawan ƙaddara tsanine na nasara gamai haƙuri insha ALLAH. Sai dai ya danganta ga yanda ƙaddarar tazo maka da kuma yanda kai ka amsheta kai haƙuri da ita.

     Sosai a kallo ɗaya zakaga ɗumbin canjin data samu. Jikinta ya murje matuƙa, ƙyawunta da nutsuwarta na sake fitowa gareta. Yayinda cikakken budurci ke sake huda gaɓɓanta da surarta. Ta kuma dage da naci akan karatu da taimakon su Bahijja duk da sukan sha wahala wani lokacin kafin ta gane abu daƙyau.

     Zuwa yanzu a hankali su Meenal na jan ra'ayinta kwana sashensu fiye da ɗakinta. Wani lokacin kuma wajen Hajiya Iyama take kwana musamman idan ta tashi batajin daɗin ƙafarta haka ko jikinta. Tsakaninta da ɗakin nata bai wuce shiga tai wanka sai kuma gyarawa. Sai randa ALLAH kuma ya ƙaddara zata kwana a cikinsa.

         

       A kwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI sai gasu Zinneerah an cinye hutun zangon farko a tsadajjiyar majaranta. Kwanansu biyar dayin hutu Baffah ya haɗa mata shatara ta arziƙi Yaya Haneef ya kaita gida wajen mahaifiyarta. Da dasu Jamal zasu tafi Baffah yace su bari sai ta tashi dawowa sai suje su ɗakkota tunta dai kwanaki goma zatai kacal ai.

     Haneef ya shiga sun gaisa. Sai dai bai jimaba ya fito ya tafi, dan makaranta zaije kuma yace yanada jarabawane. Amma daɗin tarbar daya samu ga Mama yace zai dawo. Bai iske su Sadiq gidaba suna islamiyya. Little kuma yana barci abinsa.

       Kwatanta irin farin cikin da Zinneerah ta tsinci kanta a ciki ɓata lokacine. Amma tsabar kewar Mama da tayi harda rungumeta. Little kuwa data shiga ta samu yana barci yasha kisses, harda hawayenta ganin yanda ya ƙara girma a watanni uku kacal data ɗauka bata ganshiba. Wani irin son yaron da ƙaunarsa na ƙara tasiri a ranta alamun hankali ya fara game jikinta a yanzun fiye da da.

     Lokacin kuwa data shiga gaida Maman Sakina ai baki ta saki tana kallonta tamkar sokuwa. Hakama dasu Luban suka dawo gidan daga makaranta dan suna jarabawa sai da ƴaƴan cikinsu suka hautsina da ganin canjawar Zinneerah ɗin a ƙanƙanin lokaci. Duk da sunsan dama ƙyaƙyƙyawa ce a yanzu kam ƙyan nata yafi fitowa da armashin gani gamai kallonta.

     Itako sosai ta nuna murnar ganinsu cike da sakewa alamar yanzu akwai banbanci da da kenan. Dan babu wannan yawan duƙar dakan da ɗari-ɗari tattare da ita. Miskilancin nedai kam akwaishi saima abinda yay gaba.

     Sai da suka shiga ɗaki sukaita gulma da zaginta wai dan taje gidan masu kuɗi kanta ke rawa tana musu shan ƙamshi. Duk da har yanzu basusan taka maimain a inda takeba. Har uwarsu ba sani taiba duk bin ƙwaƙwƙaafinta. Koda ta tambayi Abba cayay mata dangin mahaifanta ne suka ɗauketa dama basusan ta baro gida baneba zuwa nan shiyyasa. Daga haka kota masa maganar sai yace taje ta tambayi maman sadiq ɗin mana. Daga haka yake kashe bakin son gulma da tsugudidi.

      Maman halima kuwa taji matuƙar daɗi da canjin da Zinneerah ta samu. Koba komai itama ta samu ingantacciyar rayuwa bisa ga zaluncin Asabe ai.

     Dawowar su Sadiq aka sake kafa sabuwar murna da bidiri har takai ga tashin Little. Sosai girman nasa ya sake bama Zinneerah mamaki dan bakace ɗan shekara ɗaya da rabi bane. Da alama akwaishi da garin jiki kam. Yanda yaga su Aliyu nane da ita shima sai ya nane natan yana gwarancinsa dan maganar tasa bawani ganewa sosai akeba garama maman sadiq.

     Ganin ƴan uwanta yay mata daɗi duk da bata mance dasu Jamal ba suma. Kullum ma babu fashi sai tayi waya dasu ta wayar Hajiya Iya ko cikin wayar ƴammatan gidan............✍

      


*_1~UBAYD MALEEK_*

_By MamuhGee_


*_2~ MAKAUNIYAR QADDARA_*

_By Billyn Abdul_


*_3~ DALAAL_*

_By Miss Xoxo_


*_4~ MABUDIN ZUCIYA_*

_By Hafsat Rano_


*_5~ ALKIBLA_*

_By Safiyya Huguma_


Zaku samu wainnan duka biyar din akan farashin 700,


Guda 5👉700

Guda 4👉500

Guda 3👉450

Guda 2👉400

Guda 1👉300


Zakiyi payment dinku cikin account dinmu dake rubuce na👇👇👇👇

*_0225878823 HAFSAT KABIR UMAR GTBANK_*


Saika tura shedar biyanka ta wannan numbern👇👇

*08085405215*


Idan kuma katin wayane zaka turo da MTN card ta  wannan numbern👇👇👇

*09032345899*


Mungode

*_TM ZAFAFABIYAR🔥_*


*_TYPING📲_*



*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*



*Page 19*

_________________________


*Assalamu alaikum warahmatullah,  shin kinaba amfani da turaren gashi a matsayinki na mace data amsa sunanta idan amsarki aa toga dama tasamu *awwaba scent* *tazomaku* *da turaren fesawa a gashi natural 100% organic *wanda akahada rose water da essential oils tripped action gashi yy kamshi yay kyali kuma moisturiser at *the same time ba anan abun yatsayaba duk wanda yy order zaahada masa da freshener kala hudu ta daki *ta bandaki ta Mopping da turaren wanka a kan kudi 3,000 kacal indai q cikin watan September dinnna ne daganan kuma zasukoma *normal price dinsu, hakanan turarukqn wuta da humra dinmu anyi masu ragi duk me bukata se nememu a 08034236800 ta what's app kokuma ya ziyarci shafinmu  a instagram* @turare_by_awwaba mungode*



______________________



*Page 19*


...........Sosai zaman hutun nan yayama Zinneerah daɗi. Dan koba komai shaƙuwa sosai ta sake shiga tsakaninta da Little, dan yanzun taɗan rage yin kawaici akansa. Hakama ƙannenta koda yaushe suna nane da ita.

      A randa ta cika kwanaki goma sai ga su Jamal babu zato wajen sha ɗaya na safe. Lokacin suna shirin fita gidan sunan ƙanwar Maman Halima. Duk da taso taje gidan sunan sai zuwan nasu ya kauda son fitar, ta shiga murnar ganinsu. Su maman Halima kam dake goye da Little suka tafi bayan sun gaisa dasu Bahijja iyayen rawar kai.

