Makauniyar Kaddara Hausa Novel page 21-25 - Novels Elite

Makauniyar Kaddara Hausa Novel page 21-25 - Novels Elite

Makauniyar Kaddara Hausa Novel page 21-30 - Novels Elite

MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

 

*Page 21*

 

...........Khalipha kam da zuciyarsa tayi matuƙar nisa a cikin tunani sam baiji mi yayan nasuma ya faɗaba. Yaɗan ɗago ya dubi Moos'ab ɗin kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru yana binsu da kallon mamaki su duka ganin yanda duk suka sake nutsuwa. Sashen da yayansu yake ya maida kallonsa, sai yaga hankalinsama baya kan kowannensu.

      Maida kansa kawai yayi ga abincinsa shima, sai dai gaba ɗaya hankalinsa ya tafine ga tunanin sake son ganin yarinyar ɗazu da sukace sunanta Zinneerah.

      Har aka kammala breakfast ɗin babu wanda ya ƙara ƙwaƙwaran motsi. Shine ya fara tashi a dining ɗin, suka bishi da kallo harya shige ɗakinsa. Tamkar jira suke yabar wajen suka fara ƙus-ƙus na gulma.

        “ALLAH ya baku sa'a ya fito ya jiku”. Khalipha ya faɗa yana miƙewa shima ɗauke da kofin shayi ya nufi ɗakin Hajiya Iya. Zaune take a gaban gadon saman carpet ɗin dake a malale, ta mimmiƙe ƙafafunta dake mata zugi, dan ciwon da suke matannema ya hanata zama cin abinci a dining ɗin yau.

       Fuska ɗauke da murmushi take duban Khalipha. Ya zauna a kusa da ita yana ajiye kofin ya amshi man zafin ya fara shafa mata. “Moddibo fa?”. Hajiya iya ta tambaya tana kallon Khalipha.

    Ya buɗe baki zai bata amsa sallamarsa ta katsesa. Duk suka kalli ƙofar dai-dai yana ziro ƙafarsa ciki. Kallonsu yay ya kauda kai, sai da ya shigo ciki sosai yakai zaune a bakin gadon dai-dai ƙafafun Zinneerah dake ƙudindine a bargo sannan yace, “Ciwo ƙafan yake ne?”.

        “Ba wani da yawa bane ai. Yanzuma zakaga ta saki tunda Khalipha ya daddana min ita”.

      Kansa ya maida ga wayarsa dake haske alamar kira ake batare da yace komaiba.

     “Fita zakayine Yayanmu?”. Khalipha ya faɗa yana kallonsa.

         Kansa ya girgiza masa da faɗin, “No, Phones ɗin yaran nan ne”.

       “Woow, autoci an shigo gari kenan”. Khalipha yay maganar yana jawo ƙyaƙyƙyawar ledar gabansa. Kwalayen wayoyi masu ƙyau da tsada guda shidda ya fiddo a ciki. Ya miƙama Hajiya Iya. “Granny ga wayoyin jikokinki Yayanmu ya cika alƙawari”.

      Murmushi tayi a karan farko da miƙa hannu ta amsa ɗaya tana kallo. “A to lallai munyi rabin shiri da ja'irin nan yau. ALLAH ya saka da alkairi ya bada ladan zuminci”.

     Da amin suka amsa shi da Khalipha. Hajiya iya tace, “To ga kuma Zinneerah ta ƙaru, sai itama kasan yanda zakai da ita, dan ba'a basu wayoyiba ita batada ita”.

      Kamar bazai tankaba sai kuma ya ɗan dubi Hajiya Iyan. “Tunda bansan tana a gidanba sai tai haƙuri sai wani karon”.

      “A'a bazai yuwuba gaskiya Moddibo. A duba mata dai ko anan ita sai a saya mata”.

     Shiru yay bai sake tankawaba duk da sarai yaji mi Hajiya iyan ta faɗa. Sanin halinsa yasa Khalipha saurin faɗin, “A'a Granny a bar Yayanmu ya huta. insha ALLAH ni saina saya mata kawai”.

        Hajiya Iya tace, “To shikenan hakanma yayi ALLAH ya saka muku da alkairi. ya ƙara haɗemin kanku”.

      Khalipha ne kawai ya amsa da amin. Shiko laɓɓansa kawai yaɗan motsa kaɗan alamar ya amsa ɗin.

        Daga Haka Khalipha da Hajiya Iya suka cigaba da hira, shiko yana saurarensune kawai amma baya saka baki sai yaso, yama maida hankalinsa gaba ɗaya akan latsa waya.

      

        Zinneerah da tun shigowar Khalipha ɗakin ta farka taɗan motsa kafarta, jin ta dunguri abu yasata saurin matsarwa baya tana rintse ido. Hakanne ya sakashi ɗan juyawa ya kalli abinda ke bayan nasa duk da tun shigowarsa yaga alamar mutumne kwance. Kamar zaiyi magana sai kuma ya miƙe yana tura wayarsa a aljihun wandon 3quarter ɗinsa. “Ni bara naje zanyi magana da Baffah, zuwa anjima inason zuwa Jigawa”.

      “Jigawa kuma? Yin me?”.

Duban Hajiya iya mai maganar yayi, yaɗan kai yatsa gefen idonsa ya sosa kaɗan da cewar, “Akwai wani gona ne da nakeson yin noman shinkafa. So mun gama magana da Mahmud shine nakeson dubawa”.

       “Tofa, bana kuma nan aka tsallaka kenan? Kai dai duk hanyar neman kuɗi kasanta Moddibo. Kana gudunmu kuma kana son zuwa kaci arziƙin ƙasarmu”.

      “Tunda ni ba ƙasata baceba ko. Idan wannan mai barcin ta tashi taje ta gyaramin ɗaki”. Ya faɗa yana ficewa daga ɗakin abinsa.

       Harara Hajiya iya ta raka bayansa da shi tana yamutsa fuska. “Bauɗaɗen banza jikan ƴan Morocco”.

    A yanda tai maganarne ya tilasta Khalipha ƙyalƙyalewa da dariya shima yana miƙewar. “Granny rigima. show ɗinki da Yayanmu nada matuƙar ƙayatarwa ga mai kallo. ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsahon rai mai amfani uwargida kuma amaryar Abdul-Mutallab Shira”.

         “Oh to, ko kanamin baƙin cikine ba'a taɓamin kishiyaba?”.

    “Wah? Ni?  Rufamin asiri Granny karkisa Baffah yaji ya zagemin uwa. Kinga nayinan raba tsaraba na samo tukuyci. Itama  ya kamata ta tashi ta karya”. Ya nuna Zinneerah da duk tana jinsu amma ta lafe.

       “Eh nima yanzu nake tunanin nan a raina. Barama naji jikin nata kodai batajin daɗine, dan bata saba irin wannan barcinba sam”.

       “Okay to bara naje na dawo sai naji wane hali take ciki”. Daga haka ya fice a ɗakin.

 

       Ihun murnar waya da su Meenal suka shigo ɗakin sunayi ya tilasta Zinneerah tashi. A take suka kaure ɗakin da sabon ihu. Koda Hajiya iya data shiga bayi ta fito tana musu maganar su fice sun dameta a guje suka fita kuwa suna cigaba da ihunsu. Acan harabar gidan suka iske su Abidah suma suna nasu tsallen murnar dan da gaske yayan nasu ya shigo dasu gari da masu zafi kam.

        Duk da babu Zinneerah a cikin masu wayar babu damuwa ko ɗigon sisi tattare da ita, hasalima itace mai farke wayoyin su Bahijja daga cikin kwalinsun. Da ƙyar hajiya iya ta tilastata zama cin abinci. tana gamawa kuma taje tai gyaran ɗakin nasa daya faɗa kamar yanda Hajiya iya ta sanar mata saƙon duk da itama taji da kunnenta.

    Koda ta kammala taje tai wanka fitowa tai suka ɗora shirmensu daga inda suka tsaya ita da su Jamal. A haka Khalipha ya shigo ya samesu, daga asibiti yake yin bincike akan Zinneerah da suka haɗu wancan karon, dan gaba ɗaya zuciyarsa ta kasa yarda cewa wannan ɗin itace waccan Zinneerah ɗin. Gadai satar kammani sunayi da juna. Amma kuma wayewar kai da wasu abubuwa da yawa ya banbantasu. Babbar matsalar daya samu na rasa Number Naziru da yayi sakamakon wani tsautsayi daya samesa acan London. Yanzu kuma yaje asibitinma a iya binciken da yayi bai samu wani bakin zaren da zai iya nemansu ba. Amma an tabbatar masa ta haihu baby boy.

