Makauniyar Kaddara page 1-5 Novels Elite

Makauniyar Kaddara page 1-5 Novels Elite

Makauniyar Kaddara page 1-5 Novels Elite

MAKAUNIYAR ƘADDARA😭


            *_Bilyn Abdukk ce🤙🏻_*


*_Da sunan ALLAH mai rahama mai jinƙai. Ya UBANGIJIN al'arshi ka bani ikon rubuta abin zai amfani al'ummar MANZON ALLAH. Ka tsare harshena da alƙalamina rubuta abinda zai cutar da ni da duk wanda zai karanta littafin nan. Ka bani ikon rubuta abinda zai amfaneni duniya da lahira ni da masu karatun._*


*_Ina mai farin cikin sake dawowa a wannan karon tare da ƴan uwana, yanda muka fara lafiya ALLAH ya sa mu gama lafiya, UBANGIJI ya bamu kariya yay riƙo da hannayenmu baki ɗaya._*


*_Ya rabbi ka gafartama Mahaifina da sauran al'umma da suka rigamu gidan gaskiya. Idan tamu tazo ALLAH yasa mucika da imani. ALLAH ka wajabta mana tsoranka da soyayyar MANZON ALLAH😭🙏🏻._*



_Zafafa Next level_


*Page 1*



..............“Inada tabbacin wannan itace tashar da zaki iya samun motar duk wani gari da kike buƙatar zuwa”. Mai napep ya faɗa dai-dai yana samun wajen fakin, da ɗan karkato kansa yana duban yarinyar dake a baya zaune.

      Batace da shi komaiba. Sai ƙoƙarin kwance haɓar zaninta da takeyi jikinta na rawa. Ta miƙa masa ɗari biyar ɗin dake a ƙudundune saboda uban ƙullin da tasha a cikin zani. Baki ya buɗe kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa. Ya ɗan fisgi ƙudundunanniyar ɗari biyar ɗin daga hannunta yana ƙunƙuni ƙasa-ƙasa. 

      A yanzu ɗinma batace da shi komaiba, sai hawayen dake famar zarya daga idanunta zuwa kumatu.

      Tsohuwar ɗari biyu guda biyu da naira talatin a sama ya miƙa mata fuska a tsuke.

    “Nagode”. 

Ta faɗa a karo na farko tana amsar kuɗin. Batare da ta jira amsarsaba ta fito daga Napep ɗin tana kalle-kalle da ƙoƙarin sake maida kuɗin daya bata a haɓar zani ta ƙulle kamar ɗari biyar ɗin ɗazun. 


     A kallo ɗaya zaka iya fahimtar ƙarancin shekarunta. Dan kuwa bazata wuce shekaru sha huɗu ba. A tsarin halitta batai kama da mai taɓin hankaliba, amma a yanayi zaka iya kiranta da mai ƙarancin hankalin. Duk da kuwa babu wani datti ko makamancin hakan a kaf illahirin jikinta.

      Ƙara kai hannu tayi ta share hawayenta a karo na babu adadi, cikin rauni da alamun tsoron dake tattare da ita ta furta, “ALLAH gani gareka. Da kai na dogara, a gareka kuma nake buƙatar taimak......”

     “Ƙanwata ina zakije?”.

Karaɗin wani kwandasta ya katseta batare da takai ƙarshen addu'arta ba. Kallonsa tai da jajayen idanunta dake a kumbure saboda kuka tace, “Danya”.

       “Danya? Ƙanwata sai kinyi ƙarin bayani, dan nikam bamma taɓajin sunan wannan garin ba”.

    Shiru tai alamar nazari, ‘Gaskiyar kwandasta ɗin nan. Danya dai garinsu motama bata shiga sosai. To amma idan bata mantaba lokacin da zasu taho da Hajji Lanti bayan sun fito daga Danya a mashin, a Gozarki suka kwana, washe gari kuma daga Gozarki sukazo kusada, anan suka sami motar Katsina’.

       “Wai kodai bakisan ina kika dosa bane ƴammata?”.

     Kwandasta ɗin nan ya sake katseta. Da sauri tace, “Kusada zanje”.

     “......Kusa da kano, nesa da birnin katsina” kwandasta ya faɗa cike da barkwanci. ita dai batace da shi uffanba, sai ma faman waige-waige da takeyi, har yanzu akwai tsoron ko wani zai iya biyo bayanta tattare da ita.

     “Kinga ga motar da zaki hau can ta kaiki Gidan mutum ɗaya. Inada tabbacin daga can zaki samu motar kusada ƴar ƙyaƙyƙyawa”.

     “Nagode sosai” ta faɗa tana ɗan risinawa. Daga haka tai gaba da sassafa batare data sake bi takansa ba. 

      Tana isowa motar daya nuna mata ko jiran ba'asi bata tsaya yiba saboda jin kwandasta ɗin motar nata faman faɗin, “Charanci, kankia, Gidan mutum ɗaya, Tsanyawa, Bichi, har kano.

    Can baya ta shige inda wata mata ke zaune ita da yaranta biyu da bazasu wuce sa'annintaba. Ta sauke nannauyar ajiyar zuciya dasa hannu ta gyara ɗan labulen jikin gilashin yanda take fatan ko su Hajiya biyota sukayi bama zasu iya ganinta ba. Duk da hakan kuma roƙon ALLAH take a ranta ALLAH yasa motar ta cika da wuri su tafi.


     Addu'ar tata kuwa ta amsu. Dan ko cikin ƙanƙanin lokaci motar ta cika. Ita dai tana duƙunƙune cikin hijjab har kanta. Ko wanda ya shigo ya zauna a gefenta bata kallaba sanda ya shigo. Ta sauke wata nannauyar ajiyar zuciya jin motar ta ɗaga alamar zasu bar cikin tashar.

      Sunyi tafiya mai ɗan tsayi data tabbatar sunbar cikin birnin katsina ta tsinkayi maganar kwandasta na ambaton kowa ya bada kuɗin mota. Ciro kanta tai daga hijjab ɗin bayan ta kunto kuɗin data ɗaure a haɓar zaninta na canjin mai napep. Jin matarnan mai ƴaƴa na tambayar “Nawane gidan mutum ɗaya” ya sata tsaida hankalinta tana jiran amsar kwandasta ɗin itama.

    “Ɗari huɗu ne kuɗinki hajiya”. Ya bata amsa yana amsar kuɗin na kusa da shi.

    Matar tace, “Haba ɗana adai duba. Wlhy jiya a ɗari uku-uku mukazo. Yaran nanma ɗari bibbiyu na biya musu”.

     “Ai jiya kikace hajiya. Jiya kuma ba yau bace. Dan haka kuɗinki keda yaranki dubu da ɗari biyu ne”.

      Zatai magana wani dake can gaba yay saurin amshewa. “A'a fa gaskiya ɗari uku ne, ni kaina ɗazun nan da safe nazo a haka”.

     A take rigima ta kaure tsakanin kwandasta da matarnan da mutumin da yay maganar da safe yazo a ɗari uku. Da ƙyar dai aka tsaya akan ɗari uku da hamsin. 

     Ita dai yarinyarnan dama bata tanka ba. Ta miƙa masa ɗari huɗun da mai napep ya bata canji.

      “Ƙanwata ina zakije?”.

A taƙaice tace, “Gidan mutum ɗaya”.

     Canjin hamsin ya miƙo mata. Batare datace komaiba ta amsa ta maida a haɓar zaninta. Sai dai bata koma cikin hijjabinba tabi ayarin masu kallon hanya. Kasancewar motar mai lafiya ce bayan sallar la'asar kaɗan suka iso gidan mutum ɗaya. Danma sun ɗanyi tsaye-tsaye a hanya na sauke mutane.

          A gidan mutum ɗayarma dai a rikicen take. Dan ba taɓa yin tafiya irin haka ba sai wannan karon. Sanda zasu tafi kuwa hajji Lanti ce tai musu komai. Da ƙyar ta samu ta tambayi wani yaro mai saida biredi inda zata sami motar kusada. Shine ya nuna mata. Tai masa godiya.

       Ta iske ƙananun motoci kusan huɗu dake jere a kan hanyar da yaron yace mata itace hanyar kusada. Lokacin da suka tafi su tun daga cikin kusada suka shigo motar katsina.

     “Ƴammata kusada ne?”.

Wani tsamurmurin saurayi ya faɗa yana nufota. Saurin ɗaga masa kanta tayi alamar eh. Cike da jin daɗi yace, “Yauwa taho muje, dama mutum ɗaya muke nema”.

    Har cikin ranta taji daɗin hakan. Ya nuna mata jar motar data gama fita hayyacinta. “Yauwa shiga nan. Bayin ALLAH a matsa mata mu kama hanya ko”.

      Cike da mita fasinjojin suka shiga muskutawa dan sama mata waje. badan wajen zai wadacetaba ta shiga ta zauna. Sai dai kasancewar ta mai ƙaramin jiki yasa bata takuraba matuƙa. Sai dai waɗanda ta tarar a ciki sunata faman mita sukam an takura musu. Direban ya cika haɗama da son kuɗi. Yanda direba bai tanka musuba itama bata tanka ba. Sai dai acan ƙasan ranta daɗi takeji zata koma gida taga Babanta da su Yaya Tinene, duk da su ba son ganinta sukeba.

      Tsabar rashin isashshiyar lafiyar motar basu iso ba sai gab da magriba, dan sun kwashe kusan awa ɗaya da rabi a hanya. Ga tsaye-tsaye da suka dingayi ana sauke wasu da ɗauka a ƙananun ƙauyika har kusan sau uku.

    Hankalinta bai tashiba sai da suka iso taga kowa na miƙawa direba ɗari da hamsin kuɗin mota. Cike da tashin hankali da fargaba ta miƙa masa naira tamanin ɗin da suka rage mata. Wani banzan kallo yay mata sheƙeƙe yana nuna kuɗin.

    “Naga kina miƙamin murtala huɗu (80n), bakiga abinda kowa ke badawa bane?”.

      Cikin rawar murya da cikowar ƙwalla a idanunta tace, “Wlhy su kaɗaine suka ragemani, dama ɗari biyar ce na taho da ita da ga katsina, to sai naba mai ƴar ƙurƙura......”

      “K! dakata. Wannan damuwarkice ba tawaba. Inda kinsan baki da kuɗin mota da baki bari nayi jigilar ɗakkoki ba ai. Dan haka ni kuɗina kawai na sani ba wai yanda kika taho daga katsina ba”.

       Sharr hawaye suka shiga sakko mata. Ta durƙusa a ƙasa zata fara roƙonsa, hayayyaƙo mata yayi da masifa. A take hankalin mutane ya fara dawowa kansu. Ita dai duƙe take tana kuka da roƙonsa. 

         A mutanen da suka taru wajen duk basu bata goyon bayaba. Acewarsu miyyasa bata faɗa masaba kafin ta shigo. Idan data faɗa in yaso saiya taimaketa. Suma ɗin haƙuri take ta basu ita dai, dan harga ALLAH batasan adadin kuɗin motar ba. Hakama direba da zugar mutane ke sake harzuƙawa yana mata tujara. 

        Tun tana roƙonsu a duƙe harta koma gurfane abin tausayi. A haka wani saurayi da tausayinta ya kamashi ya ciri naira ɗari ya bama mai motar. Daga haka suka sama mata lafiya. Har ƙasa ta duka taima saurayin godiya. Yace karta damu, tadai daina shiga mota babu kuɗi. Gara ma idan bata da shi ɗin ta dinga faɗa kafin ta shiga zaifi sauƙi. Godiya nanma tai masa ta miƙe riƙe da naira talatin ɗin daya sake rage mata tunada an biya mata ɗari.


       A kusada ɗinma ba sanin ina zata gano hanyar garinsu tai ba. Dan tunda tasan kanta bata taɓa zuwa cikin Kusada ba. Iyakarta ƙananun ƙauyukan dake gefen ƙauyensu kawai. 

      Tana son tambaya tanajin tsoro, ga wani azababben ciwon ciki da takeji yana taso mata kaɗan-kaɗan. Duk yanda taso cigaba da tafiya sai ya gagara. Da ƙyar taja ƙafafunta zuwa wata runfa ta zauna. Da alama runfar mai yin faci ne. Kasancewar magriba tayi harya tashi. 

     Zama tai ta duƙunƙune kanta cikin kafafu jikinta na rawa. Ga wata irin zufa na keto mata ta ko ina saboda azabar ciwon ciki. Tun tana zaune har sai da takai kwance a wajen tana juye-juye. Bata damu da cinnakun daketa galla mata cizo ba a jiki, dan ciwon da cikin nata ke mata ya danne komai.

      Tsahon lokacin data ɗauka a yanayin ciwone yasa har dare ya rufa bata saniba. Sai jin garin tai ya rage hayaniyar jama'a. Ba ciwon cikin bane kaɗai matsalarta harda Yunwa da ƙishi. Dan rabonta da abincin kirki tun jiya a gidan Hajiya. Abincin da aka bata a gidan da aka kaita ƙinci tayi sosai, dan tana tsoron taci su yanke mata kanta kamar yanda zuciyarta ke bata danshi suka kaita gidan.