    Sukam babu ruwansu da wata baƙunta. Dan sakin jikinsu sukai tamkar a gidansu. Sai hakan yayma maman sadiq daɗi sosai, dan koba komai hakan girmamawace suka nuna mata. Maman Sakina da yaranta kam sai suka shige ɗaki suna leƙensu ta Window da gulmar a ina su mmn sadiq ɗin suka samo yaran ƴan gayu haka?. Basu da mai basu amsa, dan haka suka cigaba da habaice-habaice da sukar mmn sadiq ɗin harma dasu Meenal da basusan da zamansu a gidanba. Harda cewa kodai a gidansu Zinneerah ke zaune aikin wanke-wanke yanzun?. Sai suka yarda a haka duk da suma sun san faɗane kawai danjin daɗi. Dan Zinneerah batai kama da wadda taje aikatauba.

       Su Jamal ma sun sami rabon nasu zagin sosai, dan koda sukazo suka iske Maman sakina a tsakar gida dasu Luba ko kallo basu ishesuba. Sai mmn halima data tarbesu da fara'a suka gaida cike da girmamawa. Hakanne ya sake baƙanta ran mmn sakina taja ƴaƴanta suka shige ɗaki.

      Wainar filawa Zinneerah tai musu kamar yanda sukace suna buƙata, sai da sukaci suka ƙoshi Abba ya dawo gidan bayan la'asar suka gaisa sanan driver yazo ya kwashesu harda Zinneerah da taso yin sallama da Little da sauran yaran, dan sanda maman halima ta wucene da shi yana barci, ko ganinsu su Bahijja ma bayi sukaiba. To da yakema ba sanin labarinsa sukaiba basu kawo komai a ransuba sun zatama ɗan mmn halima ɗinne duk da dai basuga fuskarsaba.


       Sosai Hajiya iya dasu Yah Moos'ab suka nuna farin cikinsu na dawowarta. Tare da faɗi mata sunyi kewarta kowa a gidan. Cikin ƴar dariyarta tace, “Nima nayi kewarku ai, wani lokacin har mafarkinku nakeyi”.

       Sunji daɗin maganarta har cikin ransu, dan itama suna mata kallone na ɗaya daga cikinsu bawai wadda tazo cin arziƙi gidansu ba. Moos'ab da bai cika yawan maganaba shi dama yaɗan ɗage gira yana gyara kishingiɗar da yay a kujera da faɗin, “Ni ba yarda nai dakeba fa yarinya”. 

     A hankali Zinneerah ta ɗago manyan idanunta farare tas ta zuba a kansa, irin kallon da yake matane ya sakata saurin maida nata ƙasa tsigar jikinta na tashi, ba yaune karan farko da Yah Moos'ab ɗin ke mata irin wannan kallonba, shiyyasa a mafi yawan lokuta bata wani cika sakewa da shiba sosai. Kasa bashi amsa tayi, hakan yasa Saifudden kwashewa da dariya yana faɗin, “Wataran dai zata fashe”.

       “Minene zai fashe?”. Cewar Haneef dake a kusa dashi yana latsa waya.

     Saifudden yace, “No jaridar mai tsadace, duk maiso ya tanaji kuɗi akwai ranar da zan saida muku”.

     Abidah ce tai dariya tanama Saifudden alamar jinjina. “Ai Yah Saif nima na daɗe da harbo jirgin, kasanfa idanuna sun iya gane-gane nima, duk randa suka tashi saya ka nemoni zan ƙara da nawa rahoton”.

     Tsam Zinneerah ta miƙe zata bar wajen, dan haka kawai ta tsargu da zancen nasu, tanaji a ranta kenan suma duk suna sane da Yah Moos'ab ɗin komi?.

      “A'a, auta ina zuwa?”. Cewar Safiyya da sauri.

      “Im ihm Aunty Safiyya zanje cikine nayi wanka”.

     Da sauri Ni'ima tace, “Wankafa? Ba shigowata Granny ke faɗin kina ciki kina wankaba Auta (Mafi yawan lokaci haka suke kiranta auta).

      Kasa magana tai, hakan yasa Saifudden kwashewa da dariya yana raira waƙa. Duka Moos'ab ya kai masa. Yay saurin wuntsilowa a kujerar yana cigaba da dariyarsa. Da sauri Zinneerah tabar wajen ranta fal tsoro. Ɗakin da har yanzu ta kasa sakin jiki da zamansa ta shige tare da faɗawa saman gadon a karo na farko. Tai ɗan murmushi dajan filo ta cusa kanta a ciki. A ranta kuwa rayawa take itakam karsu Yah Saifudden su jawo mata rigima. Ina ita ina soyayya da waninsu bayanma duk kallon yayu take musu itakam. Wannan zance ai da girma yake idan har yazo a yanda zuciyarta ke hankaltar da ita game da take-taken Yah Moos'ab ɗin. 

      Haka ta kasance cikin dogon tunanin da har barci mai nauyi yay awon gaba da ita batare data saniba. Harsuka gama hiratsu kowa ya miƙe zuwa makwancinsa basu sake ganintaba. Hajiya Iya kam dama ta kwanta tuni saboda maganin mura da tasha, kuma dama ita ba'a doguwar hira da ita, tanada saurin barci. Wani lokacinma sai jikokin nata suzo su ƙaraci shirmensu a sashen bata saniba. Dan kullum nanne wajen hiratsu sai dai idan yayansu na gari kam babu sakewa, duk da suna zuwa a hakan.

     

        Sosai Zinneerah taji daɗi barci akan wannan gado da yau ya zame mata na farko, dan ko fitsari bata farka yiba yau saboda daɗin barci. Sai kiran sallar farko na asuba ta buɗe idanunta da ƙyar tana karanto ɗaya daga cikin addu'ar tashi daga barci.


"الحَمْدُ لله الذِي أَحْيَانَا بَعْدَ مَا أَمَاتَنَا وَإِلَيْهِ النُّشُور"

Alhamdu lillahil-lazee ahyana ba'ada ma amatana wa-ilayhin-nushoor.

       Sai da ta bada ratar kusan mintuna uku bata motsaba dan idanunta su ƙara saki sosai sannan ta tashi zaune tare da zuro ƙafarta ta sauka a gadon. Tayi mamakin ganin an kashe mata wuta da lulluɓa mata bargo, sai dai tasan bazai wuce ɗaya daga cikin su Aunty Safiyya ba. Wanka ta farayi da ɗauro alwala ta fito. Bayan ta gabatar da nafila raka'a biyu ta ɗakko AL-QUR'ANI ta fara duba inda akai mata ƙari jiya a islamiyyasu data koma zuwa ta anguwar su mmn sadiq. 

    Tana zaune a wajen har akai salla. Bayan an idar tai Azkar kamar yanda Hajiya Iya ke maimaita mata muhimmancin yinta a kowacce safiya da maraicen duniya. Sai da ta kammala gari yay haske ta miƙe ta gyara ɗakin tsaf kamar yanda ta saba, ta saka kayan ƙamshi ta fice zuwa taya su baba Rahi aiki. Amma sai da ta fara shiga ta gaida Hajiya Iya da mura sannan.