           Gida ya dawo da sabon tunani akan tunkarar wannan Zinneerah ɗin yaji daga gareta ita kuma, dan a tunaninsa da ace waccan ɗince data ganesa. To waccanma ai matar aurece miyasa zaiyi tunanin itace anan?.

      Ruwa Meenal ta kawo masa ya sha. Ya kumace ta haɗa masa abinci a dining zaije yay wanka ya dawo. Binsa Zinneerah tai da kallo a cikin wani irin bahagon yanayi. Cikin dabara takai hannu ta share ƙwallar da suka ciko mata idanu. A yanzu haka babu abinda kecin ranta da damuwarta sai yanda Khalipha ya nuna tamkar baima taɓa sanintaba. Bayan ita tunda ya barta bata taɓa hutawa da tunaninsaba a ranta. har mafarkinsa tasha yi ma. Amma insha ALLAH zata daure itama ta kama kanta gareshi, idan ya ganota fine. idan ya cigaba da pretending ɗin rashin sanin nata itama saita samawa kanta lafiya ai. Da wannan tunani ta cigaba da hidimarta har lokacin Islamiyya yayi suka fita.

 

 

*_DANYA_*

 

            Tafe take buguzun-buguzin cikin uwar ranar dake ƙwalle ga zafi da take da shi. Ga wanda baisan halin ruɗanin da take ciki a ƴan watannin nan ba sai ya ɗauka ko mahaukaciya ce. Duk ta fige ta fita hayyacinta tun barin Baba garin Danya. Duk dukiyar datake taƙama ta tara ta dabbobi da buhunan kayan masarufi sun ƙare tas wajen bin gidajen malamai dake mata aiki akan yima Baba kiranye ya dawo gida duk inda yake.

       Aikin ake kamar ba gobe amma babu alamar yanaci dan har yau ko inda Baba yake babu wanda yazo yace yaji. Gashi kullum malam nata ƙarya suke mata Zinneerah nacan tama zama karuwa a binnin ikko. Sosai wannan labarin ke mata daɗi akan Zinneerah. dan bata da burin daya wuce taga yarinyar ta tagayyara ta wulaƙanta a duniya, saboda kawai tazo matsayin ƴar kishiyarta.

     (Ƴan uwana mata dan ALLAH mu canja, mu daina saka yara a kishinmu. sannan kishinma mu dinga sassautama zukatanmu. Nasan kishi dolene domin kamar jininmune. To amma suma mazan idan suka fahimci kana musu kishi na hauka duk da sonsu ne yake jawo hakan saisu maidaka wawa mahaukaci. ka kuma fita a cikin ransu ma baki ɗaya su koma ganin baƙinka maimakon hasken da kake dashi a garesu. Babu amfani kai burin lalacewar ɗan wani ko shigarsa wani bala'in rayuwa. Dan kaima ba tsira naka zaiyiba wlhy. dan ba'a taɓa shuka dawa a girbi shinkafa. Sai ka ƙyautata zato da addu'a ga ɗan wani kaima ALLAH zaiji ƙanka ya ƙyautata rayuwar naka ƴaƴan insha ALLAH. ALLAH yasa mufi ƙarfin zukatanmu😭🙏🏻).

       Yanzunma wani ƙauye can nesa dasu sosai akai mata kwatancen wani malami shine taje. A yanzu haka dai ya mata alƙawarin dawowar Baba nanda kwanaki bakwai, idan har bai dawo ɗinba zai biyata kuɗin daya karɓa a wajenta. Hakkane ya sata tahowa gida cike da ƙwarin Gwiwa ko ranar dake dukanta da azabar tafi bataji.

        Shiru ta iske gidan babu kowa. ta zube ƙarƙashin bishiyar tsakar gidan nasu tana maida numfashi da ƙyar. Ta kusa mintuna biyar a haka kafin ta miƙe zuwa randunansu dan tasha ruwa. Wayam ta samu tabbacin dai Tinene data barma sallahon ɗebo musu ruwan bata ɗebo ɗinba kenan. A take ranta ya ɓaci taja ƙafafunta da ƙyar ta koma ta zauna dan har juwa takeji saboda yunwa. Ko karyawa bataiba ta fita, ɗan hatsin da baba ya bari a rumbu duk sun cinye ta salwantar da wani kuma wajen bin malamanta na tsiya. Hakan yasa abincima sau uku a gidan wataran gagararsu yakeyi. sai idan Yaya Gajeje taji tausayinsu ta ɗakko ta kawo musu. Koda yake mafi yawancin lokacima itace ke zama da yunwar, dan Tinene sai dai ta ganta da kayan ciye-ciye ta shigo. bata isa tambayarta kuma ina ta samosuba saita hayayyaƙo mata da rashin kunya. Wani lokacinma bata tambayar tata amsa take itama taci saboda wahala. Sa'a kuwa yanzu takan jera kwana huɗu biyar bata kwana a gidanba. Tuni ta koma gidan Baba Rabilu abinta, dan ɗansa ya maidata makaranta tana zuwa. da Inna ta nuna bata yarda bane yasa Sa'a tattara inata-inata ta kona can gidan. Sai randa ta bushi iska take zuwa ta kwana anan tunda yanzu babu talla Malamai sun cinye jarin Inna Asaben.

       Miƙewa Inna tai tana tsinar Tinene a cikin ranta, dan yunwa da wahalar tafiya tasa koma magana mai ƙarfi bata iyayi. Ɗakinta ta shige ta faɗa saman gado da fatan ALLAH ya kawo wani a cikinsu Sa'a ɗin ya taimaketa da ko kunu ne taɗan kurɓama cikinta ko taji dama-damar tashi ta bizne aykin malam.

       ALLAH kuwa ya taimaketa babu jimawa ta farajin motsi a tsakar gidan da ƙarar taunar chewing gum. ko ba'a faɗaba tasan dai Tinene ce. Dan itace mai ɗabi'ar cin cingam ɗin a koda yaushe. Idan tai mata magana tace mata ƙoshi ya sakata ci danta rage nauyin cikinta. Dole Innar keyin shiru dan Tinene kam ta fara fin ƙarfinta. Gashi kuma wani lokacin tana ɗan samun mai daɗi a wajenta taci.

     Bankaɗa labilen da akaine ya sakata ɗago idonta ta kalli ƙofar. Tinene dake tsaye a bakin ƙofa tana cakal-cakal da cingam a baki cikin rashin ladabi tace, “Oh oh, wai se yanzu kike dawowa gida Innarmu? Ke dai baki gajiya da mikama maluma kuɗi suna cinyewa mu baki anhwana mana da ko taro ba a ciki. Naga dai Baban da ƙahwarsa yabar gidan ba saceshi akaiba halan”.

     Kasa cemata uffan Inna tai, sai kanta data girgiza kawai. Hakan datai ya bana Tinene haushi, harta saki labulen da niyyar barin wajen Inna ta ƙwala mata kira cikin ƙarfin hali. “Tinene wai nikan yaushene zaki natsune? Ni yanzu duk bama wanga ba. Dan ALLAH idan da goma hannunki ko murtala kije nan gidan dije ki sayo mani kunu koba suga nasha”.

    Baki Tinene ta zunɓura gaba. kanar zatai magana sai kuma taja tsaki fuuu ta fice tana ƙunƙuni. “K kuɗinki na wajen bokaye da malamai ni kuma kin sakama nawa ido mu ramtsesu tare. Bayan duk kece kika jehwamu a wagga rayuwa ta yunwa da talauci wajen neman baƙin asirinki mtsoww”.

      Da wanan mitar taje ta sayo kunun na goma ta kawo mata dukda ba wani na kirki bane. Da rawar jiki kuwa Inna ta amsa tahau sha duk da zafin da yake da shi. Ta saki gyatsa tana ajiye kofin duk da bata ƙoshi bane yanda take buƙata. Daga haka ta zame ta koma kwance tana zufa. Tinene ta taɓe baki da nufar hanyar ficewa gidan tanama Innar tasu baƙar magana.