    Tashi tayi zaune a hankali tana ɗan waige-waige. Titin babu haske. hakama jama'a duk sun nufi gidajensu sai ɗai-ɗaiku. Duk yawan motoci da mashinan ɗazun yanzu babusu. Sai wasu da basu wuce uku ba. Mashinanma bazasu gaza haka ba. Sai fitilar mai shayi da take hangowa can a wajen da motocin ke tsayawa (Tasha).

     Komawa tai ta kwanta. Dan haka kawai taji wani shegen tsoro ya turniƙeta. Ta rufe idanunta gam tana karanto abinda ta sani na addu'a. Cikin amincin ALLAH kuwa sai ga barci ya kwasheta. Da alama hakan nada nasaba da gajiyar dake tare da ita ta wahalar tafiya da gudun da taci kafin samun Napep..


★★★★★


       Tun kiran sallar farko na asubahi ta farka da wani irin ciwon ciki. Murkususu ta dingayi tana kuka. Ta jima tana shan azaba kafin ya lafa mata. Zuwa lokacin anata ƙoƙarin shiga sallar asuba. Tashi tai a jikkace, dan yunwa takeji sosai. Ta taka a hankali zuwa inda massallacin tashar nan yake. Butocin da akai alwala ta dinga taɓawa harta sami mai ruwa. Ɗakkowa tai ta dawo wajen rumfarnan. Ta zagaya bayanta tai fitsari da yin alwala. Sauran ruwan kuma ta shanye. Sai a yanzune ta tuna ko sallar La'asar ɗin jiya batayiba. Rabonta da salla tun ta azhar da bayan idarwarta ta gudo.

       A take ta fara maka sallolin nan batare da tabi tsarin daya dace na mai ramuwaba. Sai da ta gama jerosu har asubahi. Zuwa lokacin mutane nata fitowa, hakama masu mashina da motoci.

     Da farko zaman kallonsu tayi. Daga baya kuma saita mike bisa shawarar zuciyarta. Ƙarasawa tai wajen mai  shayin nan daketa ƙoƙarin ɗora tukunyar garwar shayinsa yana raira waƙar shata. bayan ta masa sallama ya amsa ta gaishesa da girmamawa dan babbane ba laifi.

      “Baba dan ALLAH tambaya nake?”.

Ɗago kansa yay ya kalleta a karon farko. “ALLAH yasa na sani ɗiyata”. Ya faɗa da kafeta da kallon ƙurilla.

   Kanta a ƙasa tana ɗan juya yatsun hannunta cikin juna tace, “Baba dan ALLAH inane hanyar Danya?”.

      “Danya! Danya!?. To indai Danya dana sanice ta kusa da Gozarki hanyarta na nan gabas da mu”.

      Jin sunan Gozarki ya sata kallonsa cike da jin daɗi. Ta kaɗa kanta fuskarta na sauyawa alamar farin ciki tace, “Eh itace baba”.

         Yace, “To zaki zauna ki jira masu mashina dake shiga kenan. Idan kuma bazaki iya jiraba ki samu mai mashin anan ki biyasa talatin ya kaiki ainahin Gozarki ɗin anan zaki samu ƴan mashinan Danya”.

      Taji daɗin shawararsa. Hakan yasata masa godiya. Duk da talatin din ta rage mata a jiki, kuma yunwa takeji gara tabi shawararsa. Babu wani jimawa kuwa ta samu mai mashin. Kamar yanda mai shayi ya faɗa talatin mai-mashin din yace zata bashi. Sai da ta bashima sannan ta hau.

     Cikin mintuna ƙalilan suka iso Gozarki. Amma sai da ya kaita har hanyar ƙauyensu Danya. A take farin cikinta ya ƙara bayyana. Harta zauna da nufin jiran masu mashin dan babu wanda ya fito saboda akwai sauran safiya, sai kuma ta mike. Ba komai ta tunaba sai nasihar saurayin jiya daya cika mata naira ɗari. Bata da ko sile. Mizaisata zaman jiran mashin? Gara ta taka da ƙafa, duk da kuwa tasan akwai nisa. Amma ɗokin gata a kusa da gida sai ya gusar mata da komai har yunwar da takeji da rashin daɗin jiki.

       Tafiya ta fara a doguwar hanyar jan birjin da batasan iyakar lokacin ƙarewarsa ba. Ga ɗan sanyin safiya na busawa kaɗan-kaɗan.


      Tayi tafiya mai nisa ciwon cikin nan da batasan dalilinsaba a kwana biyun nan ya ƙara turniketa. Ƙarƙashin bishiyar dalbejiya ta samu ta zauna. Taci murƙususnta da kuka na wani lokaci kafin ta tashi ta cigaba da tafiya. Zuwa lokacin ƴan mashinan garinsu nata fitowa ɗai-ɗai da fasinjoji akai. 

       Kafin ta gama ankara rana ta ƙwalle. Ga yunwa na cigaba da ragaɗar hanjin cikinta. Haka ta cigaba da jurewa tana jan ƙafafu tamkar mai tsohon ciki. A lokacin da dukkan wani ƙarfinta ke gab da ƙarewa ne ta hango rufin ginin makarantarsu dake da matuƙar tsaho fiye da duk gine-ginen gidajen garin. Ta saki murmushin yaƙe idanunta dake ganin duhu-duhu na lumshewa. Sai faman sauke ajiyar zuciya takeyi da sauri-sauri. A hankali hajijiya ta fara juya mata hanyar, saiko gata ƙasa yaraf babu numfashi..........✍




*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_Typing📲_*




     *_😭MAKAUNIYAR ƘADDARA!!😭_*





                *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*




_ZAFAFA 5 NEXT LEVEL_



Page 2




............Saukar ruwa mai bala'in sanyi a jikinta ne ya sakata farkawa a firgice. Ta zabura zata ƙwalla ihu taji an riƙeta.

       Kafin ta gama tantance abinda ke faruwa muryar da bata gama sanin ta wacece ba ta tsinkaya yana faɗin, “Haba innar Karima, yanzu yarinyar da aka tsinto cikin wannan halin akema wannan izayar haka? A ganina kamata yayi musan halin da take ciki ai k.......”

        A fusace, cikin katseshi tace, “Sallau! Ince dai kai ka gama naka?. Kokuwa bayan taimakon kawota gida akwai wata a ƙasa ne a tsakaninku?”.

       Da sauri Sallau ya dubi tsirarun mutane da tarin yara da suka biyo bayanshi saboda ganin a yanda ya shigo da yarinyar cikin garin tamkar mara numfashi.

      Yace, “Haba! Haba! Innar Karima. Da ga taimakon yarinya kuma sai ki fassarani da neman laƙamani laihi. Naga dai na maki bayanin komai ban ɓoye maki a yanda na tsintota bisa hanyar shigowa gari a yashe ƙasa bata lunhwashi ba, kuma agaban kowa na hiɗi”.

       Baki ta ƙyaɓe tana wani juya idanunta abin tsoro, ta nuna masa hanyar ƙofa, “To ga hanya kama gabanka. Taimakonka kuma angode ince dai shikenan daɗa”.

     Cike da takaici Sallau ya buga ƙafarsa ya fito a gidan yana huci. A ransa kuwa sai tsinar Inna ya keyi akan mugun halinta da kowa ya sani a ƙauyen nasu.


      Duk mahawarar dake faruwa a tsakanin Inna da Sallau tana kwance a gefe cikin laimar ruwan da inna ta jiƙeta tana murƙususun azabar ciwon ciki. Yayinda yara da waɗanda suka shigo a manyan ke tsaye cirko-cirko na kallonsu. Matan makwafta nason taimakon yarinyar amma tsoron Inna ya hanasu iya yin komai, dan ba ƙaramar jarababbiya baceba kowa ya sani.

     A wannan halin wani dattijo ya shigo gidan ɗauke da icce saman kansa, sai gatari dake rataye bisa kafaɗarsa ta haggu. Tun a ƙofar gida yaci karo da tsirarun mutane, hakanne ya sakashi shigowa gidan da matuƙar sassafa. Ya jefar da iccen gefe guda saboda ruɗewar sake ganin wasu mutanen da sukafi waɗanda ke a waje yawa. Kafin yace wani abu nishin kukan yarinyar ya sashi saurin kai dubansa gareta.

      “Subahanallahi Zinneerah!!” 

ya faɗa a firgice yana nufar inda yarinyar take. Duk da yanda jikinta ya ɓaci a laimar ruwan daya gauraya da jar ƙasar garin bai fasa saka hannu ya kamota ya ɗago ba. Cike da firgicin da yafi na farko yake sake faɗin, “Zinneerah! K Zinneerah mike hwaruwa dake haka? Daga ina kika hito ne?”.

       Ina Zinneerah batasan yanayi ba, sai faman cigaba da murƙususunta takeyi a jikinsa. Duk ta naɗe masa ƙwaɓaɓɓiyar ƙasar jikinta akan matacciyar rigar yadinsa.

     Duk yanda yaso Zinneerah tayi magana bai samu hakanba. Su kuma waɗanda ke tsaitsaye a gidan tsoron Inna ya hanasu cewa komai. Yayinda ita kuma taketa sakin ɗanwakenta a tukunya tamkar batasan da shigowar mai-gidan ba ma.

     Tsahon lokaci suna a wajen har ciwon ciki ya lafama Zinneerah tai luf a jikin dattijon tana sauke tagwayen ajiyar zuciya. Da tsananin damuwa tattare da muryarsa yace, “Sannu Zinneerah, sannu kinji”.

       Kanta ta ɗago a karon farko ta dubesa, sai kuma ta yunƙura da ƙyar ta tashi zaune tana faɗin, “Baba!” kafin ya bata amsa ta maida dubanta ga sauran mutanen dake a gidan har zuwa kan Inna dake gyara wutar ɗan-wakenta. Ta duba jikinta matsanancin tsoro na bayyana mata a kan fuska. 

     Kafin wani ya samu damar cewa komai Inna ta miƙe a hasale, dan takai matuƙar cika da haushi. Bakin wuta ta ɗauka tana miƙewa. Kafinma tace wani abu an fara rige-rigen fita a gidan da gudu dan kowa yasan hali.

    Da sauri Zinneerah ta kalli dattijon dake mata kallo irin na tsananin damuwa. “Baba yunwa nakeji”. Ta faɗa tana mai raba hankalinta biyu a kallonsa da kallon Inna dake masifa tana bin mutane da bakin wuta.

       Duk da tsoron Inna dake cike fal da ransa bai ƙi amsa ɗiyar tashi ba. Ya miƙe da rawar jiki yana faɗin, “To Zinneerah jirani”. 

       Buta ya ɗauka ya nufi bayinsu, yana shiga ya ajiye butar yana waige-waige. ta inda katangarsu ta faɗi akai dannin itacen geza yay dabarar ficewa a gidan, yasan mutum ɗaya ce zata iya zuwa gidan ta taimaki Zinneerah daga halin Asabe. Duk da yunwar dake cin hanjin cikinsa shima bai fasa ɗaukar hanya ba zuwa ƙauyen Sanni inda babbar ɗiyarsa ke aure. Da yake babu nisa sosai, rafi ne ma kawai ya rabasu.

      A ƙasan ransa yana matuƙar jin ƙuna da zafin halin da ɗiyarsa Zinneerah ke a ciki, sai dai tsoron matarsa Asabe bazai barsa yay maganaba. Shi kansa yaga ƙarfin halinsa ainun a yau da har ya iya fuskantar Zinneerah kai tsaye, sai dai yasan shirun da Asabe tayi bana alkairi bane dan cike take da shi.

     Da wannan tunanin Baba ya iso ƙauyen Sanni.


       Ƙauyen Sanni ƙaramin garine da ko rabin rabin Ƙauyen Danya bai kaiba. Gaba ɗaya gidajen garin basufi goma sha biyarba. Sai dai a kowanne gida zaka samu family house ne mai tarin iyalai.  Kasancewar irin wannan lokacin na rani babu yawan maza duk sun tafi neman kuɗi birni sai mata kawai a gari da yara. Tun daga ƙofar gidansu Gajeje dake jerin gidaje uku da sukafi kowa yawan iyalai a ƙauyen ake jiyo arerewar mata da ihun yara da luguden daga.

    Baba yaɗan matsa ga yaran dake a gindin bishiyar ƙatuwar ceɗiya suna wasan langa. Ɗaya daga cikinsu ya taɓa yana faɗin, “Ɗana ko Gajeje na ciki?”.

       Wanda aka taɓa ɗin ya sauke ƙafarsa dake a ɗane yana kallon dattijon. “Eh baba tana nan, yanzuma suka gama sussukar maiwa anan”.

     “Yauwa dan ALLAH sanar mata ana sallama”.

        Kamar yaron bazaijeba sai kuma ya kwasa da gudu yana faɗin, “Kai Garzali ku jirani indawo”.


      Ba'a wani ja lokaciba wata mata ta fito, a yanayinta zaka ɗauka wani shekarune da ita masu yawa. Sai dai a kallon idanu zaka samu amsar ƙarancin shekarunta. Wahalar rayuwace kawai ta maidata tamkar mai shekaru arba'in a duniya. Ta gyara gyautan zanen data yafo a kanta tana washe baki da fadin, “A'a lale-lale. Baba kaine tahe a tsakkiyar ranarnan haka?”.