        Sai da suka kammala komai tsaf suka shirya tebir sannan ta koma ɗakin domin yin wanka. 

       Sanin ba kowa ke shigowa ɗakinba sai Hajiya iya yasata fitowa kanta tsaye da towel. Sai ƙarami da take ƙoƙarin naɗe kanta data wanke a ciki. Wani irin mugun tsargawa zuciyarta tayi dai-dai lokacin da take fitowa daga ɗan lungun da toilet ɗin yake. Tsabar ruɗani da firgici batama san ta saki towel ɗin da take ƙoƙarin ɗaurawa kantaba a ƙasa....

     Ƙyaƙyƙyawan matashin dake zaune hakimce a bakin gadon ƙafa ɗaya kan ɗaya waya manne da kunnensa ya ɗago dara-daran idanunsa masu cikar gashi da haske yana kallonta da alamun tsantsar mamaki a cikinsu. Hannunsa yakai bisa kwantaccen sajen fuskarsa da babu yawan fara'a a kanta ya shafa ɗan guntun sakewar dake kanta na ƙoƙarin gushewa gaba ɗaya. Sauke hannun daya shafa fuskar yay yana gyara ɗayan dake riƙe da wayar da yakeyi har yanzun yana janye idanun nasa daga kanta yana furzar da wani irin huci daya saka Zinneerah dawowa hayyacinta ta ƙwalla ƙara dan duk zatonta aljanine kawai ya shigo mata, shiyyasa tai sumar wicin gadi.

      Gaba ɗaya ya saki wayar a ƙasa, yay saurin saka tattausan hannunsa ya toshe kunnuwansa yana runtse idanunsa da ƙarfi.

      

     Kusan rige-rigen shigowa ɗakin akai tsakanin Hajiya Iya da Baba Rahi.  Su duka kan Zinneerah sukayi dan babu wanda ma hankalinsa ya kai kansa. Hajiya Iya ta kamo Zinneerah da alamu suka nuna bata cikin hayyacinta jikinta. “Ya ALLAHU, Zinneerah! Zinneerah kinga buɗe idonki gani tare dake. Miya faru? Ko wani abune ya tsorataki?. Rahi kawo ruwa a bata dan ALLAH da sauri”. 

       Fita Baba Rahi tayi da sauri sai gata da ruwa ta dawo. Amsa Hajiya iya tai ta bama Zinneerah daketa faman ɓoye fuskarta a jikin Hajiya Iya nata jikin na rawa dan ta tsora sosai musamman data sake kallon fuskarsa yanzu hankalinta ya sake tashi. Kaɗan ta sha dan bata tare da nutsuwar shansa. Hannunta na karkarwa ta sake ƙanƙame Hajiya Iya  ta nuna inda yake zaune kunnensa toshe, hakama idanunsa a rufe har yanzu.

       “Aljani, wlhy Aljanine Granny”. Tana maganar hawaye na ziraro mata kamar an buɗe fanfo.

       Daga Hajiya iya har Baba Rahi turus sukayi suna kallonsa suma fuskokinsu ɗauke da mamaki musamman Baba Rahi da sam bataga shigowarsaba duk da tana kitchen tana wanke-wanke. Sai dai tabbas taji baƙon ƙamshin turare datai tunanin ko cikin samarin gidanne suka fara shigowa yin breakfast.

         Fuska hajiya iya ta haɗe da kamo hannun Zinneerah dake nunashi har yanzun ta riƙe, ta sake kwantar da ita a jikinta tana shafa mata baya da sauke ajiyar zuciya. “Kinga Zinneerah kwantar da hankalinki ba aljani bane mutumne”.

     “Wlhy ba mutum bane Granny, aljanine, dan aljanine kawai zai iya buɗe ɗakin dana rufe kuma na cire key ɗin kingansa acan na ajiye......”

       “Shiii, ya isa kiyi shiru, Yayankune ba aljaniba, yanada key a hannunsa shiyyasa ya shigo”.

       Kafin Zinneerah ta samu damar cewa wani abu Baffah ya shigo ɗakin saboda jiyo muryar Zinneerah ɗin dake magana tana kuka, sai kuma ya jiyo hajiya Iya itama.

      “Lafiya kuw....” ya kasa ƙarasawa saboda sauka da idanunsa sukayi akansa shima. A take fara'ar fuskar Baffah ta ɓace ɓat. Saurin duƙawa Baba Rahi tai tana gaishesa. Bai iya amsa mataba sai hannu kawai ya ɗaga mata. hakanne ya sakata tashi da ta fice a ɗakin.

           Hijjabin Zinneerah na salla hajiya iya ta jawo ta saka mata, batare da tace komaiba ta kama hannunta suka fice daga ɗakin. Bayansu Baffah yabi shima batare da yace uffanba.

        Kansa dake a duƙe tun haɗa ido da sukai da baffa ya ɗago a hankali yabisu da kallo har suka fice gaba ɗaya. Sake lumahe idanun yay da furzar da huci mai ƙarfi tare da kai hannunsa ya dafe kansa. 

      

        Tsaye cirko-cirko suka iske yaran gidan da suka fara shigowa sashen. Dan har sunji labarin zuwan Yayan nasu gidan a bakin Yaya Khalipha da sukazo tare.

      Wucesu Hajiya Iya tayi riƙe da hannun Zinneerah dake sharar hawaye ɗakinta. Baffah kuma ya nifi dining shima fuska a ɗaure.

     Baffa mutum ne mai barkwanci ga yaransa, amma idan ransa ya ɓaci dolene kowa ya shiga hankalinsa. Da sauri Safiyya ta taso inda yake ta fara ƙoƙarin haɗa masa abincin gabansa. Hakan yasa suma sauran yaran nufo dining ɗin duk suka zauna. Hajiya Iya ce ta fito daga ɗakinta tana ƙwalama Jamal kira. Dai-dai yana ƙoƙarin zama danshi shigowarsa ma kenan sashen baisan mike faruwa ba.

      “Na'am Granny ”. 

Ya amsa yana maida kujerar daya jawo tare da juyawa gareta. 

     “Ka shiga ɗakin can ka ɗakkoma Zinneerah Uniform ɗinta da jikkarta”.

      Cikin rashin damuwa da abinda tace ɗin, yace, “Okay maa”. 

     Yanda ya nufi ɗakin kansa tsayene ya saka sauran ƴan uwansa binsa da kallo. Bahijja ta saka hannun ta rufe bakinta jin dariya na neman kufce mata. Meenal kam ƙasa tai ƙarƙashin tebir tamkar zata gyara wani abu tayi tata.


       “Oh ni Jamal ni za'a saka na ɗakkoma ƙanwata abu. yau yarinyarnan zatasha ƙwanƙwashe a kai kuwa a class na rantse”. Yay maganar yana tura ƙofar ɗakin da shiga kansa tsaye. 