 

(Hhhh yanzu aka fara wasan Hajja Asabe😂😂😜).

 

________________________★★

 

           Washe gari lahadi ma duk suna a gidan, sai dai banga Khalipha da Yah Adnan da suka tafi jigawa. Dan jiya bai samu damar zuwanba saboda wani uziri. Bayan sallar la'asar duk suna zaune a falo suna ɗan hira iyasu ƴammatan sai ga Safiyya da ita kaɗaice bata gidan. Momie ta aiketa can wajen yayarta kai saƙo.

        A yanda ta shigo falon kamar wadda aka koro ya sakasu duk suka zuba mata ido. “Ke lafiyarki kuwa?”. Hajiya iya data kasa haƙuri ta faɗa tana duban Safiyyan.

          “Humm Granny inafa lafiya, wlhy wani abun al'ajabi da ruɗani nai gamo dashi a yanzun nan hanyata ta dawowa daga gidan Umma”.

       Duka falon maida hankalinsu sukai a kanta, kowa nason jin dami tai gamon?. Wayarta ta lalubo a jakka tai ƴan danne-danne sannan ta miƙama Hajiya iya. “Granny dan ALLAH kikalli yaron nan dawa yay miki kama?”.

      Cikin rashin damuwa Hajiya Iya ta amshi wayar. Yanda tai kasare tana kallon wayar ya saka su Meenal duk suka zuba mata ido suma. Itama da alamun makamancin irin ruɗanin da Safiyyar ta shigo da shi tace, “Keko Safiyya a ina kikaga wannan yaron haka?”.

        “Wlhy Granny a Napep. Mun taho da driver motar ta mutu a hanya. Shinefa nace masa bara na tare napep na ƙaraso gida. Mun daɗe tsaye yanason taremin ba'a samuba sai da ƙyar ya tsaida wanda ke ɗauke da maman yaron nan.

     Hajiya iya daketa faman jinjina kanta tace, “Amma wannan kamanni da mamaki a cikinsa. Koda yake hakan kan faru koda baka haɗa komai da mutumba. Amma ita matar a ina take?”.

       “Wlhy ban tambayetaba Granny, amma da alama wani waje zatajema. Bama tasan na ɗauki hoton yaronba dan cikin dabara nayi”.

      Wani irin nannauyan numfashi hajiya iya ta sauƙe. Sai kuma ta miƙama Abidah wayar ganin duk sun zaƙu su gani. A haka samarin gidan dake shigowa a tare sukazo suka samesu. Ganin yanda aketa ƴar bayayya da waya ya sakasu tambayar ko lafiya?. Safiyya ce tai musu bayani. Amsar wayar suma sukai duk suka gani. Duk wanda ya kalli hoton sai ga mamaki ya bayyana a fuskarsa da ruɗani.

        Duk wannan al'amari dake faruwa Zinneerah nacan ɗaki tana shirya kayanta data kwaso a ɗakin Yah Adnan cikin wadrobe ɗin Hajiya iya. Hakan yasa batasan hidimar da akeyiba. Dan so take ta gama shiryasu a daren yau tunda gobe idan ALLAH ya kaimu monday akwai makaranta.

        Kasancewar dama bata fara aikin da wuriba sai gashi har Hajiya iya ta shigo domin sallar magrib bata kammalaba. Sai kusan sha ɗaya ta gama lokacin hajiya iya ta jima dayin barci mai cike da mafarkin yaron da Safiyya ta kawo musu a hoto, takan dai tashi tai salla idan lokaci yayi. Su meenal kuma sunɗan lekota, sanin hajiya iya idan ta kwanta batason surutu yasa suka fice suka barta ita kaɗai ta cigaba da aikinta.

          A falo kuwa hirarsu suka cigaba dayi bayan tasowar hajiya iya. Dan duk sun barma kansu cewar kamannine kawai da akan samu a rayuwa tsakanin wani da wani koda babu alaƙar jini saboda hikimar UBANGIJI. Basu wani jimaba suka fice duk da Moos'ab yaso ganin Zinneerah kafin ya wuce ɗin. Rashin samuwar hakan ya sakashi haƙura kawai.

 

        Tun daga wannan ranar babu wanda ya sake tada zance akan hoton yaro, sai dai abin na nan maƙale a zuciyar Hajiya Iya ta kasa mantawa. Tanason yin maganar kuma wata zuciya na kwaɓarta akan kamannine kawai. Idan kuma tace zata kawoma zuciyarta wani tunani daban ya zata alaƙanta al'amarin ma to. Hakan yasata tsuke bakinta ta barma ranta komai kawai.

 

     kwanaki sun cigaba da shurawa a hankali sai ga Khalipha da Adnan na cika kwanaki goma da zuwa. Ko kaɗan Zinneerah ta kasa sabawa da kasancewar sa a gidan duk da a kwanakin nan bai cika zamaba kullum suna hanyar Jigawa gonar da zaiyi noman shinkafa. Sukan fitama kafin su su fito, wani lokacin kuma sai sunyi barci suke dawowa. Wannan dalilin yasa takanyi kwanaki uku biyu ma bata sakashi a idontaba har Khalipha ɗin da take marmarin gani a ko yaushe.

      A kwanakin nan daya ɗauka gaba ɗaya hidimar gyaran ɗakinsa ta dawo kan Zinneerah. Kullum ita yake cewa taje ta gyara masa ɗaki. Bata damuba dan dama ta rigada ta saba.

Idan ta ganshi tsoro na matuƙar kamata, dan kullum abubuwan daya dangancesa suna sake danganta kansu da abinda sam ta kasa gaskatawa. 

       A randa suka cika kwanaki goma sha uku a gidan basuje gona ba, amma duk da haka babu wanda ya sakashi a ido sai yamma. Yana ɗakinsa yana harkokinsa na business a lap-top.

 

        Zinneerah, Meenal, Bahijja sai Jamal na zaune a falon hajiya iya Yah Khalipha ya shigo. duk sannu sukai masa ya amsa yana zama kujerar dake facing ɗin Zinneerah da Bahijja. Cikin kafe Zinneerah ɗin da idanu ya miƙa mata ledar hannunsa yana murmushi.

        “Ƙanwata yau dai ga wayarki na cika alƙawari”. Kafinma ta kai ga yunƙurawa amsar wayar Jamal yay azamar zuwa ya amsa yana washe baki. A take suka rufi akan wayar suna tayata murna duk da ba irin tasu Meenal ɗin bace ba, amma itama ta haɗu. Tasowa Zinneerah tai tsam inda yake takai tsigunne kanta a ƙasa tana faɗin, “Nagode sosai Yah Khalipha, ALLAH ya ƙara buɗi mai albarka”.

      Kansa ya jinjina mata yana sake faɗaɗa murmushinsa. Sai kuma ya miƙe ya fice zuciyarsa na bashi ƙwarin gwiwa akan yau ya tunkareta da zancen nan. Dan yauɗin kawai ke garesa Yah Adnan yace nanda kwanaki huɗu idan ALLAH ya kaimu maybe zasu wuce Abuja. Daga can kuma bazasu dawo Kano ba London zasu koma zaiyi wasu uzirinsa kafin ya dawo akan zancen auren su Ni'ima da ayanzu haka an tsaida rana da kuma maganar Company da yake tunanin buɗew na shinkafa.

     Binsa da Kallo Zinneerah tayi ƙwalla na cika mata idanu, sai kuma ta miƙe tsaye tana murmushi saboda wani abu data tuna. Idanuntane suka sauka akan Yah Adnan dake tsaye bakin ƙofarsa da waya a kunne yayi wani kicin-kicin da fuska............