       Baba dake duban ɗiyar tashi daso da kauna ya murmusa yana jinjina mata kansa, “Nine kuwa tahe Gajeje”.

      “To sannu da zuwa Baba. Bara na kawo maka tabarma da ruwa ko...”

    Saurin dakatar da ita yayi ganin zata juya. “A'a Gajeje dakata, tahiyarnan tawa bata lahiya bace. Dan haka zama bai ganni anan ba”.

     Cike da tsoro tace, “Wani abune ya faru kuma? Ko Innace tsiyar tata ta motsa yau?”.

      “To ba'ace ba dai Gajeje. Ƴar uwarkice ta dawo cikin wani yanayin da sam ban gane masaba. Yanzu haka na barota a gida tana maɗoɗowar yunwa. Gashi kuma naga ran Asabe a ɓace yake, dan ko uffan taƙi hiɗi mani, kinsan kuma bata barin kowa ya hiɗi yanda akai ko?”.

       “Wai Baba kana nihin Zinni ce ta dawo gida?”. 

    Da damuwa ƙarara a fuskarsa ya ɗaga mata kai.

       Zanen kanta ta gyara kawai rai ɓace tace, “Muje baba. Dan inna zumace sai da wuta. Karta sake bi ta hanyar da tabi a baya ta maidata wani gun kuma”.

      Sosai yaji daɗin hakan. Dan haka suka kamo hanyar komawa Danya suna tattaunawa akan matsalar Inna Asabe da halin da Zinneerah ke ciki a dalilinta.


★★★


         Baba da Gajeje sun iske ƙofar gidan a yamutse da hayaniyar Inna da wasu a mazan maƙwafta da suka kasa haƙuri suka tanka mata akan dukan Zinneerah da tahau yi tun bayan barin Baba gidan. Yayinda Zinneerah ke gefe tana murƙususun ciwon ciki. 

     Ran Gajeje a ɓace da halin mahaifiyar tasu ta shiga cikin rikicin da ƙyar ta lafar da kowa. Kusan minti talatin aka samu wajen ya nutsa. Inna ta shiga gida mutanen dake a ƙofar gidan kuma kowa ya kama gabansa ana zagi da ALLAH wadai da halin Inna Asabe na rashin tausayi.

      Sai a lokacin Gajeje ta samu damar kama Zinneerah dake kwance gefe buɗu-buɗu da ƙasa tamkar an tonita a rami. Gidan ta shiga da ita, Inna zata fara sabuwar jaraba Gajeje ta haɗe fuska tana faɗin, “Innarmu! Innarmu!”.

     Shiru tayi saboda sanin halin babbar ƴar tata itama. Sannan duk yanda takai ga hawa akan masifarta da Gajeje tayi magana bata iya cigaba saboda wani dalilinta daba kowa ya gama saninsa ba. 

       Itama Gajejen bata sake cewa komaiba sai kallon Tinene ƙanwarta tayi. “Ke Tinene ɗaukamin karauni a ɗakinku”.

     Baki Tinene ta cika da iska tana ƙunƙuni, sai dai kuma babu damar ƙinyi. Fuuu ta shige ɗakin kwanansu da ada can shine ɗakin mahaifiyar Zinneerah kafin tabar gidan. Wata tsohuwar tabarmar karauni ta ɗakko zuwa gindin bishiyar mangwaro dake a kusan tsakkiyar gidan. Zinneerah na zaune an jinginata da bishiyar, Baba na daga tsaye gefenta kaɗan yana kallonta dayin hawayen zuci. Sai Gajeje dake can kusa da Inna a gaban murhu taɗan kara ruwa jikin wutar ɗan waken Inna na saidawa dan yay ɗumi.

            Gidan yay tsit babu mai cewa uffan duk da kuwa kowa nada abin cewa a bakinsa. Musamman ma Baba, sai dai tsoron matarsa Inna bazai barsa iya furtawaba duk da tsantsar tausayin ƴarsa dake ransa.

      Gajeje ta juye ruwan ɗumin a wani roban wankansu ta sirka takai banɗaki tazo ta kama Zinneerah ta miƙar. Har banɗaki ta kaita da kanta. Bata wani tsaya jan zance ba ta ɗaurayema Zinneerah jiki da kanta duk da kuwa tanata mammaƙewa dan nauyin yayar tasu da suke kallo tamkar uwa a garesu. Tinene ta ƙwalama kira ta kawo mata zani da riga.

            Sosai Zinneerah taji daɗin jikinta da wannan wanka. sai faman sauke ajiyar zuciya takeyi da lumshe idanu. Baba dake tsaye har yanzu da kansa ya gyara mata tabarmar ta kwantar da ita.

      Inna na kallonsu a kaikaice, watsama Baba wata uwar harara tayi tana yin ƙwafa. Sai dai kuma batace komaiba ta cigaba da tsame ɗanwaken ta.

        Duk da Gajeje taga harar da Innar tasu taima mahaifinsu bata tankaba. Sai ma kwance gefen zaninta tayi tana ciro nera hamsin data sha ƙudindina. “K Tinene zokije nan wajen Dijen kamaye ki sayo mani kunu da suga”.

     “Yaya Gajeje tallafa zan ɗauka, kina ganin Inna harta gama kwashe ɗanwake, gahi Sa'a bata dawo ba, Karima kuma na rimaye”.

      Wani mugun kallo gajeje ta watsamata, a hasale tace, “Ni kike hiɗima haka Tinene?”.

      Kafin Tinene ta bata amsa Inna ta dubesu a hasale. “Wai Gajeje miyasa ke baƙya son zaman lahiyane? Ai gaskiya Tinenen ta hiɗi, inke idonki bai gane miki na kwashe ɗanwakenba”.

       “To amma Innarmu koda shirin ɗaukar ɗanwaken take nanda gidan Dije ne zai gagareta zuwa ta sayo mani kunu? Kenan iya shegen da sukema kowa nima ya hwara zuwa bisa kaina?”.

       Yanda Gajeje ke magana a hasalene ya saka Inna cewa, “K Tinene amshi ki sayo mata, ni bansan wani kace-nace”.

      Tinene na faman tunzura baki da ƙunƙuni tazo ta amshi hamsin ɗin ta fice bayan ta ɗauki wani tsohon kofi. Babu jimawa sai gata da kunun kuwa. Kusan tare suka shigo da Sa'a ɗauke da ƙaton botiki mai ɗauke da sauran gyaɗa da riɗi da taje talla.

      Da sauri ta ƙarasa shigowa tana fadin, “Kai, Kai, Zinni! Yaushe kika dawo?”.

       Murmushin ƙarfin hali Zinneerah taima Yayar tata da itama ke ƙaunarta a gidan, sai dai kuma ta kasa bata amsa sai Yaya Gajeje ce dake zuba suga a kunun da Tinene ta sayo ta bata amsar.

    Kafin Sa'a da hawaye suka cikama ido tace wani abu Gajeje ta maida hankalinta ga Tinene. “K samo mani lidde”.

      “Mu bamu da lidde nan gidan”. Cewar Tinene tana murguɗa baki.

    Jikake bamm! A goshin Tinene, Gajeje ta jefa mata murfin kwano dake kusa da su.

     A take ta zube ƙasa ta fara kururuwar ihu kamar wandda aka kashe. Inna ta saki kwanon yaji a ƙasa ta nufi ƴar tata da sauri. “Gajeje kashemin yarinya zakiyi akan wannan sheɗaniyar yarinyar data gudu yawon tambaɗarta?”.

      “Kaɗanma na mata Innarmu”.

Gajeje ta bata amsa rai ɓace. 

      Cikin raɗa-raɗa Sa'a data je ta ɗakko mata ludayin tace, “Yaya Gajeje ki ƙyalesu dan ALLAH, karki tahi gida a huce kan Zinni. Kindai san halin Innarmu ai”.

     Shiru Gajeje tayi bata tankaba. Baba ma dake tsaye har yanzu bai tanka musunba, hasalima hankalinsa na kan Zinneerah da ke shan kunun cike da zalamar yunwar da takeji.


      Zuwan Gajeje gidan ya matuƙar taimakawa wajen bama Zinneerah kulawa. Inda kuma ya katange duk wani bala'i da masifar dake cin Inna a rai. Dan bayanma ta kammala saida ɗanwakenta su Tinene sun ɗauka wani sun wuce talla zani ta ɗauka ta fice gidan wai taje barka wani ƙauye dake can gefensu shima.

     Hakan yama baba daɗi sosai. Dan koba komai sa samu damar jin yaya akai Zinneerah tabar gida a kwanaki ashirin da shida da suka shuɗe, da kuma yanda akai ta dawo musu yau a wannan halin?.

          Suna zaune shi da Gajeje suna tattaunawa akan hakan Zinneerah dake barci tun ɗazun ta farka a firgice da ciwon ciki. Duk kanta sukayo suna tambayar ko lafiya?. Bata iya amsasuba sai da ya lafa mata.

    Ta share hawayen dake sauka a kumatunta. “Yaya Gajeje cikina kemin ciwo”.

     Basu kawo komai a ransuba sai yunwa. Dan haka Gajeje tace, “Zinni yunwace nasani. Sannu kinji. Idan zaki iya tashi kiyo alwala kiyi sallar azahar da la'asar sai kizo ga abinci kici”.

           “Zan iya yaya Gajeje”  

Ta faɗa tana maida kallonta ga baba dake kallonta cike da raunin zuciya dana idanu.

   “Baba ina wuni”.

Murmushin ƙarfin hali yay mata da shafa kanta. “Lafiya lau Uwata yaya jikin?”.

      “Da sauƙi baba”.

“To madalla. tashi kiyi sallar maraice na ƙara yi”.

      Bata musaba ta miƙe. Jin gidan shiru ya sata sanin Inna da su Tinene duk sun fice. Hakan ya mata daɗi. Alwala tayo tazo ta wucesu zuwa ɗakin kwanansu. Babu abinda ya canja a ɗakin nasu sai ma shirgin kayan dauɗar su Yaya Sa'a. Dama itace mai kimtsa ɗakin dayi musu wanki. Kayan taɗan ture gefe ta tayar da salla cike da ƙarfin hali dan batajin daɗin jikinta gaba ɗaya. Duk da sallar ba'a cikin tsari akayitaba tadai gabatar ta sake komawa wajen baba da yaya gajeje.

          Abinci yaya Gajeje ta fara bata taci. duk da yunwar da take ji har yanzu taci abincin a nutse dan sam dama ita bata da garaje ko gaggawa. Bayan ta kammala ta wanke hannu ne Yaya Gajeje ta ce, “Zinni kinga marece yayi inason na koma gida nabar su Rabi'u. Munason ki nutsu ki faɗa mana yaya akai kika bar gida ne batare da sanin kowaba? Ina kuma kikaje?”.

          Duk da ƙarancin shekarunta hakan bai hanata jin ɗaci ba a ranta. Ta share hawayen dake rige-rigen zubo mata tana gyara zama. “Baba wlhy ban gudu ba. Bayan tafiyarka kasuwa sai I.......

       Jin tayi shiru tana kallon hanyar shigowa yasa Baba da Gajeje saurin kallon wajen suma. Inna ce ke shigowa cikin gidan tamkar wadda aja jeho.

     Ganin yanda duk suka watso mata idanu ya sata fara magana a harzuƙe. “Halan cin nama na akeyi kuka watso mani idanu haka?. Wani annamimancin kike hiɗi masu a kaina ko?”.

     Ta ƙare maganar tana watsama Zinneerah mugun kallo.

        Gajeje ta dubi Baba da yay ƙasa da kansa. ta dubi Zinneerah da itama kan nata ke a ƙasa tana hawaye. Wani irin tausayinsu da jin zafin mahaifiyar tasune ya ɗarsu a ranta, musamman yanda take ƙasƙantar musu da mahaifi a gabansu duk da tsufansa. taɗan girgiza kanta tana dubanta. “Amma Inna miya kawo wannan zancen daga shigowarki? Yarinyar da ke cikin halin ciwo wane kuma munahincinki zatayi?. Ni a ganina kamata yayi kema ki shiga jerin masu murna da dawowar Zinni gida kodan tashin hankalin da muka shiga na rashin sanin inda take a kwanaki ashirin da shida ɗin nan”.

       “Tunda uwatace ta ɓata ko? Kune kuke ɗauka ɓata tayi dama ai, yarinyar da ta tafi yawan taɓaɗanta data saba har kuke damuwa da inda taje. Inda ba guduwa taiba wane shege ne ya dawo da ita yanzu da ƙahwarta?. adai jura zuwa rafi, wataran muna zaune za'a shigo mamu da ɗan dakan kuka na tabbacin yawon tazubar....”

    Tsam baba ya miƙe batare da cewa uffanba ya fice gidan. Itama Gajeje rai ɓace ta miƙe tana magana cike da rawar murya. “Innarmu wannan hurucin naki dai kau sam bai dace ba. Dan koba komai itama Zinni ɗiya take garegi, yanda kuwa take mace haka Sa'a da Tinene da Karima suke mata. Baƙya tsoron mugun alkaba'in da kike hiɗi gareta ya dawo bisa kanmu ne”.