     Wani wawan birki yaja yana waro idanu waje ganin wanda baiyi zatoba tsaye yana ƙoƙarin zame rigar saman suit ɗinsa. Cikin rawar baki yace, “Bar... Ba.. Barka da zuwa Yayanmu. Kazo lafiya? An barosu lafiya? Ya hanya?”.

     Yanda ya jero gaisuwar kawai zaka fahimci a kiɗime yake. Shiko da ake gaidawar kallo ɗaya yay masa ya janye idanunsa batare daya amsa ko ɗayaba a ciki, dan gaba ɗaya ransa a dagule yake. Yasan shiɗin mai laifine ga mahaifinsa da kakarsa. Amma yayi zaton Baffa ya yafe masa kamar yanda ya roƙesa tun a waya kafin ya taho....

     Da sauri Jamal ya juya zai fice a ɗakin....

          “Mi kake buƙata?”.

   Nutsatstsiyar muryarsa mai kama data rowa ta bayyana cikin kunnuwan Jamal. Tamkar zai fasa kuka ya juyo garesa. “Yayanmu Granny tace nazo na ɗaukama Zinneerah Uniform ɗinta zamu wuce school”.

      Uffan baice da shi ba, sai ma towel daya ɗauka a akwatin da yazo dashi ya nufi toilet abinsa. Jamal na ganin ya shige ya sauke nannauyar ajiyar zuciya, tare da nufar Uniform ɗin Zinneerah dake ajiye a bakin gado ya ɗauka sauri-sauri tare da schoolbag ɗinta da takalma ya fita da gudu.

        Shikam koda ya shiga toilet ɗin kallon tsaf ya shiga masa, dan a rayuwa ya tsani ƙazanta. Jin ƙamshin toilet ɗin gaba ɗaya ya canja daga nashi ya sakashi cije baki a ransa yana raya hukunci da zaima yarinyar nan da har idonta yay tsaurin shigo masa ɗaki tai wanka. Gamsuwa da tsaftar bayin ya sakashi ƙoƙarin ajiye towel ɗin hannunsa a bazata idonsa ya sauka akan B&P ɗin Zinneerah data shanya. Kauda ido yay yana wani cizar baki da rinmtse idanu da ƙarfi, a fusace ya rataye towel ɗin ya fito yana ƙwala kiran sunan Jamal. 

       Wayam babu Jamal a ɗakin alamar ya gudu, ya riƙe ƙugunsa da hannaye duka biyu idanunsa na canja launi saboda haushi. Ƙofa ya nufa kamar zai fita sai kuma ya fasa ya dawo da baya yanayin ƙwafa. Haka ya haƙura ya gudanar da dukan uzirinsa, sai dai sau goma idonsa yakai ga kayan sai sun sami tsarabar harara talatin da tsaki. Sai wani faman yamutsa fuska yake tamkar yau ya fara ganin irinsu.


     Oho ita mai kayanma batasan yanayiba. Dan tanacan tayi shirin makaranta bisa umarnin Hajiya iya. Sai dai ranta cike yake da ruɗani. a kuma matuƙar kiɗime take da ganin wannan fuskar. Tasata gaba Hajiya Iya tai suka fito dining domin karyawa. Baffa ta fara gaidawa sannan su Haneef dasu Ni'ima. Ta bama Meenal da bahijja hannu sukai musabaha sannan ta zauna.

     Hajiya iya kam da suka fito tare abinci ta fara shiryawa. wanda kowa yasan na yayan nasune, shiyyasa duk suke addu'a a ransu kar mutum yazam shi za'a aika yakai masa.

    Ganin Hajiya iya ta zauna bayan tagama yasa kowa ke ƙoƙarin ganin ya gama ya fita, Jamal ne ya fara miƙewa yana kallonsu Zinneerah. Guys kutashi muje kunsan yau Sir Mansur ne damu a period ɗin farko”.

      Daga Meenal har Bahijja sun ramfo saurin nasa. Dan haka suka miƙe da hanzarinsu suna faɗin, “Hakanefa ka tuna mana”.

      Miƙewa Baffah yayi yana goge bakinsa da tissue. Ya ɗan kallesu ya kauda kansa. “Kumuje sai mu saukeku dan zan shiga makarantar taku ne”.

      Sosai daɗi ya kamasu. Duk suka washe bakuna suna kashema juna ido najin daɗi yau tare da Baffahnsu zasuje school. Duk da dama yakan musu haka lokaci zuwa lokaci dan kawai ya sakasu farin ciki.

       Zinneerah dai duk jikinta a sanyaye yake har yanzu. Babu abinda ke mata gizo a zuciya sai ƙyaƙyƙyawar fuskarsa mai cike da kwarjini da kamalar cikar haiba. Sallama sukaima Hajiya iya sukai waje suna ɗagama sauran yayyensu hannu.

             Cikin raɗa-raɗa Saifudden yake cema Moos'ab mumafa mu tashi mu fece dan yau gidanan akwai ƙura tsakanin Granny da Yayanmu. Wannan faɗan kuwa yafi ƙarfin ganinmu koda ta bayan katanga ne”.

    Miƙewar kuwa duk sukayi sunama Hajiya Iya dake kicin-kicin da rai sallama. A dai-dai wannan lokacin Khalipha ya shigo falon da sallama. Kansa ƴammatan sukai cike da ihun murna ƙasa-ƙasa dan gudun kar Yayansu yajiyosu. Fuskarsa washe da murmushi kuwa ya buɗe musu hannayensa. Sai dai harar da Hajiya iya ta balla masa ce ta sakashi maida hannun ya naɗe a ƙirjinsa yana dariya. Duk da haka sai da sukaje suka ɗan fabu da jikinsa suna jera masa kalaman kewarsa da sukayi. 

     Gudun samun matsala yasa sukai masa sallama suka fice su dukansu. Shi kuma ya ƙarasa ga Hajiya iya. Ɗan rungumeta yayi ta gefe yana faɗin, “Oh my sweetheart, i miss you so much”.

       “Oh ai nazata kaima ka koyo halin turawanne ka fara ƙyama da gudun danginka”.

       “Kai! Granny ni na isa. Babu wani ɗaukaka da ALLAH zai mana a duniya mu kyamaceku ai. Dan kune kuka nunamu ga duniyar harta san da zamanmu”.

     Cikin taɓe baki tace, “Kai kasan wannan ai. Banda wasu bauɗaɗɗu masu bahaguwar rayuwa”. Ta ƙare maganar da harar gefenta tana ƙara ɗaure fuska.

      Juyawa Khalipha yay da sauri saboda jin ƙamshinsa, ya kuma tabbatar da shi Hajiya iya ke wannan zancen. Ilai kuwa shine ke takowa inda suke, kuma komai da Hajiya Iyan ta faɗa ya shiga cikin kunnuwansa. Amma yay tamkar bai jiba sai ma kujerar daya ja ta dining ɗin ya zauna.

     Murmushi Khalipha yay yana dubansa. “Barka da fitowa Yayanmu. Yanzu nake batun zuwa na fiddoka kayi breakfast dan nasan kana jin yunwa sosai”.