 

 

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

 

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

 

*_ AL-ƘIBLA_*💘

 

*_ MADUBIN ZUCIYA_*💖

 

*_ DALAAL_*💝

 

*_ UBAYD MALEEK_*💓

 

*_ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

 

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

 

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

 

Kamar haka👇🏻💃🏻

 

Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700

 

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

 

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

 

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

 

*_08085405215_*

 

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

 

  0903 234 5899

 

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

 

*_ALLAH ka gafarma iyayenmu🙏🏻😭_*

 

 

*_TYPING📲_*

 

 

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

 

 

__________________________

 

 

*_ina 'yan uwa musulmai masu kishin addinin islama???_*

 

*_maza ku matso ga wani aikin lada ya samu_*

 

*_Ɗanku kuma dan uwanku kuma qaninku wato ABDURRAHMAN, yaro mai hazaqa, ƙwazo da tarin baiwa, gami da kwadayin haddace littafin Allah mai tsarki, ya bude YOUTUBE CHANNEL nashi na qashin kansa, ku tallafa masa ta hanyar shiga wannan shudin rubutun ku danna masa subscribe, ba abunda xai rageku dashi saima samun dimbin lada dalilin KARFAFA MASA GWIWA, MUN GODE 🙏🏽🙏🏽🙏🏽_*

👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽

 

https://youtu.be/WWIGq5Jbtb0

 

 

_______________________

 

 

*Page 22*

 

.........Cikin sauri ta haɗe murmushinta dayin diri-diri na alamar rikicewa. Dan wani irin kallo da take kasa fassarawa a duk sanda yay matashi ya watso mata yanzuma ya ɗauke kansa fuskarsa na ƙara tsukewa fiye da yanda ya fito. Sum-sum ta juya gasu Bahijja da suma sukai tsitt daga ihun da sukeyi na murnar wayarta zata zauna yace, “Haɗomin black tea yanzun nan”. Daga haka ya juya ya koma ɗakinsa.

       Da sauri duk suka kalli Zinneerah da itama kallonsu take. Meenal tace, “Wlhy ki tashi kafin yace kin ɓata masa lokaci”. A take idon Zinneerah ya fara tara ƙwalla. Dan wannan shine karo na farko da ya sakata irin wannan aikin bayan gyaran ɗakinsa.

     Bahijja tace, “Kinsan mi zakiyi?”

Zinneerah ta girgiza mata kai da sauri. “Kije kima Baba Rahi magana ta haɗa miki, dan tafi kowa sanin abinda yakeso a nan gidan bayan Granny. ALLAH yasa basu tafi ba, tunda ba gani yayba ki fiske abinki ki kai masa kawai a rabu lafiya. Dan shi inhar ya sakaka abu bakayi dai-dai yanda ya buƙataba ka shiga uku”.

       Jin abinda Bahijjan ta faɗa ɗinne ya sake tsurar mata da ciki, amma shawarar saka Baba Rahi ta haɗa matan ya sata jin sassauci. Da sauri ta miƙe zuwa kitchen, sai dai wayam babu baba Rahi a ciki. Tai saurin kallon agogon dake a kitchen ɗin wanda ya bata tabbacin Baba Rahi ta wuce gida dan ba'a nan take kwanaba daman.

     A take ƙwallan da take maƙalewa suka silalo mata. Jiki a sanyaye ta ɗiba kayan ƙamshi tasa a turmin ƙarfensu ɗan ƙarami ta hau dakawa. Cikin ƙanƙanin lokaci ta gama dafa shayin daketa uban ƙamshi a kicin ɗin, sai dai duk wannan ƙamshin nasa dazai iya saka mai kallo buƙatar sha ita a tsorace take. Ƙaramin flask ta samu ta juye tare da ɗorawa a tire ta saka kofuna biyu da mitsilin bowl data zuba suga a ciki ta ɗakko ta fito tana karanto addu'ar nasara a cikin ranta.

       Bata iske kowa a falonba su Jamal sun gudu, hakanne ya sake ɗarsa mata tsoro a cikin rai ta nufi ɗakin tamkar an daddoke mata gwiyawu. Sai da tai sallama kusan sau huɗu sannan ya amsa mata da bata izinin shiga. Ta tura ƙofar ta shigo ƙamshinsa na rige-rigen shiga mata hanci. Tsaye yake a gaban mirror sanye cikin farar jallabiya ruwan madara yana ƙoƙarin ɗaukar wayarsa dake vibration.

     Tai saurin kauda kanta ƙasa murya na ɗan rawa tace, “Yayanmu ga tea ɗin”.

        Juyowa yay dai-dai yana ɗora wayar tasa a kunne ya kalleta da fararen idanunsa da suka nema ruɗata. Dan itama yayi dai-dai da ɗago nata zata saci kallonsa. Ƙasa tai da kanta shima ya janye nasa yana zama kan sofa. Ƙafa ɗaya ya ɗora kan ɗaya yana kai bayansa ya jingina da kujerar ya sake dubanta ya ɗauke kai. “Zaki cigaba da tsayamin a kaine?”.

         A sanyaye Zinneerah ta ƙaraso ta ajiye tiren saman table ɗin gabansa, dai-dai yana faɗin, “Ina ruwanki da ko wacece. Ki cigaba da maganarki kona kashe wayata”. Ya ƙare maganar dajan guntun tsaki.

        Zinneerah dai dake saurarensa haka kawai ranta ya bata matarsace. maganar su Meenal data tuna yasata kaiwa tsuggunne ta fara ƙoƙarin zuba masa a kofin. Sai dai jin kamar ana kallonta ya sata ɗan daburcewa, kamar zata ɗago sai kuma ta fasa.

     Kamar ya fahimci ta gane kallonta yake sai ya miƙe gaba ɗaya yana bama matarsa dake tambayar ya bata hajiya iya amsar da cewar “Bama tare”.

           Tabbas Zinneerah taji kalmar “Bama tare” daya faɗa, sai dai batajin mi matar tasa ke faɗa dagacan, a bazata taji saukar wata gigitacciyar tsawarsa cikin kunnuwanta. Ai batama san sanda ta zube ƙasa daɓar ba tana cusa kanta a ƙafafunta jikinta na rawa. Shiko da baisan tanayiba ya cigaba dayin magana a hasale matuƙa.

        “Farah! Ki shiga hankalinki, ke miyasa a kullum tunaninki baya a layin na masu hankali? To kije hakaɗinne ma, ai dai nima namijine ko? Wawuya kawai mtsoww”. Ya ƙare maganar dajan wawan tsaki yana yanke wayar ya jefa saman gado. Wadrobe ya nufa ya finciki murfin da ƙarfi ransa na nasa suya, ya rasa wane irin hukunci zai fara yima Farah akan yawan furta kalmar zargi gareshi a duk lokacin da yay nesa da ita zuwa wani waje. Inhar zaiyi tafiya ta dinga bin ƙwaƙwƙwafinsa kenan tamkar wani ɗanta saboda shegen kishinta na tsiya.

          “Zan koya miki hankali”

Ya fada zuciyarsa na sake kumbura. Ɓacin ran da yake a ciki ya sakashi mantawa da Zinneerah a ɗakin ya fara ƙoƙarin fara shiryawa.

        Shirun da tajine ya sakata ɗago kanta a tunaninta fita yayi. Babu shiri ta miƙe ta fita da gudu ganin ya fiddo kaya alamar sanyawa zaiyi.

       Shikam baimasan tanayiba, Sai da ya gama saka kayan ya nufo mirror dan saka turare idonsa ya sauka a kan kayan data ajiye, sai dai babu ita a wajen. Wani sabon takaicine ya sake lulluɓesa tuna abinda Farah ta faɗa akanta. Ya cije baki da rumtse idanunsa da ƙarfi yana raya wannan karon sai tasan shi take dangantawa da Zina wlhy.....

       Yana ƙoƙarin zaman shan shayin da Zinneerah ta zuba kira ya shigo masa. Sanin mai wannan ringtone ɗin yasashi miƙewa ya ɗauka wayar yana ƙoƙarin sassauta fushinsa.

       “Barka Mammah”. Ya faɗa cikin nuna girmamawa a gareta. A take zuciyarsa ta kara rinewa da ɓacin rai dan dama yasan bai wuce Farah takai ƙararsa wajentaba kamar yanda ta saba. Uffan baiceba har Mammah dake zuba faɗa daga can tayi ta gama. Sai daga ƙarshe da tace Farah ɗin zata biyowa Nigeria itama sannan yay magana.

       “Mammah abinda nazoyi nanfa important ne, karki biyema shirmen.......”

    “Saurara min Abdul-Mutallab!!” Ta katsesa a tsawace. “Kana nufin bansan abinda ubanka da kakarka suke shiryawa a kanka bane?, to wlhy su sani ƙwatarka a hannuna wannan karon sunyi kaɗan. Idan har bakaso Farah ta biyoka ka dawo London yau yau ɗin nan tunda kasan tanada lalura a jikinta. Inba hakaba bayan itama tazo nima zanzo dan ina dai-dai da kowa cikinku”.