      Wani mugun kallo Inna taima Gajeje. Kamar zatai magana sai kuma tai shiru. Itama Gajejen bata sake tankawaba sai miƙar da Zinneerah da ke kuka tayi suka shige ɗaki. Sai da taga ta kwanta sanann ta fara magana. “Zinni bara naje gida, insha ALLAHU gobe da hwarar sahiya zan dawo, dan akwai raɗin suna gidan malam mato dama da zamu shigo. To daga can nan zan wuto na yini. Ki ƙara haƙuri da halin Innarmu watarana sai labari kinji”.

       Kai Zinneerah ta ɗaga mata tana share hawaye. Muryarta na rawa tace, “Nagode Yaya Gajeje”.

    Murmushi kawai Gajeje tayi da shafa kanta ta fito a ɗakin. kai tsaye ɗakin Inna ta nufa dan tanaso suyi magana.............✍



      *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_Typing📲_*




     *_😭MAKAUNIYAR ƘADDARA!!😭_*





                *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*



_________________________

Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗


Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku  zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali 

Ina masu pimples 

Tabo(spot)

Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance 

Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba 


Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki 


Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu


Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself

100%tested nd trusted 


Soap price:3k

Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free


Maiso kindly message 08062991549

Call 08064532391


Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market  b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏


Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝


Mg's skincare


Mg's bakery 

You can still order ur birthday cake, cupcake,slice cake,meat pie,shawarma,samosa nd spring rolls for ur event @mg's bakery

Kindly call or chat 

07046881166

07067210195

08062991549


Masu bukatar abayas,takalma da jakunkuna,ashobe,laces d atamfofi, materials nd the rest 

07046881166

👏🤝

_________________________



_ZAFAFA 5 NEXT LEVEL_



*Page 3*



............Gajeje bata wani jima ba a ɗakin Inna tafito rai ɓace alamar dai wani rikicin suka sake tafkawa. Tana fita a gidan kuwa Inna ta fito a matuƙar hasale itama.

    Ɗakin su Zinneerah ta shiga. Zinneerah dake zaune tana hawaye har yanzun sai jin saukar lafiyayyen mari tayi. Zabura tayi zata ƙwalla ihu Inna ta daka mata tsawa.

      “Munahika yimani shiru kona lallasaki. Dan uban daya haiheki sheri da kikai shirin ƙullamani ashe? Wa billahillazi koda wasa kika sanarma wani a yanda kika bar gidanga sai na lahira ya hiki jin daɗi. Idan kuma kiji ƙarya don ALLAH ki hiɗi masu yanda akayi. Aradun ALLAH ubanki ma sai na ci masa bura-uba bamake kadaiba dan buhun ubanki. Lalatacciya kawai mai shegen nunkuhurci irin na uwarta”.

       Ita dai Zinneerah kuka kawai take jikinta na rawa dan tsoron Inna da takeyi. Sai da ta gama zazzage mata ruwan bala'i iri-iri sannan ta fice a ɗakin.


    Kuka kam Zinneerah ta shashi matuƙa. Ga ciwon da cikinta kanyi lokaci zuwa lokaci. Dawowar Sa'a gidan da kayan ɗanwake ta samu tsagaitawar kukan saboda lallashinta da Sa'a ta zauna yi. Ganin yanda Sa'a ta nuna matuƙar damuwarta yasata shanye sauran kukan nata dan ba yaune farauba a gareta ga halin Inna matar ubanta. 


WASHE GARI. 


       Da safe kamar yanda ta saba kafin tayi tafiya tanayin sallar asubahi ta fito tsakar gida ta hau shara. Duk da sanyin dake busawa na sanyin safiya haka taima tsakar gidan ƙwal da shara, ta gyara turken dabbobin Inna ta zuba musu sabon abincinsu. Sannan tazo ta fara haɗa wuta. Cikin dauriya take komai, dan wani irin zazzaɓine ke ratsa dukkan ɓargon jikinta a hankali. Haka ta cigaba da daurewa harta kammala dukkan ayyukanta wajibabbu a gidan. 

     Babu wanda ya fito a mutanen gidan sai can gyallowar rana. Sa'a ce ta fara fitowa tana mata sannu, sai ga Tinene ta fito itama tana mika da hamma dan sai yanzu zatai sallar asuba. Can sai ga baba ya shigo gidan, da alama tunda ya fita salla masallaci bai shigoba sai yanzun. 

     Dukawa sukai har ƙasa ita da Sa'a suna gaishesa. Ya amsa idanunsa aka Zinneerah da ya kwana da damuwarta a cikin ransa. Murya ƙasa-ƙada dan kar Inna taji yace, “Zinneerah yaya jikin naki?”.

      “Da sauƙi Baba”. Ta amsa kanta a ƙasa. 

    Kafin ya ƙara cewa wani abu Inna ta fito wuff. Da sauri yabar wajen saboda wani shegen kallo mai kama da harara data watso masa. Taja tsaki tana duban Zinneerah dake durƙushe har yanzu.

        “Ki tashi ki ɗebo mani ruwan rahi dan randunan gidanga duk babu ruwa. Kuma na rahin yamma nakeso dan ruwansa yahi garɗi da haske”.

     “To inna. Ina kwana?”.

A takaice ta amsa mata tana karasowa wajen murhun inda wutar da Zinneerah ta haɗa ta kama sosai.

      Fuskar Sa'a babu walwala tace, “Inna dakin barta sai anjima rana ta ƙara dagawa sama, kinga akwai sanyi garin sosai”.

         “To uwata, yanda kikace ai haka zanyi”. Inna ta faɗa a hasale..  

     Shiru Sa'a tayi, dan tasan gatse Inna tai mata.

     Zinneerah dama bata tsayaba, tuni ta ɗauki botikin fenti da hijjab ta nufi ƙofar fita cike da dauriya. Hakan ba sabon abu bane a gareta, shiyyasa fita ɗibar ruwan a yanzu bai dametaba. Kawai yanda takejin jikinta babu daɗine matsalarta. Amma haka ta nausa kanta hanyar jeji domin ɗebo ruwa. Harta isa babban rafinsu da su kansu basusan iyakar inda ya tsayaba bata haɗu dako kare ba. Ta ajiye botikin a gaban rijiyar da aka gina a tsakkiyar yashi wadda bawani zurfine da itaba. Hasalima a gabanta ake duƙawa asa kwano a kwarfo ruwan dake kwance. Bismillah ta ambata tana saka kwanon cikin ruwan, sai da ta kwashe na ciki tas ta watsar waje sannan ta jira ya sake taruwa ta diba a botikin nata. Bayan ta cikashi taf ta miƙe da ƙyar ta ɗora bisa kanta.


         Koda tai sallama Sa'a ce kawai dake wankin baki da gawayi ta amsa mata. Inna ko dake bakin murhu tana yanka tuwon dare daya rage tana jefawa a ruwan data saka a wuta ko kallonta bataiba. Hakama Tinene dake gefen Innar tana shan koko. 

      Sai da ta wanke duk randunan gidan guda huɗu sannan ta juye ruwan ta Sake komawa. Haka ta dinga kai kawo tsakanin gida da rafi ɗibar ruwa. Tun bata haɗuwa da kowa har mutane suka fara fitowa. harma da irinta masu zuwa sakkon ɗibar ruwan na rafi. Duk wanda ta haɗu dashi gaisuwar mutunci ce tsakaninsu. Har ALLAH yasa ta kammala gaba ɗaya.

        Zuwa yanzu Inna ce kawai a gidan, Baba ya fice wajen sana'arsa. Sa'a da Tinene kuwa sun ɗauki tallar gyaɗa da Riɗi da itama tasan tata tallan na jiranta ne.

     Sai da ta gama ɗauraye ƙafafunta da sukai futu-futu da ƙura tazo inda Inna ke tankaɗen garin ɗan-wakenta. 

     “Inna na gama ɗibar ruwan”.

Yanda tai maganar murya na rawa yasa Innar kallonta. Duk da yanayinta ya nuna bata jin daɗi hakan baisa Inna tambayarta ba. Sai ma sake tsuke fuska tayi da faɗin, “Zauna inason magana dake”.

     Babu musu Zinneerah ta zauna duk da ranta fal tsoro.

         Ƙare haɗe fuska Inna tai tana dubanta da ƙyau. A tsawace tace, “Miya maidoki garinga?”.

       Sosai gaban Zinneerah ya ƙara tsananta faɗuwa. Murya na rawa tace, “Inna sune suka koroni. Sunce basa buƙatar baƙauya irina. Kuma saida suka shinhiɗa mani uban bugu da aibantani kahin su bani jikka biyu da rabi su sani a mota....”

      “Munahika, halan wata tsiyar kika ƙulla masu acan? Saboda kina buƙulu da abunda zan samu na hassahi daga kuɗin aikin naki?”.

      “Wlhy Inna ba haka bane. Matar gidance bata sona dai na rantse”.

       “Ruhwa mani baki dan bantan ubanki. Ai hajji Lanti zatazo ne, zanji gaskiyar zance a gareta. Wa billahillazi naji saɓanin abinda kika hiɗi yanzu ina halakaki na halaka banza wohi babu mai sanin yanda akai. Ƴar banza, kinhi son mu zanna ga ƙugunki ga nawa a gida. Sabidda kina kishi dani tunda uwarki bata gida? To mu zanna ga hili ga mai doki ai. Dan uban mutum yayi idan yana iyawa dani ko. Tashi ɓacemin a ido kahin naita tsinarki har se zaman Danya ya gagari ubanki ma bake kaɗai ba”.

       Mikewa Zinneerah tai tana shartar hawaye. Duk da cin zarafi ga inna ba yaune farauba a gareta. Sai na yau ɗin yay mata zafi ainun. Karon farko taji tana kwaɗayin son sanin inda mahaifiyarta ke rayuwa a yanzu.

    Ɗakin kwanansu ta shige, ta faɗa akan yamusashshiyar katifar da Yaya Sa'a da Tinene ke kwana. Dan ita bisa tabarmar karauni take kwana kamar yanda Inna take buƙata. Dauɗaɗɗun kayan dake gefe ta jawo ta shiga rufawa a jikinta saboda sanyi da takeji.

     Sosau ta ringa rawar sanyi tana sambatun zazzaɓi. Har tsahon lokaci babu wanda ya shigo ɗakin. ba kuma ta ƙarajin motsin Inna ba. A haka barci yay gaba da ita mai nauyi.


      “Zinni!! Zinni!!. Wai dan buhun ubanki baki jina inata kware baki?”.

     A firgice ta tashi zaune jin irin kiran da Inna ke ƙwalla mata tamkar ana yaƙi. Ta amsa a kasalance tana ƙoƙari janye kayan data nausama kanta gefe dan ta samu damar mikewa.

       Fitowar tata yay dai-dai da shigowar Yaya Gajeje gidan da sallama. Inna ta sake tsuke fuska tana kallonta. sai kuma ta ɗauke kai ta maida ga Zinneerah dake fitowa tana rawar sanyi da yamutse fuska alamar bata da lafiya.

      “Oh sannu ƴar gata! Ina nan tsaye ke kina can kina jan nashari a ɗaki? To kizo ki haɗa mani wutar ɗan wake kar rana tayi..”

      Da sauri Yaya Gajeje tai saurin tare numfashin Inna, “Haba Inna, wane haɗa wutar ɗanwake kuma kike magana haka? Diba kiga yanda take rawar ɗari da alama bata da lahiya”.

       “Mtsoww!!” Inna taja tsaki. Kafin ta cigaba da magana a hasale. “To ina ruwana da ciwon nata. A yanzu ma wagga duniya waye ke da lahiyar. Gajeje ki hita idanuna, karki kaini maƙurar randa zan maki bankaɗa wallahi”.

      Murmushi Gajeje tai tana kaiwa zaune. Cikin kwantar da murya tace, “To inna idanma kin mani bankaɗa ai kin isane tunda kece kika haiheni. Ni dai kin sanni ban ganin gaskiya na riheta ai. Amma dai kiyi haƙuri ni bara na haɗa miki wutar tunda ita batajin daɗi. Harma sakin danwaken yau nice zan miki Innarmu kwantar da hankalinki”.

    Baki taɗan taɓe. sai dai batace komaiba. Hakan yasa Gajeje fahimtar taci nasara. Tai murmushi da tura hannu a zaninta ta ciro leda dake a lalitarta ta bujen ciki. Goro ne da alawa da biscuits guda biyu ƴan goma-goma. “Innarmu ga kayan suna”. Tai maganar tana miƙa mata.

      Ɗan sakin fuskarta tayi da miƙa hannu ta amsa. “Yo kuma ƙya bani duka. Su su Rabi'u fa?”.

      “Karki damu na ba Salame ta kai musu nasu suma. Wannan nakine. Nima Agali ya bani shi bayan mun hito”.

      “To, to maddala. Ni bamma sami leƙawaba yau na tashi da ƴar mashashshara ne. Sai zuwa anjima zanje nai masu an raɗa suna. Miye sunan ɗiyar ne?”.

       “Ai Hadiza aka samu, sunan Innar Bilkin aka saka”.

     “Tofa ɗigifi. Shi yanzu duk yawan gidansu ya rasa wazai saka sai sunan uwar matarsa?”.

      Ƴar dariya Gajeje tayi tana yafito Zinneerah dake tsaye rakuɓe jikin bango da hannu. “Inna kenan, ashe babu daɗi Lawal ya sakama Ummita sunanki shima”.