       Wani ɗan murmushi yayma Khalipha ɗin yana lumshe idanunsa masu yalwar gashi da cikar gira. Khalipha yasan halin kayansa. Dan haka cike da rashin damuwa yace, “Mi za'a haɗa maka?”.

     Kafin ya bashi amsa Hajiya iya ta amshe da faɗin, “Ni ban girka abincina da shi ba. Sai yayi waya su ƴan can London ɗin ko Morocco su kawo masa yaci”.

       Ƙaramar dariya Khalipha yayi da kai hannu ya fara buɗe kwanikan dake shirye akan tray wanda ya tabbatar nasu ne. Shiko gogan hannayensa kawai ya harɗe a ƙirji yana kafe Hajiya iya da kallo.

      “Bar kallona malam karka cinyeni da waɗanan shu'uman idanun naka  lokacin mutuwata baiyiba”.

       A karo na biyu ya sake sakin lallausan murmushi yana kauda kansa gefe. Cikin magana ƙasa-ƙasa yace, “Bazata canjaba kullum”.

      “Anƙi canjawar dan ubanka”. Hajiya iya ta faɗa tana zabga masa harara da masa daƙuwa.

     Bakinsa yaɗan taɓe da ɗaukar wayarsa ya hau latsawa kamar bashine ya takalo rigimarba. Khalipha dai abinci yake haɗa masa yana dariya, dan inhar Yayansu na gidan nan irin wannan rigimar shi da kakar tasu ba sabon abu bane. Sai suyi sau goma a rana su shirya. Hakan kuma bazai hana gobe su ɗora daga inda suka tsayaba.

     Masifa Hajiya Iya ta cigaba dayi, inda take shiga ba nan take fitaba. Shi dai yay mata shiru yanata cin abincinsa hankali kwance. Danshi mutum ne da baya wasa da abinci. Cinsa yake bil haƙƙi da gaskiya a duk lokacin daya samesa. Musamman daya kasance mutum mai tsananin son abincin Nigeria ma.

       Hajiya iya dai batai shiruba sai da tayi mai isarta sanann ta mike tabar wajen. Dan Khalipha ne keta faman bata haƙuri, shiko yayi kamar babu shi a wajen sai cin abinsa yakeyi.  

    Bayanta yabi da kallo harta shige. Ya maido idonsa kan Khalipha, “Besty matarnan bazata taɓa canjawaba da wannan faɗan nata?”.

        Dariya Khalipha yake sosai. “Yayanmu kaimafa mai laifine, bai kamata kai mata shiruba, amma ka barni da bada haƙuri”.

      “Bazaka gane bane, itafa idan kana bata haƙuri kamar tunzurata kakeyi. Bakinta ko gajiya bayayi”.

       “Munafiki, ai inajinka”. Suka jiyo muryar Hajiya Iya da basuji fitowartaba a bayansu.

      Dariyace taso kufce masa. Dan haka ya miƙe da sauri yana goge bakinsa da tissue yabar falon gaba ɗaya. Da alama gaida matan gidan zaijeyi.

          Harya gama ficewa bai daina jiyo masifar Hajiya iya da dariyar Khalipha ba. Ya ɗan dafe kansa yana furzar da huci da faɗin, “Madam Problem”............✍



       *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_TYPING📲_*



*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*



*Page 20*

______________________


*Mg's herbal whitening black soap*



Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗


Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku  zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali 

Ina masu pimples 

Tabo(spot)

Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance 

Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba 


Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki 


Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu


Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself

100%tested nd trusted 


Soap price:3k

Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free


Maiso kindly message 08062991549

Call 08064532391


Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market  b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏


Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝


Mg's skincare



_____________________



*Page 20*


..........Ƙarfe biyar da rabi motar dake ɗakko su Zinneerah makaranta ta shigo harabar gidan. Kamar yanda ta fita gidan da damuwar baƙon dasu Jamal ke kira Yayansu haka ta dawo da ita a rai. Babban damuwarta ya ganta daga ita sai guntun towel a jiki. Gashi yanda taga fuskarsa da yanda su Meenal ke labarinsa tasan ba kirki zaiyiba sam, sai kuma wani abu mai kama da almara da take hangowa, wanda ƙwaƙwalwarta sam ta kasa ɗauka.

        Kamar kazar da ƙwai ya fashema a ciki haka ta nufi sashen Hajiya iya tana mai addu'a a ranta ALLAH yasa baya nan. Koda tazo ƙofar falon sai da ta tsaya tai addu'a sannan ta shigo bakinta da sallama. Da sauri taja birki a taku huɗu, dan tun sakko ƙafarta ciki hancinta ya shaƙo mata mayataccen ƙamshin turare. Bata kawo a ranta falon yakeba idanma shine, sai da ta ƙarasa shigowa sosai idanunta sukai gamo maiban ruɗani, dan a yanzune ta sake samun damar yimasa kallo mai ƙyau.

      Zaune yake bisa kujera 1seater dake facing kofar, ƙafarsa ɗaya kan ɗaya. Hajiya Iya na zaune kujerar gefensa tana dama fura. Sai wanda bataga fuskarba saboda juya mata baya da yayi. Har cikin ranta taji daɗin samunsa bashi kaɗaiba duk da bataso ganin nasaba ma gaba ɗaya.

       Sallamarta Hajiya iya ta amsa fuska ɗauke da murmushi take faɗin, “Ƴan makaranta an dawo?”.

       Cike da ƙarfin hali Zinneerah ta sakima Hajiya Iya murmushi da faɗin, “Eh Granny barka da yamma”.

       “Barka dai Inno na, da alama yau kam an dawo da yunwa naga kinyi zuru-zuru?”.

       Murmushi tayi batare da tace komaiba. Ta ɗan saci kallon inda yake zaune idonsa a wayarsa dake hannunsa yana latsawa tamkar baisan da shigowartaba. Sai dai abinda bata saniba cikin abinda baifi sakkani ashirinba ya gama ƙarema shigar Uniform ɗin jikinta kallo. Skirt ne iyakar ƙwauri pink color. Sai farar shirt dataji guga da baby hijjab fari daya tsaya mata iya ƙirjinta shima dai a gogen yake. Sai farar safa data rufe ƙwaurin nata da farin takalmi. Bayanta goye da school bag ɗinta data saki hannunta guda. Babu mai cewa Zinneerahn danya ce data taɓa rainon ciki harta haifesa yake gudu ko ina da kafarsa a halin yanzun. Baka iya hango komai tattare da ita sai zallar ƙuruciya da jin daɗin rayuwa na canjin data samu cikin ƙanƙanin lokaci.

         “Yayanmu barka da yamma”.

Ta faɗa ciki-ciki tsabar fargaba da tsoron dake mamaye da ita. Harta fidda rai zai amsa sai taga ya ɗaga mata hannu alamar amsawar kenan.

     Gaba tai zata wuce, batare da ta gaida ɗayan wanda bata ganin fuskar tasa ba. A tunaninta ko shi baisan da shigowarta ba. Sai da taɗan gitta su taji ashe waya yake amsawa. Numfashi ta sauke da nufar ɗakin Hajiya Iya da saurinta, dan bata fatan abinda zai sake tsaidata a wajen. Ajiyar zuciya ta sauke a hankali dai-dai tana saɓule school bag ɗinta da zubewa akan sofar ɗakin. Zamewa tai ta kwanta ko jininta daya ɗauke na wucin gadi zai dawo aiki jikinta yanda ya kamata.