       “No, Mammah Please, nafa faɗa miki abinda zanzoyi tukan na taho”.

      “Amma baka sanarmin zaka daɗe haka a nanba, dama an manna maka harkar noman ne saboda munafunci ai. Sannan wannan munafikin yaron dake nane da kai ko yaushe idan kun dawo ya wuce hostel da zama, inba hakaba Abdul-Mutallab sainayi bala'i bala'in ɓata ranka, wlhy ubanka ma sai yayi dan.........”

       “Mammah Pleaseeee!”.

Ya faɗa cikin zafin rai, dan ya mugun tsanar yaji tana zagar masa mahaifinsa da ƴan uwansa.

         Ƙitt ta yanke wayar batare data sauraresa ba.

       Kansa ya dafe saboda wani jiri-jiri dake neman kwasarsa. Shin wai wace irin rayuwace wannan mahaifiyarsu kesan taga sunyi? Gaba ɗaya ta tsani taga sun raɓi mahaifinsu da ƴan uwansu. Ta yaya kuwa hakan zata kasance bayan hausawa sunce da uba ake ado. Duk ƙoƙarin da yake wajen fuskantar da ita muhimmancin family ɗinsa bata fahimta. nata ƴan uwan kawai takeso su girmama su raɓa. Anya kuwa idan ya cigaba da biye mata bazai halaka ba. Tunda suke da Baffah bai taɓa nuna masa matsanancin ɓacin ransa akan abinda Mammah takeyi na katangesu daga garesaba irin wannan karon. Har a yanzu haka ya kasa tarosa gaba ɗaya. A da kam idan yayi masa faɗan yakan sakko ya koma nasiha. Amma wannan karon yaƙi sakkowa. Ya dage akan sai yabi umarnin hajiya iya ya ƙara aure yabar matar anan Nigeria idan ita waccan tafi ƙarfin dawowa cikin family ɗinsa ta zauna.

     Zazzafan huci ya furzar yana zamewa ya kwanta a sofar da dafe kansa kawai ya lumshe idanunsa.

       Lokaci mai tsaho ya ɗauka a haka batare da ya saniba. Dan har saida Hajiya Iya ta shigo ɗakin dubashi dan taga har anyi magrib bai gitoba.

       “Moddibo kana lafiya kuwa?”.

Ta faɗa tana kai hannu ta cire nasa daya dafe kansa. Idanunsa ya buɗe a hankali yana kallonta, ta sake maimaita tambayar tana taɓa goshinsa.

     “Lafiya kuwa kake yau har anyi salla baka fito kaje massallaci ba Moddibo?”.

       Zaune ya tashi sosai, Sai kuma ya girgiza mata kansa, “Kaina ke ciwo kawai Granny, bamma san anyi sallanba ai”.

     Tsura masa idanunta tai cike da nazarinsa. Dan ta riga ta gama karance halayyarsa tun ƙuruciya. Duk da ta hango damuwa tattare da shi sai batace komai a kai ba. ta nufi hanyar fita kawai tana cemasa ya tashi to yay sallar”.

      Goshinsa ya murza yana cige laɓensa na ƙasa, har yanzu yana takaicin da mamakin yanda Mammah ke biyema Farah a kowanne lokaci. Duk da yasan akwai nata halin itama ya fahimci akwai zuga mai ƙarfi da akai mata a yau ɗin, a bazata wani guntun murmushi ya suɓuce masa, ya miƙe yana abinsa harya shiga toilet dan shi kaɗan yasan muguntar daya shiryama Farah da mai zuga Mammah ɗin dan ya tabbatar itace taje London ɗin kokuma sunyi waya akan tahowar tata.

     Alwala yayo yazo ya gabatar da sallar magrib data wucesa. Daga haka ya fito zuwa massallaci samun jam'in isha'i. Koda aka idar tare da samarin ƙannensa suka shigo gidan abin sha'awa, su sukai sashensu shi kuma yanufo sashen Hajiya iya. Kamar yanda ya fita bai samu kowa a falonba yanzuma haka ya dawo bai samu kowaba.

     Ɗakin Hajiya iya ya shiga da sallama. Tana zaune a inda tai salla Zinneerah dake fashin salla na kan kujera kwance tana latsa waya, lokaci-lokaci takan matse idanu da baki saboda mararta dake ɗan mata ciwo can ƙasa. Saurin miƙewa tai zaune saboda jin sallamarsa. Sai dai kafin tace zata tashi harya rigada ya shigo. Akanta ya fara sauke idanunsa ya janye. Batare da damuwar ganinta zaune a Sofa ɗinba yakai zaune yana cema hajiya iya “Barka da dare”.

      Zaram Zinneerah ta miƙe a sofar har tana neman faɗuwa. “A hankali mana Zinneerah. Koma saman gado ki kwanta, jira nake wani ya shigo cikin su Mas'ood su nema miki magani”.

     Da sauri Zinneerah tace, “Granny yama daina ai, bara naje wajensu Bahijja”

    Kafin Hajiya Iya tace wani abu harta nufi hanya da sauri. Tana gab da fita yace, “Zonan”.

        Tamkar ta fasa ihu taji. babu yanda ta iya dole ta dawo kanta a ƙasa. Batare da shima ya ɗago daga latsa wayar da yakeba yace, “Ki ɗauka min lap-top a ɗaki da abinda kika kai ɗazun”.

         Amsa masa tai da to tana fita cika umarninsa. Harga ALLAH yana burgeta saboda baida hargowa. Banda ɗazun bata taɓa ganin yayi faɗaba ko tsawa ma wani a gidan. Shi dai kawai baida sakewane, idan kaga fuskarsa a sake yana tare da Yah Khalipha ne ko Hajiya Iya. A zatonta yanda yasan ita ba komai bace a gidan face mai cin arziƙinsu zaita karta mata wulaƙancine. Amma sai taga saɓanin hakan.

     Da wannan tunanin ta ɗakko duk abinda ya sakata ta dawo ɗakin. Magana ta samu yanayi da Hajiya iya. Amma ko a cikin ɗakin kake da wahala ka jisa. 

      Wani shayin ta sake zuba masa zata saka suga uku yace, “two is ok”.

    Maida ɗaya tay ta saka masa biyun, daga haka ta ɗauki ƙaramin hijjab ɗinta da waya ta fice ta barsu

 

      koda taje sashensu Bahijja da suka tambayeta labarin yanda ta ƙare da kai shayi catai musu ai babu abinda ya faru, dama takai masa shayin yana wanka ajiyewa kawai tayi ta fito abinta. Mararta ke mata ciwo kaɗan-kaɗan shiyyasa taje ɗaki ta kwanta ganin sun fito.

       Meenal tace, “Yo tsoro mukaji kar wani abu ya faru yazo ya haɗa damu. dan laifinmu sai yafi naki. cazaiyi mune bamu nuna mikiba yasin”.

     Ƙaramar dariya kawai Zinneerah tai ta zame ta kwanta. Daga haka suka cigaba da hirarsu. Daga ƙarshe ranar anan ta kwana abinta.

 

_____________________

 

    *DANYA*

 

     Ta daɗe kwance tana maida numfashin gajiya dana yunwa daya jigatata. Kafin ta miƙe dan ɗan kunun da tasha ya taimaketa. Ledar data shigo da ita ta jawo, ta buɗe tana fiddo kayan da malam ya haɗa mata da ƙara bitarsu yanda bazata mantaba. Baki ta washe na farin ciki tunawa da baba ya kusa dawowa gareta. Ta ɗaga wata ƴar kwalbar turare tana jujjuyawa.

        “Yanda ka bani wahala akan ƴarka Sule, sai na sakaka mantawa da ita na har abada acikin jerin ƴaƴanka. Duk dukiyata data salwanta dan ganin ka dawo saina fansheta a jikinka ko sisi bazanyi asaraba. Ƴan uwanka kuwa dake aibantani a gari cewar ta sanadina kabar Danya zan koyar dasu hankali a sannu, duk sai kunsan kunyi da Asabe wlhy”. Ta ajiye kwalbar tana cigana da dariyarta. Maida komai tai a ledar bayan ta ɗauka wasu layu guda biyu ta fice a ɗakin.