     Shiru tai bata tankaba. Dan an ƙure tsoguminta kenan.

    Zinneerah ta zauna tana gaida Gajeje. Cike da kulawa ta amsa mata da kai hannu a jikinta. Jin uban zafin ya sata ambaton, “Ya subahana. Zinni ai masassara ce a jikinki sosai. Kin karya dai ko?”.

      Ƙasa Zinneerah tai da kanta tana haɗiye hawayen dake neman zubo mata. Dan harga ALLAH yunwarma tanajinta mai tsananima kuwa. Saboda Inna batai mata tayin abinciba yasa ta haƙura.

     Shirunta yasa Yaya Gajeje fahimtar bataciba ɗin. Tasan za'a rina. Dan innarsu lamarinta sai du'ai. Bata sake cewa komaiba kamar yanda itama Innar bata tanka musu ba. ta dai miƙe zuwa gindin murhun inda tukunya ke aje saman duwatsun murhun. Tuwone a ciki na dawa da aka yanka aka ɗumama. Duk ma ya zama gutsatstsari alamar masu gidan sunci. Yaya Gajeje da ranta ke mata ƙuna ta ɗauka kwano ta zubama Zinneerah, tare da koriyar miyar kukar dake gefe. Har gabanta takai ta dire tana fadin, “Maza ci na samu mai sayo miki magani nan gidan Rahine idan bata fita tallar kayan koli ba”.

      Jan kwanon Zinneerah tayi gabanta, babu musu ta hau ci dan yunwa takeji sosai..

     Inna dai bata sake tankawaba har Zinneerah ta gama cin tuwon nan. Yayinda Yaya Gajeje ta koma can wajen murhu tana haɗama Inna wutar ɗanwake da ƙoƙarin saka ƙatuwar tukunyar da take amfani da shi.      


            Kasancewar Yaya Gajeje a gidan yau sai ta samu ƴar salama. Dan har Baba daya shigo shima ya ɗan samu sakewar bata kulawa, harda siya mata awara. 

     Washe gari kam Inna bata saurareta ba. Duk da ta fahimci har yanzun bata da lafiya, dan ba'a ƙulla awa biyu Zinneerah bata raɓe gefe tana riƙe cika ba alamar dai cikin na mata ciwo. 

      Sai dai tsabar rashin tausayi ko'a fuska Inna bata nuna ta fahimtaba, daga ƙarshema tallar riɗi da gyaɗa ta sakata ɗauka. Da Sa'a tayi magana kuwa ta hayayyaƙo mata da masifa kamar zata daketa. Dole tai shiru tana maijin babu daɗi da halin mahaifiyar tasu.


★★★


            Yau satin Zinneerah ɗaya kenan da dawowa da ga Katsina. Tun Inna na zuba idon ganin Hajji Lanti ta biyo bayan Zinneerah harta fara sarewa. Dan har ranta ta ɗauki alwashin sai Zinneerah ta koma, bazata taɓa yarda kuɗin data ƙwallafa ran samu su wuceta a banza ba.

       A ɓangaren Zinneerah kam a kwanakin nan daka kalleta kasan bata da lafiya. Musamman yanda ta wani rame sosai. Gashi sam bata da kuzari a jikinta. Yanda ta saba aiki ada da kazar-kazar yanzu sam bata iya hakan. Komai zakaga tana yinsane da sanyin jiki kamar mara ƙashi. Inna tayi masifar harta gaji ta barta, sai dai zagi da tsina ne tana shansa, dan ranar har marinta tayi.

       Yau ma kamar kullum tana gama ɗibar ruwa da dukkan aikinta na gidan tai shirin ɗaukar tallar riɗi da gyaɗa. Tinene kaɗai ta samu a tsakar gida tana suyar wainar fulawa. Inna kuwa ta fice barka wai. 

      Ɗakin Inna ta shiga ta ɗakko ƙaton farin botikin da aka cika da gyaɗa da riɗi, ta sake fitowa tsakar gidan. Cike da sanyin murya tace, “Tinene idan Inna ta dawo ki hiɗi mata na wuce”.

      Kallon banza Tinene tai mata ta ɗauke kanta. Cike da rashin mutunci tace, “Inma wannan allagiran kike mawa kima cire rai yarinya, dan aradu baki cin ko ranyo anan”.

     Murmushi Zinneerah tayi kawai ta fice, dan tasan inhar ta biyema Tinene zama su iya faɗa, itako bata da wannan ƙarfin yanzu kam.

         Dai-dai fitowarta ƙofar gidan nasu gabanta ya faɗi. Tai ƙasa da kanta saboda cin karo da fiska mafi daraja a zuciyarta bayan ta iyayenta. Ba kowa bane face saurayinta Babawo wanda a yanzu ya maida akalar neman auren nasa kan yayarta Karima da yaya Sa'a ke bimawa. Babawo ya sota tun bata san kantaba. Da farko matsin rayuwar data tsinci kanta a hannun Inna dalilin rashin mahaifiyarta a gidansu Babawo yake tausaya mata. Shine silar cigaba da karatunta bayan gama firamare , shine ya tsaya tsayin daka harta shiga makarantar gaba da firamare (Secondary), tana aji ɗaya wani kawunsa ya zo ya tafi da shi kaduna. Bai dawo ba sai da ya shekara. Kamar yanda ta ɗokantu da zuwansa haka shima ya ɗokantu da ganinta. Yazo mata da tarin tsaraba, tare da burin iyaye su shiga akan maganar aurensu, a cewarsa data kammala aji uku na sakandire zasuyi aure. zai wuce da ita can kaduna sai ta cigaba a gidansa har sai taga ƙarshen biro. Hakan yama Zinneerah daɗi a zuciya da ruhi, sai dai kuma a kwana biyu da zuwan Babawo labarin ya canja alƙibla. Dan kuwa bai komaba sai da tsuntsun soyayyarsa ya tashi daga kanta ya koma kan yayarta Karima yar wajen Inna ta uku. Ƙiri-ƙiri ta gaza gane kan Babawon ta, ya canja mata gaba ɗaya. Kosan ganinta bayayi. Taci kuka sosai, ta kuma shiga ruɗani, dan har ciwo tayi. Mutane sunta kace nace akan wannan al'amari, wasu na faɗin asiri Inna taima Babawo ɗin, wasu suce kuma shine dai yake ganin Karima ta fiye masa tunda ita babbar budurwace wadda akema surutu akan rashin samun miji. Dan Karima shekararta sha takwas da wasu watanni, a ƙauyen kuma sa'annin su Zinneerah sune dai-dai aure ƴan sha biyu. Amma sai dai ita ƴaƴan Inna dama sukanyi jinkirin samun miji a ƙauyen saboda mugun halinta, shiyyasa ma har yau babu wacce ta taɓa aure a nan cikin Danya. Gajeje na kauyen Sanni, Atine na can Rimaye. Sai yanzu ga Karima da Sa'a waɗanda duk sun zama manyan ƴammata. Karima nada sha takwas Sa'a na sha shida. Sai Tinene sa'ar Zinneerah itace auta.

         Bayan wucewar ruɗanin canjawar Babawo da shekara ɗaya da wasu wattani, dan har manya sun shiga maganarsa da Karima sai kuma Inna ta haɗata da hajji Lanti da tai sanadin kaita birnin Katsina da niyyar aikatau, inda ita kuma ta gudo ta dawo gida........

         “K! Wai baƙyaji ana miki magana”.

   Tsawar da Babawo ya daka matace ta dawo da ita daga dogon tunanin da ta tafi batare data farga ba. Saurin haɗiye hawayen da suke neman zubo mata tayi tana girgiza masa kanta.

         Ta ɗan risina kaɗan tana faɗin, “Kayi haƙuri Ya Babawo banji bane wlhy”.

      Tsaki yaja yana taɓe baki da jifanta da wani irin mummunan kallo na tsana, wanda a da idan wani yay kuskuren yimata irin wannan kallon sai inda ƙarfinsa ya ƙare. A gadarance yace, “Kiramin Karima nace”.

        Idonta ƙasa-ƙasa tana mai satar kallon yanda ya ƙara ƙyau da cikar zati tace, “Yaya Kareema bata nan, tana Rimaye wajen Yaya Atine, nima ban dawo na sameta ba”.

       Tsaki yaja yay gaba batare da ya sake tanka mataba. Ta bisa da kallo cike da tsananin so da ƙaunar da take masa har yanzun. yayinda ƙamshinsa daya bar mata take jinsa mafi daraja da tsada a cikin iskar da take shaƙa. Duk da ƙarancin shekarunta zuwa yanzu tasan minene soyayya, dan shine ya rene ta akan bigirenta, tun bata fahimta harta fara ganewa da banbancewa, sai gashi rana tsaka rabuwa tazo musu bisa tafarkin MAKAUNIYAR ƘADDARAR da batasan sila ko mafarinta ba, tunda har yanzu bazata iya faɗin dalilin rabuwar tasuba balle dalilin komawar Babawonta kan yayarta.

     Hannu tasa ta sharce hawayenta tana gyara riƙon botikin gyaɗa da riɗinta ta cigaba da tafiya ranta na mata zafi da ƙuna.............✍



*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_Typing📲_*




     *_😭MAKAUNIYAR ƘADDARA!!😭_*





                *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*




_ZAFAFA 5 NEXT LEVEL_



Page 4


...............Ƙarfe kusan biyu na rana Zinneerah ta dawo gidan a gajiye. Duk uban riɗi da gyadan data fita da shi kaɗanne ya rage a botikin. Tun a sallamar farko na shigowa gidan dukkanin ɗan guntun farin cikinta ya gushe. Ba komai ya kawo hakanba kuwa sai cin karo da Yaya Kareema datai, wadda ta dawo daga Rimaye wajen yayarsu ta biyu dake bima yaya Gajeje dan ita acan take aure.

        Zaune suke a ƙarƙashin bishiyar tsakar gidan nasu sun baje kaya ita da Sa'a da Tinene. Inna na daga bakin murhu tana talgen tuwon dare. Dariyarsu suke sha cike da nishaɗi dajin daɗi.

     Sa'a ce kawai ta amsa sallamar Zinneerah tare da mata sannu. Ta amsa a ɗarare tana duban Karima data haɗe girar sama data ƙasa. “Yaya Karima ashe kin dawo, sannu da zuwa, yaya kika baro su Yaya Atinen?”.

        “To uwar iya, halan kin aikenine da kike lissaho mani wannan tambayoyin? Kai wagga ɗiya hi'ilinki yayi yawa wallahi, k.......”

        “Haba Yaya Karima, minene laihinta anan kuma? Danta maki barka da dawowa da tambayar su Yaya Atine?”. Sa'a ta faɗa cikin katse ƴar uwar tata rai ɓace.

     A fusace itama karimar ta katseta da fadin, “To kema waya saki a ciki, ALLAH ina ci maki uwa yanzun nan Sa'a. Ita ɗin uwarki ce ko mi?”.

       “Ba uwata bace, amma ƴar uwatace kamar yanda take ƴar uwarku kema. Daga hiɗin gaskiya sai laihi. Ni banga abinda Zinni ta tarema wani a gidan nanba da kuke tsangwama mata, itama fa ɗiyace kamar yanda muke ɗiyan gidan. Duk da baba baya magana akan abinda ake mata na tabbatar yanajin ciwo a rans........”

          Timmm!! Kake jin saukar dundu a bayan Sa'a. Ta gyantsare saboda azabar zafi tana sosawa. Inna dake tsaye a kanta tana huci tace, “Kaɗanma nai miki dan ubanki. Wa kike hiɗima waɗanan maganar banzar to? Sheɗaniya munahika. Anya kuwa nice uwarki Sa'a? Kodai kema Hauwar ce ta haiheki taimin mucanje ban saniba?”.

         Baki cike da iska Sa'a tace, “Amma inna dan na hiɗi gaskiya sai kimin wannan uban ƙullin a baya?”.

       “Kaɗanma nai miki shegiya ƴal bura'uba bai baki kamar na reza, hita kibar gidan nan kona sauya miki wannan shegiyar huskar da maruka”.

      Fita Sa'a tai tana ƙunƙuni da cigaba da shafa bayanta inda yasha dundun.

     Sum-sum Zinneerah ta wuce ɗakin Inna zata kai botikin tallar tata Karima ta daka mata tsawa. “Munahika dawo a lissahwa sannan”.

       Dawowa Zinneerah tayi jikinta na rawa ta  mikama Karima kuɗin da botikin. Fisgar botikin Tinene tayi, Karima kuma kuɗin ta ƙwata tana buge mata hannu.

      “Innarmu na nawa kika aza mata?”.

    Karima ta faɗa tana fara irga kuɗin.

           Daga inda Inna take ta bata amsa da, “Na jikka sha huɗu ne cir gaba daya, dan na rantse da ALLAH kona hicika ya ɓata ina miki ɓatanci da shegen bugu a gidan nan. Kuma sai ubanki ya biyani kuɗina babu ɗagin ƙahwa”.

     Zinneerah dai batace komaiba. Sai su Tinene ne suka kwashe da dariya. Karima ta gama irga kuɗin tana jijjigasu da faɗin, “ALLAH ya sota Inna sun cika. Kuɗin anan jikka goma sha ɗaya da murtala uku, sai kayan daya rage na jikka uku ba murtala uku”.