        “Kina lafiya kuwa Zinneerah?”.

Hajiya iya data shigo ta faɗa tana kai hannunta saman goshin Zinneerah dake kwance rigingine. Buɗe idanu tai a hankali tana kallon Hajiya Iyan, ta yunƙura zata tashi Hajiya iya tace, “Kinga yi kwanciyarki abunki. Amma kina lafiya dai ko?”.

       “Lafiyata ƙalau Granny, na gajine sosai yau shiyyasa”.

     “Tofa, halan tsalle-tsallen wofin nan naku kukayi a makarantar ko?”. 

    Ƙaramar dariya Zinneerah tayi tana tashi zaune saboda ganin a yanda Hajiya Iya tai magana fuska a yatsine. “Granny yanzu yaya zanyi kayana nacan ɗakin fa. Ni kuma wlhy wannan mutumun tsoro fuskarsama take bani. ALLAH yasa dai baiyi faɗan ganina a ɗakinsaba”.

       “Idan yayi tsoronsa zanjine Zinneerah? Indai Moddibo ne ma bar wahalar da kanki wajen tsoron wani faɗansa na wofi. Shi haka yake baida fara'a dason hayaniya. Harkar kowa kuma ba shiga yakeba sai idan yaso hakan dan kansa. Tashi kije ki ɗakko kayan da zaki saka, zuwa weekend idan ALLAH ya kaimu sai ki tattaro kayan da zakiyi amfani dasu harya tafi kafin ki koma”.

     Cikin waro idanu Zinneerah tace, “Granny kina nufin sake koma masa ɗaki zanyi da zama?”.

       “Oh to kajimin ja'ira bakison ɗakinne?”.

      “Nidai zan zauna dake anan. Ɗazu ɗinnan da ace babu kowa a gidannan da yazo ya sameni a ɗakinsa ai kakkaryani zaiyi yasin”.

     Yanda take maganar da iya gaskiyarta yasa Hajiya Iya yin dariya. “Idan bazaki takuraba anan ɗin nima zanfi jin daɗin ganinki kusa dani. Dama danki sake yasa nace kije ɗakinsa ki zauna a binki ai. Yanzu tashi ki watsa ruwa sai kizo kici abinci duk kinmin zuru-zuru a idanuna”.

       Miƙewa Zinneerah tai tana ƙoƙarin cire baby hijjab ɗinta. Hajiya iya kuma ta fice a ɗakin.


       “Granny wai keda wa naji kuna magana ɗazun ina waya?”.

    Khalipha ya faɗa dai-dai Hajiya iya data fito tana kaiwa zaune. Sai da ta zauna ta bashi amsa da, “Ƙanwarku ce mai kama da Inno. Yanzu zata fito sai ku gaisa”. Cikin rashin damuwa da sonjin daga ina yace, “Okay. Bara naje nan waje ga Sadam yana jirana zamu ɗan fita. Yayanmu baka buƙatar komai?”.

         Har yanzu idanunsa nakan wayarsa tun yanda Zinneerah ta barshi. Ya ɗan ɗago kansa ya duba Khalipha ɗin ya maida. “No jeka abunka. Nima zuwa 6:30 Mahmud zai shigo muɗanyi magana”.

     “Okay bye, insha ALLAH zan dawo nima kafin ya tafi. Dan nasan yau tare zakuci abincin dare. Granny bye”.

       “A dawo lafiya”. Ta faɗa dai-dai yana ɗaga mata hannu zai fice. 


     Koda Zinneerah tai wankan ƙin yarda ta fito ɗaukar kayan tayi, duk da tanajin yunwa ta gwammaci ɗaukar sauran biscuit ɗinta dake cikin jakka taci, a ranta addu'a take ALLAH ya kawo wani acikin su Jamal ya taimaketa ya ɗakko mata kayan. Sai dai addu'arta bataciba. Dan muryar Hajiya Iya ta tsinkayo tana ƙwala mata kira. Hijjab ta ɗauka ta fito badan tasoba. Hajiya iya dake kallonta tunda ta fito tace, “Wai nikam bazakizo kici abinciba kika maƙale a ɗaki kamar wata sabuwar amarya?”.

        “A'a Granny dama yanzu zan fito”. Ta faɗa tana satar kallonsa ta gefen ido. Yanzu kam waya yake a kishingiɗe saɓanin ɗazun. Saurin nufar kitchen tayi ɗebo abincin a bazata ta tsinkayi nutsatstsiyar muryarsa mai kama data rowa cikin kunnenta a karon farko. “Ki kwashe tarkacen da kika barmin a toilet”.  

      Duk da ba ita yake kalloba ta tabbatar da ita yake. Tuna abinda ta bari ɗinne ya saka kunya mai tsanani lulluɓeta. da sauri tabar wajen.

     Gaba ɗaya turarensa mai ƙarfi ya danne nata daya fara zama a ɗakin cikin wuni ɗaya. Toilet ta wuce sum-sum tamkar yana a cikin ɗaki. Ganin alamar yayi amfani da toilet ya ƙara saka zuciyarya shiga cikin wani irin matsananciyar kunya. Ta kwaso kayan tana rintse ido kamar ta fasa ihu. shikenan ya gama gane mata sirrinta wayyo ita Zinne. Koda ta fito sum-sum ta wuce bata yarda ko sashen da suke ta kallaba.

        

      Fitar da yay da daddaren saboda zuwan abokinsa Dr Mahmud ta bama yaran gidan damar shan sharafin hirarsu yanda suka saba. Sai dai anayi ana leƙen waje wai karya shigo. Sai ma ALLAH ya taimakesu har suka tashi bai shigo ɗinba.

     Washe gari da safe ma har suka gama breakfast kowa ya fice yana ɗaki bai fitoba. Kasancewar juma'a ce da wuri su Zinneerah suka dawo gidan. 

              A bedroom ta iske hajiya iya zaune tana karatun AL-QUR'ANI. Bata zaunaba ta ajiye school bag ɗinta da cire hijjab ɗinta ta fice zuwa kitchen dan yunwa takeji, yau bata wani zauna tayi karin kirkiba suka fita makaranta. Gaba ɗaya ta shafa'a da kasancewar sa a gidan. dan haka ta fito kanta tsaye ko ɗan kwali babu akan nata. Sai gashinta data wanke dan zuwa kitso dake ɗaure a tsakkiya. Tanada gashi duk da bamai wani uban tsaho bane, dan yakanzo mata dai har kafaɗa musamman idan ta wankosa a saloon.

        A yanda take tafiyar yasa sam bataga mutum dake tahowa a gabantaba. Gab sukai karo da juna. Ta ɗago a firgice tana murza goshinta zatai magana, amma sai maganar tata ta maƙale a maƙoshi ta tsaya kawai tana kallomsa. Shima ɗin dai kallo yake mata irin na sani, sai dai ya kasa tunano a inda yasan fuskar.