        Inda murhun girkinsu yake ta nufo. kasancewar jiyama ba girki sukai a gidanba yasa ta turbuɗa hannunta tsakkiyar tokar hankali kwance ta fara tonawa. Sai da ta ƙwakule tokar duka tasa icce ta fara tona ƙasar sannan ta saka layun nan guda biyu ta maida ƙasar da tokar ta rufesu ruf tamkar komai bai faruba. Duk da basu da isashen hatsin yin tuwon dare a gidan haka ta tattare ɗan wanda Yaya gajeje ta kawo musu daya rage ta wanke ta fita kai niƙa da kanta. Tasan ko jiran Tinene tace zatayi tayi a banza, baizama lallaima ta sake ganinta gidan a yanzuba kuma.

 

       Da ƙyar ta samu Malam Mati yay mata niƙan akan bashi zata kawo masa kuɗin. Rai ɓace ta baro injin saboda yarfin da malam mati ɗin yay mata a gaban yara. Tai ƙwafa kawai da ayyana rashin mutuncin da zatai masa shima.

         Sa'a ta iske a gidan tana shara, da alama ganin gidan datai kaca-kaca yasata takaici tana shigowa tahau aikinsa. “Sannu innarmu. Tun ɗazu nazo ai gida babu kowa ga ko ina kaca-kaca kamar ba mutane ke rayuwaba. Shiyyasa na hau aikin nan”.

        Baki innar ta taɓe tana ajiye ƙwaryar da tayo niƙan dawa a ciki. “Kin san dai Tinene ba moriya takesoba, ke kuma tunda kin zaɓi dangin ubanki sama dani wazai gyara mani”.

        “Kiyi haƙuri dan ALLAH Innarmu”.

     Banza tai mata. saima ƙoƙarin fara haɗa wuta a murhun data saka layun nan ta farayi, itama Sa'a sai ta cigaba da sharar tsakar gidan ranta duk babu daɗin. Bayan ta gama sharar ta tattara duka kwanika ta hau wanke-wanke da ruwan data fita ta roƙo a maƙwaftansu dan gidan ko ruwa babu. Itama Inna shita samu ta ɗiba tasa ruwan tuwo. Tsaf ta gama wanke-wanken shima ta ɗauki botiki ta fita dan dama ta gyaro ɗakunan.

       Sa'a na fita Inna ta miƙe ta ɗakko sauran kayan da malam ya bata ta ƙarasa yin yadda yace, sannan ta cigaba da hidimar girka tuwonta.

       Haka Sa'a taita kai kawon ɗibar ruwa har sai da ta cika ko ina na gidan sannan tai zaman hutawa. Sai a lokacin Tinene ta dawo gidan niƙi-niƙi da ledar kayan ƙwalam da maƙulashe. Yanda tayi tamkar bataga Sa'a bane ya bata haushi tahau zaginta, a take suka harƙume faɗa. Inna najinsu da kallonsu taƙi ta tanka sai da ta gaji da hayaniyarsu ta kora Sa'a wai ta tashi ta koma inda ta fito ita batason fitina.

       Da haushi Sa'a taja hijjabinta ta fice a gidan tana sharar hawaye......

 

__________________________

 

*_SHIRA'S FAMILY_*

 

         Washe gari a bazata suka tashi da baƙuncin matar Yah Adnan. Lokacin duk suna dining suna karyawa saboda masu fita makaranta. Sai dai shi bandashi, amma yana zaune a falon shi da Khalipha suna magana akan wasu takardu dake baje a centre table ɗin falon, shi yanata danna lap-top Khalipha na gefensa yana masa magana da takarda ɗaya a hannunsa.

     Kasancewarsa a falon yasa babu yawan hayaniyarsu, dan Baffah ma bayanan yayi tafiya tun shekaran jiya. Iyakar sune kawai a falon suna taya Zinneerah murnar wayarta kowa na ƙoƙarin saka mata Number ɗinsa.

       Hajiya iya ce ta fito daga kitchen ɗin ita da baba Rahi tana faɗin, “Oh ALLAHU ni Amina. Yanzu dan ALLAH zaman latsa wayoyi zakuyi ko karin kuyi ku tafi makaranta. Sai kuma kun makara ku ishi mutane da mitar an saku makara”.

      Alamar roƙon tayi shiru suke mata wai dan kar Yayansu yaji. Basu sanma duk abinda suke tun ɗazun yana jiyosun ba. Ya sharesune kawai saboda aikin dake gabansa mai matuƙar muhimmanci ne. Suna fidda kuɗaɗen da zasuyi ginin company shinkafa ne da waken suya. Shiyyasa tun jiya yake busy. Da niyyar yin noman shinkafar kawai yazo Nigeria, sai dai Dr Mahmud da Khalipha sun canja masa tunani da shawarar mizai hana ya buɗe company kawai tunda dai yanzu Alhmdllh noma ya fara farfaɗowa a arewan. Ya yarda da Dr Mahmud sosai, dan ya jima yana bashi shawara tai masa amfani kuma, Shiyyasa ya amince babu wani ja'inja ya fara shirye-shiye. hakama Khalipha na hannun damarsane, akwai shaƙuwa mai ƙarfi a tsakaninsu kasancewarsa mutum maison ƴan uwansa. Kosu sauran yaran gidan gama fahimtarsane kawai basu yiba, shiyyasa suke nuna tsoronsa da ganin tsaurinsa a garesu, dan da shima Khalipha hakanne a tsakaninsu, sai a ɗan zaman da yake tare da shi yanzu London ya fahimci yayansu mutumne mai sauƙin kai da haƙuri, sakewace dai kawai baida ita ga mutane sai wanda yaso. A yanzu haka suna kan yin cinikin wani fili ne da za'a fara ginin company ɗin.

       A fusace Hajiya Iya tace, “Anƙi ai shirun dan ubanku”.

     Bakuna suka shiga turawa gaba, dan duk ɗinsu sukanji haushi idan ta zagar musu iyaye. Yanda sukayinne ya sata hararsu ta koma kitchen.

      Baki Ni'ima ta buɗe baki zatai magana ƙarar takun takalma masu azabar tsini suka katseta. Su dukansu ƙofar suka zubama idanu banda shi da yayma wajen kallo guda ya maida kansa ga aikinsa duk da baisan wanene ba.

       “Hii Guys!!”. Ta faɗa dai-dai tana shigowa cikin falon.

      Duk idanu suka waro waje na mamakin ganinta matuƙa, dan badan ma akwai hotunan bikinta da Yayansu a gidanba, babu yanda za'ai su iya ganeta. Cikin ƙarfin hali Khalipha ya miƙe yana murmushi da faɗin, “Woow Aunty Farah Surprise Kece tafe haka?”.

         Ɗan yatsine fuska tai tana wani yarfar da hannu gefe da juya idanunta manya masha ALLAH, “Oh ko bakuyi murnar ganinaba na koma?”. Tai maganar tana kafe Khalipha daya nufeta da ido. Amsar handbag ɗinta yayi da cewa, “No. no auntynmu, taya zamu ƙiyin murnar ganinki bayan duk gidanan ƙishirwar ganinki sukeyi daman”.

      “Oh nice”.

  Ta faɗa cike da yanga tana sauke idanunta kan mai gayya mai aiki da yay mata kallo guda tun shigowarta ya maida kansa. Inda yake ta nufa cikin takunta na izza da tsantsar gayu da yanga mai gauraye da wayewa. “I miss you my hero”. Ta faɗa tana kaiwa duƙe ta sumbaci gefen fuskarsa na dama. Tare da nufar bakinsa da ware duka hannayenta zata rungumesa............