      “Ta taimaki kanta. Ga tuwo can kije ki ci idan kina so, dan nasan dai abokan iskancinki sun gama cika maki ciki da shinkahwar tasha”.

      “To” kawai Zinneerah ta ce ta nufi hanyar ɗakinsu. Dan wani irin jiri takeji yana neman kwasarta. Tana shiga ɗakinsu ta zube a katifar su Tinene tana sauke numfashi. A hankali barci ya fara rinjayar idanunta mai daɗi. 

       “Baƙo na sallama da Zinneerah a waje”.

     Ta tsinkayo muryar yaro sama-sama da ga tsakar gida. Tsawar da inna ta dakama yaron ce ta sakata buɗe idanunta gaba ɗaya babu shiri. Sai kuma ta jiyo Sa'a na faɗin,

         “Inna bafa wani bane ba, malam badamasi ne malaminsu”.

     Tsaki Inna taja batare data tankaba. Yayinda Sa'a ta ɗaga labulen ɗakin tana kiran sunanta. “Zinni ki tashi ga Malam Bade yazo nemanki”.

      Yinƙurawa tai ta tashi zaune tana gyara hijjab ɗin jikinta. Cikin sanyinta dana barcin data fara tace, “To Yaya Sa'a”. Daga haka ta miƙe ta fiti cike da dauriya.

    

        Matashin saurayine, dan gaba ɗaya shekarun nasa bazasu wuce talatin da ɗoriya ba. Zinneerah data fito a ɗarare saboda tsoron Inna ta rissina tana murmushi. “Sannu da zuwa malam. Ina yini?”.

     Shima tashi fuskar faɗaɗe da murmushi ya amsa yana kallonta. “Zinneerah Sulaiman ashe kin dawo gida babu labari? Sai ɗazu ina bisa mashin na hangeki da botikin gyaɗa da riɗi a bakin yara”.

      Har yanzu tana a duƙe kai a ƙasa tana murmushi, cikin ƴar muryarta tace, “Na dawo Malam, dama naje wajen mamana ne gaisheta”.

       Yanzu kam da mamaki yake dubanta. Cikin kasa haɗiye abinda ke a ransa yace, “Amma a gari aketa hiɗin guduwa kikai bama asan ina kika nuhwaba? Kai mutane sai dai a barsu da halinsu. ALLAH ya ƙyauta to, kin baro maman naki lahiya ko?”.

       “Lahiya lau suke Malam”.

“To Alhmdllh, Yanzu ni bama wannan ba, nazone dama akan jarabawarku ta jsce. Ina hwata dai baki manta nanda kwanaki takwas zaku hwara ba ko?”.

      Karan farko ta ɗago taɗan kallesa ta sake maida kanta ƙasa. Kafin tace wani abu Inna ta banko ƙyauran langa-langar ƙofar gidan nasu ta fito.

            “Uhyimm! Kaji farkar taka ta dawo kazo kenan? To billahillazi bari kaji yanzu bazan ɗauki wannan sheɗancinba. Kaji da ƙyau karna sake ganinka ƙohwar gidan nan. Idan son ganinta kake ta bika can mahaɗar taku man......”

      “K dalla malama saurara, tsohuwar banza da bakinta bai hiɗin alkairi sai sheri wa ɗiyan mutane. Na rantse da ALLAH kika ƙara hiɗin wani kalmar ɓatanci garemu yau sai kin kwana ofishin ƴan sanda. Ni nazo ne akan maganar jarabawa da zasu yi ta koma makaranta....”

        “Anƙi ta koma ɗin munahiki algungumi. Dama can niya nai na barta take zuwa. da ga yau da ga yanzu kuma na hwasa. Bata sake zuwa talla zataimani”.

      “Ashe kuwa zaki gurfana gaban mai-gari......”

       “Kaini gaban sarkin katsina ma ƙarewar mai-gari mana. Ke kuma munahika dan ubanki tashi ki shige ciki, ƴal bura'uban yarinya kulin bata iya komaiba sai janyoma mutane jidali da yaye-yaye a ƙwar gida. Zanyi maganin rawar kanki ne ai...”

       Yanda ta kaima Zinneerah duka ya sata miƙewa da gudu ta shige gidan. Shima Malam Badamasi bai sake tanka mataba ya bar ƙofar gidan rai ɓace. Inna kuwa masifa ta cigaba da zazzagawa har sai da Sa'a da Karima suka fito suka shiga da ita gida.

     Tana shiga ta hau dukan Zinneerah babu ji babu gani. Sai da tai mata lilis ta barta kwance tana numfashi da ƙyar. Zinneerah akwai taurin zuciyar tsiya da kafiya wani lokacin. Duk wahalar da take sha wajen Inna akan jima ba'aga kukanta ba idan ba ita taso ba. Idan kuwa kaga ta cika yawan kuka to lallai abin ya kai babba gareta sosai.


      Inna na tsaka da cigaba da jarabarta aka buga sallama. Sa'a ce ta amsa tare da nufar zauren gidan nasu dan taga wanene. (Sanƙira) mai shela idan abu ya faru a garinne tsaye yana baza babbar riga. Ta rissina tana gaidashi dan dattijo ne sosai, amma Baba zai iya girmarsa. 

     “Tsohuwar taki na nan ko?”.

“Eh baba tana nan”.

“To maza sanar mata mai-gari na biɗar ganinta. inko bata zuwa cikin salama ƴan doka zasuzo su kaita da kansu. Tazo tare da ƴar uwarki zinneerah”.

      Sosai gaban Sa'a ya faɗi, amma ta daure cikin girmamawa ta amsa masa tare da juyawa cikin gidan. 

       Inna ta dubi Sa'a cikin haushin Zinneerah da bai gama sakintaba tace, “Ke kuma minene kika shigo ma mutane haka? Halan shegen nanne bai tahi ba?”.

     Kan Sa'a a ƙasa tace, “A'a Inna. Baba Lado sanƙira ne fa, wai ana kiranki gidan mai-gari ke da Zinni....”

       “Ki koma ki hiɗi masa ba'a zuwa. Ba'a kamar ana zuwa ɗin...”

    “Inna wlhy cayay fa idan baki zuwa ƴan sanda zasuzo su tahi da ke”.

       Shiru Innar tayi ƙirjinta na bugawa. Ta tsani harkar ƴan sanda, dan tun sanda sukai faɗa da Lamunde aka adashi ta kaita kusada ofishin ƴan sanda akazo har gida aka kamata sai da tai kwana biyu a kusada hannunsu take shakkarsu. Ba ƙaramin wuya taciyo a kwana biyun datai wajensu ba. Amma a fili sai ta ƙyaɓe baki zata fara masifa kuma.......

       “Shin wai Asabe saƙon mai-gari bai iso gareki bane?”.

    Karaɗin Sanƙira daga ƙofar gida ya katse mata masifar datai nufin farawa. A tsorace Karima tace, “Innarmu dan ALLAH kije, tunda kinga harda ita akace kuje. Kinsanfa mai-garin nan ba mutuncine da shi ba wlhy yana iya kira maki ƴan dokar”.

      Kamar zatai magana sai kuma ta fasa. Ta kai dubanta ga Zinneerah dake kwance barci ya fara ɗaukarta. Tsawa ta daka mata wadda ta sakata tashi a firgice babu shiri.


      Ran Inna fal masifa ta tasa Zinneerah gaba Sanƙira na biye dasu suka tafi gidan mai-gari. Acan suka iske malam badamasi. Tun daga nesa Inna ta dinga antaya masa uwar harara kai kace idonta zasu zubo ƙasa ne. Shiko baima san tanaiba. Dan hankalinsa dana mai-garin da fadawa duk yana kan Zinneerah ne dake ɗingishi.

       “Ranka ya daɗe ka ga abinda nake hidi maka ko! Da alama bayan barowata gidan bugunta tai”.

      Ran mai-gari a ɓace ya wurgawa Inna mugun kallo. “Ke dai Asabe baki gamawa da duniya lahiya inhar baki canja halinki. Ace mutum shi dai baisan komaiba sai mugunta, ke shikenan zicciyarki tamkar ta kahiran hwarkon ƙarni! Kai ALLAH ya wadaran halinki wlhy Asabe. shi dai malam Sule bai sa'ar mace irinki ba. Ya auri ta arziƙin kin koreta a gidan kina kuma gallazama abunda ta haihwa. Wlhy ina mai tabbatar maki wata rana sai kinyi nadama, dan wanga ɗiya sai ta zame miki ɗan hakkin faka raina, RAINA KAMA kuma mara mutuncin mata”.

        Kan Inna a ƙasa tanata faman kumurya da kumatu babu damar magana, sai da mai-gari ya ƙare mata zagi tas da gorin asalinta kafin ya ɗora da gargaɗi.

      “To naji kince baki sake barin yarinyar nan taje makaranta. Kece kika sata ne?”.

     Kan Inna a ƙasa har yanzu tace, “ALLAH shi sawwaƙa ranka ya daɗe. Niko miya ja mani kai ɗiyana boko. Ubana bai saniba bani kai ɗiyana su tabaɗe. Can abokan cin mushenta ne suka kaita......”

        “E, ai shi abokin cin mushen nata da kike magana shine kika asirce ya koma kan ɗiyanki, kinga ashe kema abikiyar cin mushen tashi ce ko?”.

     Malam badamasi ya faɗa a harzuƙe cikin katse Inna. Babu wanda ya dakatar da shi, dan kowa yasan Babawo take nufi, tunda shine yay tsaye tsayin daka har Zinneerah ta shiga makaranta saboda tana so. Amma yaran gidansu daga firamari basa cigaba. Sa'a ce ma taɗan fara sakandire ɗin itama zango ɗaya tayi ta gudo saboda wani malami ya daketa Inna taje tai masa tijara tace Sa'ar bata sake zuwa. Daga nan kuma bata sake zuwan ba.

       Mai-gari ya cigaba da faɗin, “To bara na gaya miki a gaban kowa ki riƙe a ranki yarinyarnan zata cigaba da karatunta har sai ta gama. Ni nan mai-gari zan ɗauki nauyin ɗawainiyar karatun natama daga yau, tunda ance dama yaron daya kaita ya janye dama daga yi saboda sherin da kikayo ta ƙarƙashin ƙasa. Wlhy kinji na rantse, dai-dai da rana ɗaya yarinyarnan kika hanata zuwa makaranta sai kin kwana a kusada ofishin ƴan sanda. Kowa dake nan ya shaida”.

       A take duk suka amsa masa da cewar sun shaida. Banda Inna dakeji tamkar zata haɗiye zuciyarta ta mace. Zinneerah kam a ranta wani irin daɗi ne ya lulluɓeta. 

        Sai da mai-gari ya ƙarama Inna dogon gargaɗi sannan ya sallameta banda Zinneerah.  

      Bayan wucewar Inna Mai-gari ya shiga yima Zinneerah tambayoyi tana bashi amsa kanta a ƙasa. Sosai tausayinta ya sake mamayesu, suka shiga mata nasiha akan muhimmancin haƙuri da ribar da mai yinsa kanci a duniya ko a lahira. Sannan ya damƙa amanarta hannun malam Badamasi. Tare da tabbatar masa duk abinda za'a buƙata na ɓangaren makaranta na Zinneerah yazo gunsa ya amsa. Daga haka aka sallamesu bayan mai garin ya bata ƙyauta jikka biyu da rabi (500).

       Godiya tai musu sosai cike da girmamawa itama, tare da addu'oin fatan alkairi sannan suka taso ita da malam badamasi daya rakota har gida yana ƙara mata nasiha.


      Koda Zinneerah ta dawo gida tayi tunanin inna zata hukuntata akan abinda ya faru a gidan mai-gari. Amma sai taji shiru batace da ita ƙala ba. sai dai tana ɗaure mata fuska fiye da yanda ta saba. Sannan komai ƙanƙantar aiki ita ake kira tayi koda su Sa'a na zaune a kusa da ita.


★★''★★"★★"★★


           Akwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI, haka rayuwa ta cigaba da shuɗawa. Yau fari gobe tsumma a gidan su Zinneerah. Ita dai batasan minene farin ciki ba ko jin daɗi a gidansu. 

       Tun randa sukaje gidan mai-gari da inna sai ta sake ninka gallazawar da take mata fiye da da. Makaranta dai ta barta tana cigaba da zuwa. Amma kafin ta wuce ƙa'ida saita kammala ayyukanta. Idan kuma ta dawo ta iske wasu na jiranta him. Ga tallar riɗi da gyaɗa babu fashi gareta. Tsangwama wajen Karima da Tinene sai abinda yay gaba. Idan kaga taji daɗi sai wajen Sa'a da Yaya Gajeje idan tazo gidan. Shi dama Baba ba'a sakashi a lissafi. Dan tamkar bashi da wanima amfani a gidan. Idanma baiso ba sai ya yini a gona tun safe sai yamma zai dawo. Duk abinda Inna zatai a gidan ƙala bai iya cewa saboda tsoron da yake mata.