        Baki ta buɗe da nufin ambaton sunansa ya katseta yana murmushi. “Sorry Beauty. Ko kece Sister ɗin tamune?”.

        Saurin haɗiye maganar tata tai itama mamaki na neman kasheta a tsaye. Kenan bai ganetaba komi? Kokuwa basarwace irinta masu hannu da manda. Aiko inhar hakane itama ta iya ai, musamman a yanzu da take ƙara samun wayewar rayuwa da zamantakewa wajen malamta su Jamal.

       Kanta ta kaɗa masa tana ƙaƙaro murmushi. Tace, “Eh nice Yayanmu, kunzo kafiya?”.

        “Alhmdllh, amma kinma sanni kenan?”.

      “Eh mana. Na sanka a bakinsu Bahijja”.

      “Kai-kai a bakin magulmatan gidannan kenan. to ALLAH yasa dai basu koyama ƙanwar tawa gulma ba?”.

         Ƙayataccen murmushi ta saki har haƙoranta na bayyana fili. Hakan yayi dai-dai da isowarsa wajen. Ta buɗe baki da nufin bama Khalipha amsa idanunta suka faɗa cikin nashi. Wani irin yarrr tsigar jikinta ta tashi, tai azamar maida kanta ta duƙar ƙirjinta na bugawa saboda abinda zuciyarta ta hasko mata a yanzunma kamar jiya data fara ganinsa, koma wanda yafi na jiyan, idanunsu iri daya hatta da kwayoyin ciki.

      Juyawa Khalipha yayi domin son ganin abinda ya hanata maganar, yay murmushi a dai-dai sanda yayan nasu ke ƙoƙarin gittasu tamkar baima gansuba. Da sauri Khalipha yace, “Barka Yayanmu”.

     Hannu ya ɗaga masa kawai yawuce abinsa. Hakan yasa Khalipha ƙara matsawa gaban Zinneerah da kanta ke a ƙasa. Cikin raɗa-raɗan magana yace, Beauty bara muje massallaci, idan na dawo zakizo ki tayani hira”. Daga haka yabi bayan Yayan nasu ɗakin Hajiya Iya daya shiga.

        Nannauyan numfashi Zinneerah ta sauke tare da lumshe idanu ta dafe kirjinta. Zuciyarta na gargaɗinta akan abinda ƙwaƙwalwata ke hasko mata maiban tsoro da ruɗani. jiki a saɓule ta wuce kitchen dan neman abinda zata sakama cikinta ko taji dama.


      Sosai ran Zinneerah yake a jagule da tunani mai tarin ruɗani kala-kala. Ba komai ya janyo hakanba sai ganin da taima Khalipha. Wanda zuciyarta taƙi aminece mata cewar bai ganetaba. Amma har a ranta tana shiga ruɗani da al'ajabin yanda ya nuna ɗin. Itako tayi imani da ALLAH ko shekaru fiye da haka sukai bata gansaba duk randa suka haɗu saita ganesa. Kenan itace keta shirmenta shi baimasan tanayiba, koda yake alkairinsa garetane yasa ta kasa mantawa dashi bawai wani abuba. A take ƙwalla suka cika mata idanu, sai dai tai ƙoƙarin hanasu su zubo dan ba wannan matsalar kaɗai bace matsalarta, hadda wadda take tsoron bayyanar tabbatuwarta saboda ɗimuwa.

     Duk yunwar da take iƙirarin ji sai gashi ba wani abincin kirki taciba  bakuma ta yarda ta fitoba har saida ta tabbatar a ranta sunbar gidan.

    Koda ta koma ɗakin Hajiya iya wanka ta farayi itama tai salla sannan tai zaman karanta suratul kahfi. Bayan ta kammala suka gaisa da Hajiya iya take sanar mata “Af Inno na kinga ina neman shafa'a. Idan kin idar da addu'arnan jeki ki gyara Moddibo ɗakinsa”.

      Cikin dauriya da danne damuwoyinta tace, “To Granny”. Daga haka ta miƙe zuwa ɗakin nasa datai zaman watanni kusan uku a ciki. Cikin ƙanƙanin lokaci ta gyara komai ta baza ƙamshi. dan ita bama taga wani datti da ɗakin yayiba. Rufo ɗakin tai ta fito. Hakan yayi dai-dai da fara shigowar samarin gidan falon alamar yanzu suke dawowa daga massallaci. A ƙa'ida kuma duk irin wannan ranar anan suke lunch saɓanin breakfast kawai da sukeyi anan kowacce safiya.

       Ƙasa tai da kanta cike da jin kunyar kallon da Moos'ab ke mata tunda suka haɗa ido. Batare da tayi tunanin hardasu Khalipha ɗin suke tareba itama ta zauna a falon saboda harda Jamal daya ja hannunta suka zauna a centre table ɗin falon yana miƙa mata ledar hannunsa da faɗin, “Surprise sweet sisi”..    

      Murmushi tayi tana ƙoƙarin buɗe ledar. Ganin abinda ke a ciki ya sata waro manyan idanu waje ta ɗago da niyyar yin magana taja birki wajen ganin ta haɗiye abinda ke a bakin nata saboda idanunta da suka sauka akan wanda batai fatan ganiba....

      Ledar hannun nata Khalipha ya zare yana faɗin, “Ƙanwata mi muka samu haka?”.

      Kasa amsa masa tai saboda wani kallo data kasa fassara inda ya dosa da Yah Adnan ya watso mata. Sai dai zata iya fassarashi da kamanni dana gargaɗi ko takaici.

    Tsam ta miƙe batare data iya amsa Khalipha daya fiddo agwaluma ɗaya dake a ledarba yana faɗin, “Lallai kayan daɗin nan dani za'a shashi ƙanwata”.

      Tana ƙoƙarin gittashi tace, “Na bakama Yah Khalipha kasha ma duka kawai”.

        Saurin bin bayanta yay dan shima yaga kallon da Yayan nasu yay mata, wanda ya tabbatar shine ya hanata zama wajen. “No. Kinga tsaya Beauty guda ɗaya ma ya isheni karɓa kayanki”. Badan tasoba dole ta tsaya ta amsa. Shi kuma yace, “Thanks” cike da wani salo daya sanya Moos'ab dake binsu da kallo cike da kishi yay azamar kauda kansa garesu.


      Koda ta samu ta shige bataso sake fitowaba Hajiya Iya ta korota domin zaman yin Lunch. Badan tasoba dole ta biyota, dan ko tace taci ba barinta zataiba sai dai ma tai mata faɗa. Duk sun hallara a dining har Baffa dasu aunty Ni'ima. Baffah ta fara gaidawa da juma'a, sannan ta zauna a kujerar data rage kusa da Khalipha da Meenal. Hajiya Iya kuma ta zauna a mazauninta da kowa ya sani.

          Sai da Ni'ima ta fara miƙewa ta zubama Hajiya iya abincin sannan Baffah. Sanin halin Yayansu itama Safiyya ta miƙe ta zuba masa dukkan abinda tasan yana buƙata a wajen. Daga haka kowa ya fara ƙoƙarin zubama kansa abinda yafi buƙata.