 

*_Wa yaga ƙawar su aunty Shahudah ƴar turawa😜😂😂_*

 

 

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

 

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

 

*_ AL-ƘIBLA_*💘

 

*_ MADUBIN ZUCIYA_*💖

 

*_ DALAAL_*💝

 

*_ UBAYD MALEEK_*💓

 

*_ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

 

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

 

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

 

Kamar haka👇🏻💃🏻

 

Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700

 

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

 

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

 

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

 

*_08085405215_*

 

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

 

  0903 234 5899

 

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

 

*_ALLAH ka gafarma iyayenmu🙏🏻😭_*     

 

 

*_TYPING📲_*

 

 

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

 

 

 

*Page 23*

 

______________________

 

_*YERWA INCENSE & MORE**_

_(The scents with diff essence for YOU& your HOME)_

 

_(MASARAUTAR KAMSHI)_

 

_Ina masu neman kayayyakin kamshi yan nahiyar ketaran chadi da Senegal? Kai harma da ingataccen had’i yan bornu? To ku matso domin nesa tazo kusa..._

 

_YERWA INCENSE & MORE: Sun zo muku da kayayyakin turaruka kamar haka:_

 

_Khumra kowacce Iri._

_Turarukan Wuta_

_Mopping khumrah_

_Washing khumrah_

_Bathing khumrah_

_body mist_

_kullaccam_

_scented hair cream/spray_

_wardrobe balls_

 

_carpet spray_

_air-fresheners_

_scented pebbles_

_body sprays_

_oil perfumes_

_Perfumes_

 

_kabbasa_

_burners_

_coal igniter_

_tong_

_kasko_

_kujerar tsugunno_

_english coal_

_dilke&halwa set_

_scented body mist_

 

_kai dama sauran kayayyakin da bamu ambata ba, YERWA INCENSE AND MORE, Na tura kayayyakin su ko’ina a fadin Nigeria da ketare. Domin tuntubar su. Suna instagram: _@yerwaincense_and_more. Ko _Facebook site:YERWA _COLLECTIONs. Ko a duba su ta number su: ___08095215215/09044191709! _

 

_suna bada kayan su kan sari ko sayi dai-‘dai_

 

_______________________

 

 

*Page 23*

 

...........Mamakinta ya sakashi ɗago manyan idanunsa ya zubasu cikin nata. Ɗunbin al'ajabin sabon salon nata na bayyaya ƙuru-ƙuru a cikinsu. Dan wannan salon iskancin tabbas ba nata bane aroshi tayi saboda wani dalilinta.

         Itama ganin yanda ya zuba mata idanunne yasa gwuyawunta yin sanyi, ta sakar masa Murmushin ƙarfin hali da cije leɓenta na ƙasa tana janye jikinta baya.

          Duk da yaji ɓacin ran ganin nata bayan ya gargaɗeta jiya da daddare akan kar tazo amma tay watsi da maganar tasa tazo, ga kuma salon isanci data shigo dashi gidan alhalin hakan ba ɗabi'arta baceba sai ya basar ya sakar mata wani lallausan murmushi daya sata sauke ajiyar zuciya babu shiri.

     Su Saifudden kam dake dining jin shiru ya sakasu ɗagowa daga duƙar da kawunansu da sukayi, ganin  abinda sukai tunanin zatayi bashi ya faruba duk sai suka saki numfashi. Musamman da suka hangota zaune a gefensa suna kallon juna da murmushi kamar ba yayansu ba. Itama kuma kamar ba itace ta shigo da salon rawar kai ba yanzun. Ta koma Farah ɗinta da suka sani mai tsanin miskilanci a garesu da jan aji.

       Cikin magana ƙasa-ƙasa da babu wanda yake iya jiyosa. Dan saima ka ɗauka wani magana mai daɗin gaske yake faɗa mata, yace, “Wannan salon bai dace da ke ba, kowaye ya baki shawarar shigowa cikin shirawa dashi ya ɗoraki a kan keken ɓera da ta zubewar mutuncikine, da sakaki a layin masu ƙarancin tarbiyya”.

           Shiru kawai tai tana kallosa cikin ido, tabbas gaskiya ya faɗa mata, dan ita kanta yanda ƙannensa duk suka zubo mata ido sanda ta shigo sai taji kamar ta muzanta a cikin idanunsu.. Dama da ƙyar ta iya dauriyar hawa kan shawarar auntynta da tace ta shigo musu gidan a salon gatse-gatse zasuji shakkarta fiye da da da take musu isa da shariya kawai. Kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta ɗago tana kallon sashen dining ɗin.

       Ganin duk yanda sukai ƙasa da kawunansu yasa ta wani yatsine fuska tana taɓe baki, dubanta ta maida ga Yah Adnan daya sake maida hankalinsa ga aikinsa. “Baby ku baku iya tarbar baƙo bane da masauki a gidan naku?”. Tai maganar a Farah ɗinta daya sani mai tsananin son nuna isa da miskilanci.

      Cak ya tsaya daga danna keyboard ɗin da yakeyi. Sai dai bai ɗago ya kalletaba. Kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa yay wani guntun murmushi na takaici ya cigaba da abinda yakeyi batare daya tanka mataba.

       Ganin zata ƙara magana Khalipha yay saurin tareta da faɗin, “Sorry Aunty. muko muka iya tarar baƙi. Amma muje ki gaisa da Granny first”.

      “Oh no Khalipha, zan fara wanka kafin na iya gaisuwa-gaisuwa ɗin nan naku da baya ƙarewa”.

           Saurin girgiza mata kai Khalipha yay yana nuna mata Yayansu da ido, dan yasan hakan da zatai ba ƙaramin kuskure bane duk da yasan itama ta sani, tunda tafi kowa sanin halin Yayan nasu ai.......

       “Kai lafiya na ganku cirko-cirko?”.

Hajiya iya dake fitowa daga ɗakinta ta faɗa batare da hankalinta yakai ga Farah ba. Kafin wani ya samu damar bata amsa Farah ta miƙe tsam cikin komawa ainahin takunta ta nufi hajiya iyan. Idanu Hajiya iya ta zuba mata harta ƙaraso gareta dan ta ganeta sarai duk da zuwanta gidan uku ne kacal, kuma duk kwananta bibbiyu ta koma

        “Granny barka da safiya” ta faɗa tana ɗan kai jikinta ga hajiya iyan ta rungumota kamar yanda larabawa keyi. Duk da abun yazo banbarakwai Hajiya Iya bata damuba. Dan tasan akwai banbancin al'adu da yanki a tsakaninsu, kuma ko wancan zuwan da tayiyyi haka ta dinga mata gaisuwa, shiyyasa takemata uziri idan tayi wani abun. Hannu biyu ta karɓeta tana sake faɗaɗa murmushinta. Kafin ta ɗagota tana faɗin, “Uhm lallai yau munada manyan baƙi ashe”.

       Murmushi Farah tayi cikin  basarwa, dan tanajin hausa ras yine saita gadama take, tafi yin larabcin ƴan Morocco da turanci.

           Sai a yanzu suma yaran gidan suka fara gaidata, duk da mamakin a yanda ta shigo gidan ɗazun ya kasa barinsu. Binsu kawai take da kallo tana amsa musu a yatsine. Kowa ta gane a cikinsu tunda tanada hotunansu na biki, duk da sanda akai auren nasu su Meenal basu da wayo sosai, amma tana jin hirarsu bakin Khalipha koshi uban gayyar idan yaso, musamman idan ƙanwarsa tana tare dashi.

       Kafe Zinneerah dake can ƙarshe tai da idanu, kamar zatai magana sai kuma ta basar abinta ta maida kallonta ga Khalipha da Hajiya Iya ke masa magana ya rakata ɗakin Moddibo ta huta.

        Da to ya amsama hajiya iyan.

Shi dai oga na zaune har yanzu yana aikinsa kamarma ya manta dasu a falon, sai da Hajiya iya ta zauna a kusa dashi sannan ya ɗago ya kalleta. Ganin yanda launin idonsa ya canjane ya sata sakin murmushi ta shafa fuskarsa.

       “Babba da haƙuri aka sanshi, tunda ta kawo kanta karka wani saka damuwar hakan a ranka. Mu dama ai burinmu ta dinga shiga cikinmu a koda yaushe. Ba daɗin nisantarmu da kuke mukejiba”.

        “Amma Granny sau nawa nake cemata tazo domin gaisheku tace batason zuwa. Sai yanzu dan son fitina. Wai kinmaga a yanda ta shigo gidannan da farko ma kuwa?.......”

        “Shiii! ya isa, koma dai a wane dalili tazo ko ta shigo kai ka ɗaukesa ƙyaƙyƙyawa a ranka, ka kuma ɗauki ɗamarar canjata yanda kakeso duk da kayi sakaci tun farko, amma lokaci bai ƙure makaba”.

     Huci ya ɗan furzar kawai yana jingina da kujera da lumshe idanunsa.