       A haka su Zinneerah suka fara jarabawar junior waec ɗinsu. Zinneerah ba wani ƙoƙari ne da ita sosai ba. Sai dai tanada naci akan abu sosai. Duk abinda takeso takan dage a kansa domin ganin ta cimma nasara. Hakan yasa sam bata da wasa, musamman ma daya kasance itaɗin miskilace ta gaske. Ga halin gidansu ya sake maidata shiru-shiru da rashin son sakewa da mutane.

     Zuwa yanzu ta daina jin ciwon cikin nan da kasala. Sai wani irin ƙiba take mai ban mamaki da haske. Ɗan matashin ƙirjinta na ƙara fitowa fili sosai fiye da da. 

      Kowa ya ganta sai ya tanka canjawar tata na ƙanƙanin lokaci, dan abun na bama mutane mamaki sosai. Musamman da aka san bawani daɗi takeji a gidan nasu ba. Ita kanta Innar bata gajiya da kallon Zinneerah ɗin a ƴan kwanakin nan. Sai dai tanayi tana jan tsaki da ƙyaɓe fuska.


            A yau ma data kasance juma'a bayan tasowarta makaranta gida tayo. dan jarabawa ɗaya kacal sukayi, wadda daga ita sai ta ƙarshe da zasu zana. Cike ta iske gidan nasu da ƴan kawo lefen yaya Karima, wanda aka kawo da ga gidan su Babawonta. akwatina uku zuƙa-zuƙa ƴan yayine. Itace kuma budurwar farko da akaima akwati uku a garin, dan ɗaya sukeyi kacal su haɗa rio irin na saka kayan yara ɗin nan babba. Wasuma basayin Rio ɗin. Amma sai ga Babawo shi yayi har uku, ga kaya fal.

           Sosai hankalin Zinneerah ya tashi, dan zuwa yanzu dai ta tabbatar Babawo kam ya barta har abada. Sum-sum ta lallaɓa ta shige ɗakinsu tunda babu wanda ya ganta hankalinsu nakan ganin kayan. Hijjab kawai ta cire ta zauna tana haɗiyar zuciya da ƙoƙarin ganin hawayenta basu zuba ba. Tsawon lokaci tana zaune hayaniyar mata da yara na daɗa ƙaruwa harda guɗe-guɗe. Ganin abin nasu bana ƙare bane ta zame ta kwanta hawayen da taketa ƙoƙarin dannewa suka shiga silalowa a kumatunta. Daga haka ta lula duniyar tunani mai zurfi har barci yay gaba da ita bata farga ba.


       Timmmm!!!

Kakejin ƙarar saukar dundu. A firgice Zinneerah ta farka tana sosa gadon bayanta inda Karima ta daketa.

       “Munahika ƴar buƙulu. Ashe nan kikazo kika ɓuya kina baƙin ciki da abun hwarin cikin daya sameni ko? To bara ki ji sai dai ki mutu wlhy. Ni Karima kamar na zama matar Babawo na gama. Dan nan da sati biyu za'a ɗaura mana aure ma”. Ta ƙare maganar da ƙyalƙyalewa da dariyar rashin mutunci.

     Ita dai Zinneerah ko ɗaga kai ta kalleta batayiba. Ta kuma ƙi yarda tai kuka. Dan dama wani lokacin haka take da shegen taurin zuciya. Musamman akan abinda ta tabbatar da natane akai mata fin ƙarfi. Haka Karima ta cigaba da mata tujara har sai da Yaya Gajeje da bata tafi ba ta shigo tana zaginta sannan tabar Zinneerah.

             Karan farko da baba ya nuna tsananin ɓacin ransa akan abinda akema Zinneerah har takaisa da yima Karima faɗa. Dan duk abinda tayi ya farune a kunnensa kasancewar ya shigo gidan.

      Babu wanda ya iya magana har Inna. Dan ita kanta yau sai taji wani shakkar Baban a cikin ranta. Dama ance mai haƙuri bai iya faɗa ba.

      Ɗan Murmushi Zinneerah dake a ɗaki zaune har yanzu tayi. A ranta kuwa tana mai tsananin jin tausayin mahaifin nasu da ta tabbatar anfi ƙarfinsa ne dama game da al'amarin gidan nasa, bawai dan Inna ta gagaresa bane ba.


★★★


         Tun daga wannan rana su Inna suka hau shirin biki. Dama can a shirye suke tsaf dan sun daɗe suna jiran wannan ranar dan dai kawai Babawon nata musu yawo da hankaline kamar ma zai suɓuce. Sai kuma gashi cikin lokaci ƙanƙani hankalin nasa ya sake dawowa ga Karimar a bazata.............✍

       

        

    

  

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_Typing📲_*




     *_😭MAKAUNIYAR ƘADDARA!!😭_*





                *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*




*_HAPPY HAUSA DAY!!🎈🎉🎊🪄_*

         _Inama ɗaukacin al'ummar HAUSAWA na duniya baki ɗaya murnar zagayowar wannan rana ta HAUSA ta duniya. Alkairin ALLAH yakai gareku a duk inda kuke, ALLAH ya ƙara ɗaga darajar HAUSA da ɗaukacin HAUSAWA baki ɗaya. Harma da sauran yarukanmu🥰🥰_🤗




*Page 5*


..........Lallai da gaske shirin biki ake na ƴar gata. Dan bama Inna kawai ba hatta da Atine dake aure Rimaye ta shiryama bikin. Ko kayan ɗakin Karima daga can akayosu. Ita dai Yaya Gajeje bata biye musu. Sai ma nuna musu illar ƙulla wannan aure takeyi. Dan ta tabbatar an cuci Zinneerah. Tun abin bai kai hakaba take ma Inna magana amma bata saurarenta. Sai ɓacin rai dake biyo baya a tsakaninsu akan hakan. Zuwa yanzu kuma data tabbatar sunyi nisa saita zuba musu ido. Dan akwai ranar ƙin dillanci ai. Kuma nasihar baba ta shigeta. Dan shima da kansa yace ta barsu karta sake cewa komai akan auren. Inhar an cutama Zinneerah ne akan hakan ALLAH na nan baya barci.

         Tun ra da aka kawo lefe lafiya taima Zinneerah ƙaranci, a haka ta daure take komai na rayuwarta data saba. Harma ta ida zana jarabawarta ɗaya data rage ranar litinin. Sun kammala junior secondary school kenan suna jiran result kuma ya fito aga abinda ALLAH zaiyi.

         Biki kam dai shiryashi ake sosai kamar yaune aka fara aurar da ƴa a gidan. Ita dai Zinneerah nata ido ne kawai, sai idan ta keɓe ne takan sha kukan zuci. A randa aka saka Karima a lalle jikinta yay tsanani, har takaita da kaiwa kwance dole.

      Cike da damuwa Yaya Gajeje ta takura mata taci alala da suka girka a gidan saboda baƙi da sukazo daga marabar musawa dangin Inna. Da ƙyar Zinneerah ta iya cinye guda ɗaya sai amai. Kowa ya tausaya mata anata mata sannu. Harma wata ƙanwar Inna na cewa shawara ce a nemamata sassaƙe tasha. Itadai bata iya magana sai amsawa da kai harta samu ta koma ɗaki ta kwanta.

     Cikin tsoffin da sukazo daga maraba ne ɗaya ta dubi Yaya Atine dake gefenta tana shayar da ƴarta da take goyo. “Niko nace Atine”.

      “Na'am Gwaggo ladi”. Yaya Atine ta amsa tana kallonta tana maido hankalinta gareta. Wadda aka kira da Gwaggo Ladi tace, “Wanan ƴar uwar taku tayi aure ne dama bamu da labari?”.

      Da mamaki a fuskar Yaya Atine tace, “Gwaggo wai kina nufin Zinneerah? Indai itace batai aureba. Yaya zatai aure baku jiba”.

     Cikin waro idanu na alamar gulma tace, “Kanjakar ubancan kayyasa. To lallai idon Asabe a rufe yake a gidan nan bata bahimtar komai daɗa”.

      “Gwaggo miyasa kika hiɗi haka”. Yaya Atine ta sake faɗa tana duban Gwaggon nasu da ƙyau.

     “Uhm-uhm babu komai Atine. Kawai dai naga abinda yafi ƙarhin ganina ne. Dan wannan ɗiyar ciki ke ga jikinta, harma ya tasa gashi nan”.

      A razane Atine ta saki ƴarta ƙasa da dukan ƙirjinta tace, “Gwaggo ciki?!! Zinni ɗince ke da ciki!!?”.

     Yanda tai maganarne ya jawo hankalin sauran mutanen dake a gidan kansu. Ga ƴarta data saki ƙasa ta tsage da kuka saboda zafin faɗuwar da taji..

            Yaya Gajeje ma a ruɗe ta saki kwanon data ɗakko zata saka a sayoma Zinneerah kunu ko zata iya sha. Ta ƙaraso gasu Atine da sassarfa tana faɗin, “Atine wannan wane irin mugun alkaba'ine kike hiɗi dan ALLAH?”.

        Da sauri Atine tace, “A'a yaya Gajeje bafa ni na hiɗi ba....”

     “To waya hiɗi?”.

Gajeje ta katse ƴar uwar tata.

         “Kunga bafa zancen hayaniya bane ba Gajeje. Ku kira yarinyar tazo nan”. Gwaggo Ladi duk ta katsesu.


       Zinneerah na ɗaki kwance tana sauke numfashin wahalar amai da tayi wata cikin ƴan bikin ta shigo ɗakin tana ƙwala mata kira. Miƙewa tai daga kwancen da take a razane tana dubanta batare data amsaba.

    Matar tace, “Kinga taso ana kiranki a waje”.

         Batare da tunanin komaiba Zinneerah ta miƙe ta biyo bayanta cike da dauriya. Tana fitowa gabanta ya faɗi ganin kowa na gidan ya zubo mata idanu, har waɗanda ke a cikin ɗakin Inna duk sun fito tsaye cirko-cirko. Rasa ina zata dosa tayi dan ruɗiya. Sai da yaya Gajeje tai ƙarfin halin kiran sunanta cike da tashin hankali. Dan ita kanta kam zuciyarta ta fara gaskata zancan tsohuwar saboda wani irin canjawar da Zinneerah tayi, wanda ada sam hankalinta bai taɓa bata abu makamancin ciki ba akan canjin....

     Ƙarasowar Zinneerah inda suke ne ya katse tunaninta. Tsohuwa Gwaggo Ladi ta kamo hannun Zinneerah ta buɗe tafin tana kallo, ta kuma ɗago fuskarta ta gwale mata idanu nanma. Sai kuma tace ta buɗe bakinta ta turo harshenta waje. Ita dai Zinneerah babu musu komai yi take cike da tunanin ko wani ciwone ya kamata. dan a watani uku ɗin nan data dawo gida ƙwarai da gaske tanajin canji sosai a jikinta wanda batasan kansa ba.....

       “Wlhy wannan yarinyar ciki ne da ita Asabe. idanma baku yarda ba ku kaita ayi gwaji wajen likita”.

     Zancen Gwaggo Ladi ya katse tunanin Zinneerah. Yayinda a take gidan ya harmutse da salllami da gulma. Sam Zinneerah bata fahimci komai a zancen Gwaggo Ladi ɗinba, duk da yanayin mutanen dake gidan ya sake sakata a tashin hankali.

     A haukace Inna tazo ta kai hannu zata kai mata maguza wata ƙanwarta ta tare tana janye Zinneerah ɗin. “Haba Asabe, ita dake cikin wannan halin zaki kaima wannan bugun? Kamata yayi a bita a sannu asan inda al'amarin ya hito ai ko?”.

         “A ina ya hito banda wajen yawonta na tazubar Haule. Idan na hiɗi ya rinyarnan nabin maza sai ace sheri nake mata dan ban haiheta ba. Kwanan nan fa tahiya tai babu wanda yasan ina taje kusan mako huɗu sannan ta dawo. Amma da yake ubanta shashasha ne bai ɗauki wani mataki a kantaba. Wace irin makauniyar rayuwace wannan? Na rantse da ALLAH bata zaunamin gida da cikin rariya. Sai dai ta koma can gidan wanda ya ƙunsa mata masihwar su ƙarata tambaɗaɗɗiyar yarinya”.

      Yanda Inna ke masifa kamar zata haɗiye harshentane ya saka gidan yin tsit kowa yana saurarenta. Yayinda hajijiya take juyama Zinneerah garin a hankali. Babu zato sai ganinta kawai akai ƙasa ta zube.

     Babu wanda yay yunƙurin taimaka mata sai Sa'a dake kuka tun farkon fara maganar, ta taho da gudu ta durƙusa gabanta tare da ɗagota jikinta tana jijjigata. Tsawa inna ta daka mata akan ta tashi a wajen kota tsine mata.

     Cikin kukan Sa'a ke girgizama Inna kanta. “Haba Innarmu! Haba Innarmu!. Wlhy Innarmu Zinni ba ƴar iska bace. Wlhy Zinni bata iskanc......”

    Ta kasa ƙarasawa saboda kukan daya sarƙeta. Yaya Gajeje ce ta tako inda suke itama tana share hawaye da bakin zaninta. Ta durƙusa ta kamo kan Zinneerah dake a jikin Sa'a ta maido kan cinyarta tana fashewa da kuka maiban tausayi.....