       Zinneerah dai duk jinta take a matuƙar takure. Kaɗan ta zuba dambun cus-cus a filet ɗin gabanta. Tana ƙoƙarin ɗaukar Mango juice ta zuba Khalipha ya rigata azamar ɗauka jug ɗin ya zuba mata a ƙaramin cup yana murmushi. “Thanks you Yaya” ta faɗa a hankali tana ƙoƙarin kai hannu ta ɗauka aka rigata..  

      Da azama ta ɗago fararen idanunta tana tsuke baki dan duk zatonta Jamal ne, kasancewar sun saba irin wannan wasan. “Malami kafa raina min....” ta haɗiye sauran maganar tata da sauri har tana sarƙewa saboda a hannun data hango juice ɗin.

       Kowa dake wajen sai da ya ɗago ya dubeta tare da kallon abinda taima kallo guda ɗin ta duƙar da kanta. Jamal ya ɗan harareta batare da yace komaiba. 

       Duk kansu suka maida ƙasa kowa na mamaki a ransa ganin Yayansune da aikin, harma ya kai juice ɗin bakinsa tamkar bashi ya aikataba. Baffah da Hajiya iya kam da basu fahimci ainahin abinda ya faruba har haɗa baki suke wajen faɗin, “Kubata ruwa mana kuna ganin ta sarƙe”.

     Saurin miƙa mata ruwan Meenal tayi a baki. Babu musu Zinneerah ta buɗe baki ta hau sha. Hajiya iya tace, “Maganin mai cin abinci yana magana ai kenan”.

       Shiru Zinneerah tayi, dan bata da bakin yin bayanin gaskiyar zance. Khalipha dai mamakin abinda Yayan nasu yayi yake a zuciyarsa. Dan shi da kansa yasan baya shan mango juice. Hasalima daga shi sai Baffah suke matuƙar sonsa. Zinneerah ɗinma dan yaga ta nuna tanaso ne ya zuba mata. kauda tunanin yayi a ransa ganin yanda Yayan nasu ya sake cin mur tamkar bai aikata komaiba, sannan kuma yafi kowa sannin halinsa, shiyyasama bai kawo komai a ransa ba.

         Kowa nama Zinneerah sannu shi banda shi, abincinsa ma yaketa faman ci hankali kwance tamkar baya jinsu.

       Tsakurar abincin kawai Zinneerah keyi a takure matuƙa. Sosai zamnsa a wajen yay masifar cika mata ido. Hakama idanun Yah Moos'ab suma sun takura mata. Ga kuma wani irin yanayi mai kama da shauƙi da takeji game da ganin Khalipha, duk da yanda ya nuna bai ganetaba yana damunta cikin rai. Ganin batacin abincin sai juya cokali yasa Baffah yimata magana.

         “Baffah na ƙoshine”.

“Ƙoshi kuma ɗiyata? Haba yaushema kika fara cin abincin, bayanma kaɗan dama naga kin zuba. Kodai baki da lafiyane?”.

     Kai ta girgiza masa da sauri. “A'a Baffah lafiyata ƙalau, barci nakeji”.

        “Barci kuma? A to tashi kije ki kwanta kafin la'asar tayi dan yau lokacin gudu yake ga mai yawan rai...”

     Zaram ta miƙe kafinma Baffah ya rufe baki. Ta nufi ɗakin Hajiya iya tanaji kamar ta runtse ido ta ganta a kwance ko zataji sassauci daga abinda takeji na ruɗani akan mutanen nan uku da sukazo mata da mabanbanta tunani.


       Washe gari weekend suka tashi kowa yana a gida. Sai sune zasu fita islamiyya zuwa yamma. Tunda Zinneerah ta gama taya su Baba Rahi aikin safe ta gudu ɗaki ta sake kwanciya. Har Hajiya iya na mata ƙorafin anya wannan yawan kwanciyar tata ba shawara bace ke damunta?.

      Luf tayi tamkar tai barcin, dan batason Hajiya iya tace yau saita fita dining yin breakfast. Batare da tunanin komaiba hajiya iya tace, “Oh harma kinyi barcin kenan? Dolene nazo na nema miki maganin shawara kuwa”. Daga haka ta cigaba da duba littafin hannunta, Zinneerah kuwa ta ƙara lafewa a bargo.

      Tun tana barcin ƙarya harma na gaskiyar yay gaba da ita. Kasancewar weekend basu zauna breakfast ba sai wajen tara. Iya su yaranne kawai babu Baffah. 

      Shine ƙarshen fitowa sanye cikin wando 3quarter fari da yellow ɗin t-shirt. Gaishesa ƴammatan suka farayi yana ɗaga musu hannu saboda waya dake manne a kunnensa yana magana. Ni'ima ta fara haɗa masa abinci gabansa. Kamar an tsikari Moos'ab ya ɗan wawwaiga yana faɗin. “Wai ina Zinneerah ne?”.

       Saurin ɗagowa Khalipha dake zuba kunu a kofi yay yana kallon Moos'ud saboda jin sunan daya ambata. “Dama sunanta kenan?”. Yay tambayar ga Moos'ab ɗin kansa tsaye. Wani ɗan murmushi Moos'ab yay yana sosa gefen wuyansa alamar dai akwai wata a ƙasa. “Sunanta kenan Yah Khalipha, ya haɗu ko?”. Ya ƙare maganar da ɗage gira.

     Dariya su Haneef sukayi suna masa daƙƙuwa.

         Ɗan jimm Khalipha yayi yana tunani a ransa. sai dai kafin yace wani abu Moos'ab ɗin ya sake faɗin, “Bahijja dubata a ɗakin Granny tazo ta karya”.

      “To Yaya”. Bahijja ta faɗa tana miƙewa. Sai dai babu shiri ta koma ta sake zama saboda wani malalacin kallo da Yayansu ya watso mata a kaikaice, ya kuma ɗauke kansa tamkar bashi yayiba. 

       “A'a yaya kika koma kika zauna kuma? Nace kije ki duba Zinneerah ne fa”. Fuska ta narke tamkar zata fasa kuka tana duban sashen Yayan nasu da yay tamkar baisan abinda akeba a wajen. Dan dama dai duk a hankali suke magana gudun yin laifi a garesa.

     Kallonsa shima Moos'ub ɗin yayi, mamaki ya kamashi ganin hankalinsa bama a garesu yake ba. Cikin faɗa yace, “Bazakije bane komi?”.

       Da sauri ta girgizama Moos'ab ɗin kanta, da idanu ta nuna masa Yayan nasu tana ɗan noƙe kafaɗa. Baki ya sake buɗewa zaiyi magana suka tsinkayi fitar siririn tsakinsa. yaɗan watsama sashin da Moos'ab ɗin yake  kallo. A yanayin maganarsa na rashin son sakewa yace, “Kun isheni da surutu fa”.

        Tsit wajen yay suna satar kallonsa ta ƙasan idanu da mamakin ganin yanda yay maganar tamkar a hasale..........✍

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post