         Bayyana irin tashin hankalin da Zinneerah ta tsinci kanta a cikin wannan rana da duk wani masoyinta ma ɓata lokacine. Hatta da maƙiyan nata jimami suke nunawa a zahiri, a baɗini kam ransu fari tas musamman ma Inna da ke ganin fatanta ya tabbata.

       Kamar yanda Zinneerah ta yanke jiki ta faɗi sai da aka zuba mata ruwa haka Baba ma da labarin ya riskesa tamkar saukar aradu ya zube babu numfashi sai da aka zuba masa ruwa ya farfaɗo da ƙyar.

      Kafin wani dogon lokaci garin ya ɗauki zance Zinneerah tayi cikin shege. Tofa abin nema ya samu ga masu ƴancin faɗin albarkacin baki. Wasu suce mugun alkaba'in Inna ne ya kamata, wasu suce wahalar da Innar ke batace ta kaita da fara bin mazan ai. Wasu suce babu wani dama halintane. Dan kawai tana shan wahala a gidansu sai ta bi maza.

     Kowa dai da inda nasa furucin ke sauka. Duk da ba yaune ainahin ɗaurin aure ba sai ga mutane na tururuwar shigowa gidan gulma da son ganin ƙwaƙwaf. Ƴammata kam harda waɗanda Karima ma bata gayyata zaman ƙunshin ba sai gasu.

      Inna kam tanata zabga bala'i sai Zinneerah ta bar mata gida ƴan uwanta na tausarta. Yayinda Zinneerah ke a ɗakinsu tare da Baba da Yaya Gajeje da Sa'a. Sai wasu ƙanen Baban maza su uku da mace ɗaya sun turketa akan saita faɗa musu a ina ta samo wannan jidalin?…

      Kuka Zinneerah keyi tamkar numfashinta zai rabu da gangar jikinta. A karo na babu adadi ta sake faɗin, “Wlhy! Ta-kwaran-kwatsa Kawu ban taɓa aikata iskanci ba. Wlhy ni banda ciki.”

       Cikin daka mata tsawa Kawu haruna yace, “Kinci uwarki Zinni. Su waɗanda sukace kinada cikin zasu maki ƙarya kenan? Bayan duk ga alamomin mai juna biyu tattare da ke. Idanfa baki hiɗi mamu wanda kukai wannan lalatar to kuwa kina barin garinga kije can ki nema wasu iyayen bamuba. Dan bamu zama da mai halin banza cikin zuri'armu kau...”

        “Ai bama barin gariba ni nan da kake gani rami zansa amani na bizneta da ranta har sai ta mutu idan bata hiɗi mamu gaskiya”.

     Tirƙashi. Tunfa su kawu nabin Zinneerah da lallami akan sanin gaskiyar magana har takai Kawu Sabi'u da fara bugunta amma ta kafe akan itafa bata taɓa aikata abinda ake tuhumarta ba. Tsabar tashin hankali kowa kansa ya ɗauki zafi. Baba ma ya kasa magana sam.

     Ganin suna neman halaka yarinya wata a cikin ƴan uwan Inna dake aure a kankia tace, “Kunga karkuce ta wannan hanyar zaku tuhumi yarinyarnan. Sannan har yanzu babu tabbacin cikinne a jikinta ko saɓanin haka. Kamata yayi ku sami likita yay mata gwaji, idan an tabbatar cikinne sai a bita ta hanya mai sauƙi a binciketa bawai ta kwakwazo da azabtarwaba. Dan yanzu idan cikinne ai sai kuyi mata lahani ita da shi k.......”

       “K Halima bamu son tsarin banza da wohi. Kinason hiɗin ita Yaya Ladi ƙarya tayi kenan da tace akwai cikin? Bayan duk wanda ya kalla wannan sheɗaniyar yarinyar zai tabbatar da alamomin mai ciki tattare da ita...”

       “Ba haka nake nihi ba yaya Asabe. Tayaya zan ƙaryata Yaya Ladi ni kuwa. Ni dai ina nuna maku muhimmancin bin komai a sannune. Yanzu wannan ruɗama yarinyar tunani da bugun nata da akeyine zaisa ta hiɗi gaskiya? A ganina idan anbi komai a sannu sai a kamo gaskiyar al'amarin da mahwarinsa basai anbi hanyar ilatata ba a dawo kuma ana dana sani”.

    Inna zata sake magana Yaya Gajeje ta katseta. “Maganar Gwaggo Halima gaskiyane. Ya kamata mubi komai a sannu kawu. Dan kowa yasan halin Zinni bazata aikata wannan al'amari da ganganba inma har ya tabbata hakane. Ba muba ko jama'ar gari idan zasu hiɗi gaskiya sunsan Zinni yarinyace mai nutsuwa da haƙuri. Wlhy inaji a raina inhar da gaske ciki ne a jikin Zinni sai dai ɗayan biyu ne ya hwaru. Kodai wani la'ananne ne yay mata wayo ya ɓata mata rayuwa. Ko kuma acan inda ta baro wani yay mata hin ƙarhi ya aikata mata wannan zaluncin. Ku tunafa yarinyarnan nemarta akai aka rasa rana tsaka. sai kuma gata ta dawo babu zato. Abin mamaki kuma tamkar an rihe mana bakuna har yanzu bamu sake bi takanta muji yaya akai tabar garinga ba ta kuma dawo? Miya hwaru da ita data tahi? Ina taje? Waye silar hitar tata? Duk bamu binciketa b..........”

       “Gajeje!!!” 

  Inna ta faɗa da wata irin mahaukaciyar tsawa tana nunata. Ta cigaba da faɗin, “Na rantse da ALLAH idan baki hita batun wannan ƴar iskar yarinyar ba daga yau sai na tsine maki a gidan nan ke da Sa'a. Har uban waye zai hiddata a gida da gari banda abokan iskancinta wanda ga sakamakon abibda takeyi ɗin nan ya bayyana kowa ya gansa”.

      Dubanta Gajeje tayi zatai magana. Sai kuma mita tuna oho tai shiru kawai tai ƙasa da kanta tana sharce hawayen dake sakko mata.


        Har dare gidan ya gagara komawa dai-dai. Zinneerah kam tana can ƙuryar ɗakinsu ta ɓuya tana cigaba da kukanta. amma duk da haka bata kasa jiyo yanda ake aibantata a tsakar gidanba ita da mahaifiyarta a bakunan wasu a cikin dangin Inna. Yayinda ƴammata masu zaman ƙunshin Karima suka fara raira mata waƙa cikin habaici da izgili kamar yanda Karima ta sakasu.

     Babu wanda ya hanasu, dan Yaya Gajeje tabar gidan tun ɗazun. Baba kuwa yana zaune daga can bayan runbunsu shiba mai rai ba shiba gunki ba. Sam zuciyarsa da ƙwaƙwalwarsa basa aiki irin na mutane.

        Duk da ƙarancin shekarunta yinin yau ya sake tabbatar mata da rayuwa ta sake kaita wani ajin jarabawar da yafi zaman gidansu ƙunci da tashin hankali. Ita dai ko Al-qur'ani aka bata zata iya rantsewa da shi akan bata taɓa aikata iskanci ba, amma sai gashi yau an wayi gari ita ake kira da suna mai ciki, cikinma cikin shege. Ta sake fashewa da kuka mai cin rai.


★★★


        Zamu iya cewa a wannan dare barci ɓarawo ne kawai ya saci Zinneerah kasancewarsa gwanin iya sata. Amma badan taji sha'awar yinsaba ko buƙata.

      A kiran sallar farko ta tashi, taji daɗin jin gidan shiru alamar kowa bai tashiba. Ta lallaɓa ta fito zuwa bayi. Bayan ta kammala lalurarta tai alwala ta sake shigewa ɗakinsu. Daga haka bata sake fitowa ba har sai da rana ta haska. Zuwa lokacin gidan ya cika da hayaniyar baƙi da yaransu. Kamar jiya dai kowa da zancen cikin nata ya tashi a baki, hakan yasa ta sake maƙurewa a ɗaki taƙi fitowa.

    Tana zaune kanta cikin gwiwarta taji muryar Gwaggo Laritu ƙanwar su baba na kiran sunanta. Kanta ta ɗago muryarta data sha kuka a dusashe tana amsawa. Fuskar Gwaggo Laritu a haɗe tace, “Taso ki hito”.

       Sosai gabanta ya faɗi, sai dai babu damar musu dole ta miƙe tana rangajin yunwa da damuwa. Kamar jira ake ta fito tsakar gidan yay tsit idanu caahh a kanta. Tai ƙasa da kai zuciyarta na tsitstsinkewa dan tashin hankali...

      “Munahika, ƴar iskar yarinya. Ƙyahwa ta duƙar da kai kamar balamar tunkiya tunda kin kwaso mamu abin kunya”.

    Inna ta faɗa tana jan tsaki. Ita dai Zinneerah kanta a duƙe bata yarda ta kalli kowaba. Ta kuma kasa ɗaga ƙafarta dan batasan ina zata dosaba. 

        Sa'a ce ta taso daga inda take zaune tazo ta kama hannunta, itama muryar tata a dasashe alamar tasha kuka tace, “Muje Zinni, su baba na jiranki a zaure”.

     Da ƙyar ta iya ɗaga ƙafafunta tabi Sa'a har zauren. Baba na zaune shi da su Kawu Haruna. Ƙasa ta zube cikin rawar murya tana gaishesu. Babu wanda ya karɓa mata, sai Gwaggo Laritu ce tace, “Ya kamata mutahi kar rana tai tsaka tunda ta hito”.

     Nanma babu wanda ya iya cewa komai, sai miƙewa da su kawun sukai amma banda Baba da kansa ke ƙasa. tunda Zinneerah ta fito ko motsi baimayiba. Koda sukai masa sallama zasu tafinma bai motsa ba. Bai kuma ce uffanba har suka tasa Zinneerah gaba suka fice.

      Mashina biyu dake jiransu suka taras a ƙofar gida. Kawu Sabi'u da Kawu Haruna suka hau ɗaya. Ita kuma da Gwaggo Laritu suka hau ɗaya batare da tasan ina suka nufa ba. 

         Ƙasa zinneerah tai da kanta har suka baro cikin garin Danya. Wanda tasan tunda kasancewar safiyane kowa yaga tahowar tasu, waɗandama basu ganiba zasu samu labari ga waɗanda suka gani ɗin.

          

      Har cikin Kusada masu mashinan nan suka kaisu babban asibitin Kusada. Kasancewar ɗan mashin ɗin daya goyo su Kawu babban ɗan Kawu Sabi'u ne shine yay musu shige da ficin komai har suka sami ganin likita kusan sha ɗaya na rana. Duk da a matuƙar tsorace Zinneerah take bataƙi amsa tambayar da duk likitan yay mata ba. Bayan ya gama mata tambayoyin yasa aka kira masa wata matashiyar budurwa. Zinneerah ya nuna mata yana faɗin, “Maryam kuje da ita tai hitsari akaima Bashir”.

      Budurwa daya kira da Maryam ta amsa da to a girmame tana duban Zinneerah. Tashi Zinneerah tayi ta bita zuciyarta na ƙara shiga damuwa da firgici. Bayan ta kaita wani banɗaki tayi fitsari a wata roba suka fito. Zinneerah wajensu Gwaggo Laritu ta dawo. ita kuma Maryam ta tafi cika umarnin likita.

     Sunyi zaman kusan mintuna arba'in Maryam tazo ta wucesu zuwa ofishin likita. Dansu tuni sun dawo waje sunba sauran marasa lafiyar damar shiga suma.. Kusan mintuna goma Maryam tazo tai kiransu.

     Kamar ɗazu daga ita sai Gwaggo Laritu suka shiga. bayan sun zauna likita ya dubesu da murmushi yana faɗin, “Masha ALLAH mamana ga sakamakon gwajin hitsarin da mukai mata ya hito. Duk da dama dai kafinma hakan na fahimci ciwon na ƙanwata abin so ne. Amma duk da haka dai nafi yarda da'a gwada ɗin......”

       Cikin ƙosawa Gwaggo Laritu tace, “To madallah, mike damunta?”.

       Sake faɗaɗa murmushi likita yay yana duban Zinneerah da kanta ke a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta. “A'a Inna ba wani abu baneba face ƙaruwa muka samu. Tanada ciki na kusan watanni huɗu. Kuma Alhmdllh yana cikin ƙoshin lafiya kamar yanda itama alamomi suka nuna tana cikin ƙoshin lafiya, sai dai kuma ya kamata a ringa kula da abincin da zataci saboda shima yaron cikin nata ya samu nagartaccen raino.......”

     Sam Gwaggo Laritu da Zinneerah ba fahimtar bayanin likitan sukeba tunda ya ambaci ciki. Dan Zinneerah ma wani irin hajijiya take gani. Tun ofishin na juya mata har ta koma ganin duhu a cikin idanunta. Sai kawai ganinta sukai a ƙasa daga ita har kujerar robar da take zaune a kai.

       “Ya subahana”. Doctor ya faɗa yana zabura saboda faɗuwar Zinneerah. Hakan kuma yay dai-dai da dawowar Gwaggo Laritu datai suman wucin gadi itama hayyacinta. Yayinda su Kawu Rabilu suka shigo da gudu saboda jin sallalamin da likita da budurwar nan Maryam keyi akan Zinneerah da alamomi suka tabbatar da suma tayi............✍

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post