    

    Sudai su Zinneerah da bajin mi su Hajiya iyan ke faɗaba sauri-sauri duk suka kammala cin abincinsu suka miƙe dan suna neman makara. Ɗakin hajiya iya ta nufa ɗakko school bag ɗinta, lokacin data fito su Yah Moos'ab duk sun fice, harsu Jamal ma. Da alama ita kaɗaice ta rage. Sau ɗaya ta kalli sashen da yake zaune har yanzu yanata faman aiki a lap-top, shi kaɗai ne a falon yanzun. Hajiya iya ta tashi zuwa kitchen saka su Baba Rahi haɗama Farah breakfast tare da Khalipha dake nuna musu yanda zasuyi.

    Sum-sum ta wucesa a tunaninta baya ganinta saboda aikin da yake kamar ya kwashe dukan hankalinsa.

      “Zonan”.

Ta tsinkayi muryarsa cikin kunnenta a bazata. A lokaci guda ƴan cikinta da jinin jikinta suka yamutsa na tsoro, tuna maganar su Jamal da sukace baya maimaita magana idan yay maka yasata nufosa. Zinneerah yarinyace mai tarin nutsuwa, sam bata da garaje akan komai, hakan yasa ko tafiya takeyi saika ɗauka yangace. sai dai sam ba haka bane, halittartace hakan. Komai nata cikin sanyi da nutsuwa bana sakarciba ko rawar kai.

       Gabansa takai tsugunne kanta a ƙasa tana faɗin, “Yayanmu gani”.

       Batare daya ɗago daga abinda yakeba, a daƙile yace, “Ɗiba tissue ki kwashe wannan jambakin”.

        Ɗagowa tai babu shiri ta kallesa tare da waro manyan idanunta masu tsananin haske, cikin suɓucewar baki tace, “Iyeee Yayanmu miye laifinsa? Malaman basa faɗa f.....”

       Sai kuma tai saurin ɗora hannunta a baki saboda tuna a ida take.

      A karan farko yaɗan ɗago ya dubeta, hararar data saka kayan cikinta sake hautsunawa ya wulla mata tare da maida kansa ga aikinsa. Da sauri takai hannu ta cira tissue ɗin dake a centre table ta kaisa kan bakinta ta kwashe pink lipstick ɗin da yay mata ƙyau sosai tana ƙoƙarin haɗiye ƙwallarta. Cikin ɗan rawar murya tace, “Na kwashe”. Yanzun ma batare daya ɗagoba yay mata nuni da hannu alamar taje.

     Tana miƙewa Hajiya iya na fitowa da ga kitchen, tabi Zinneerah ɗin da kallo. “Inno lafiya baku tafi bane?”.

      Ɗan juyowa Zinneerah tayi kanta a ƙasa tace, “Eh Granny yanzu zamu tafi”. Daga haka ta fice da sauri kafin hajiya iya ta sake cewa wani abu. Duban inda yake zaune Hajiya iya da zuciyarta ke ayyana mata ba lafiyaba tayi, “Moddibo mike faruwane da Inno, ko wani abu akai mata?”.

        “Waye haka?”. Ya faɗa yana ɗan ɗagowa ya dubeta. Harara ta zabga masa tana kaiwa zaune. “Kaifa wulaƙancinka yawane dashi Moddibo, ita Zinneerah ɗince baka saniba ko yau na fara kiranta Inno a gabanka?”.

      Ɗan murmushi yayi hankalinsa a aikinsa, a taƙaice yace, “ALLAH ya baki haƙuri”. Daga haka yaja bakinsa ya tsuke batare daya amsa mata maganar farko ba.

       Ƙwafa tayi ta miƙe da sauri ta nufito ƙofar fita danta leƙa. tana fitowa maigadi na rufe gate alamar su Zinneerah sun wuce. Dawowa tai ranta daɗan damuwar ALLAH yasa ba wanine yayma Zinneerah ɗin wani abuba mara daɗi. Koda ta dawo falon bata kulashi ba saima harar inda yake da tayi ta shige ɗakinta abinta.

       Murmushi yayi a karo na biyu yana girgiza kansa. dan yaga hararar da Hajiya iyan tai masa. Ajiye lap-top ɗin yayi zai miƙe Khalipha ya fito ɗauke da tire. Yaɗan bisa da kallo harya ƙaraso inda yake. “Yayanmu ga abincin Aunty”.

     Kauda kansa yayi yana ƙarasa miƙewa. Sai da ya raɓa Khaliphan zai wuce sannan ya bashi amsa da, “Ka ajiye mata anan mana ta fito taci inma zatacin”.

       Sanin abinda Yayan nasu ke nufi ya sakashi yin ƙaramar dariya, ganin zai shige yace, “To kaima ai baka karya ba”.

       “Karka damu Besty yau ina azumine”. Ya bama Khalipha amsa yana shigewa corridor ɗin ɗakin nasa.

 

         Zaune a bakin gado ya iske Farah ɗaure da towel nashi ajiki alamar wanka tayo. Sallamarsa ta sakata saurin zare wayar dake a kunnenta ta ajiye alamar magana takeyi da wani, kuma bataso yaji. Wayar yaɗan kalla tamkar zaiyi magana sai kuma ya fasa.

        Cike da basarwa itama ta miƙe duk da tasan ya fahimci waya take ya basar dan shi mutum ne mai lura. Sai dai bai zama lallai ya nuna makan ya fahimtaba sai yaso.

           Ganin yanda ta ciskule fuska cike da isar tata shima sai ya basar da ita ya nufi wadrobe zai dauka abu. Bayansa ta harara da miƙewa sanin idan miskilancine ya fita iyawa. Rungumesa tai ta baya tana jero masa kalaman kewarsa da tayi a kwanakin nan da basa tare. Komai bai ceba sai janyeta a jikinsa da yayi. Tabbas yana son Farah fiye da hasashen mai tunani. Dan duk inda mace takai ƙyaƙyƙyawar Farah takai, a zaman takewarsu tana ƙoƙarin ganin ta ƙyautata masa da faranta masa. matsala ɗaya ce ke cimasa tuwo a ƙwarya game da ita zuwa uku. Na farko shine ƙin danginsa. Sai dai yasan wannan training ɗin su Mammah ne, dan mafi yawan rayuwarta a hannunta tayi. Shiyyasa yakan mata uziri da hakan da ƙoƙarin ganin ya canjata. Sai kuma shegen kishinta da sam ta tsani taga wata mace ta raɓesa koda a wayane, ga ɗan banzan zargi daya tabbatar duk kishinne yake kawo matashi. Na uku son isa da nuna gadara a dole ita isashshiyace ƴar masu mulki.

      Zaune yakai saman sofa yana lumshe idanu. Da wannan damar tazo ta zauna a cinyarsa tana ɓata fuska da faɗin, “Wai kana nufin fushi kake dani? Bayan nice ya kamata nai fushi da kai Yah Mutallab”.

      Banza yay mata kamar bazai tankaba, sai da yaji ta fara masa murje-murje a jiki cike da salo ya buɗe idanunsa da sauri. “Kinga tasarmin a jiki azumi nakeyi”.

      “Azumi kuma? Nami to?”.

“Ina ruwanki da ko namiye?”. Ya faɗa yana tureta.

       Kallonsa tayi da ƙyau idanunta na kawo ruwan hawaye dan tanada saurin kuka dama. Muryarta na rawa tace, “Dan nazo gidanku zakaimin wulaƙanci?”.

         “Anmiki wulaƙancin, ni bance karkiyi abuba amma kikayi saboda kin rainani yanzu kina ganina dai-dai dake ko? Sannan tsabar iskanci wai gidanmu zaki shigo da wani salon sakarci, yanzu da Hajiya iya ko Baffah wani na falon kika shigo ɗin nan mi zasuyi tunanin kin koma kuma?”.

       A take jikinta yayi sanyi, hawaye na rige-rige sake zubowa. Kamar baza tayi maganaba sai kuma mita tuna oho mata ta kallesa da sakin ƙaramin murmushi tana share hawayenta. “Kayi haƙuri nayi kuskure, kuma daka tabbatar min hakan sai naji ban ƙyautaba, nima kuma salon bai dace dani ba sam. Amma maganar tahowa ba laifina bane har da su Mammah”.

       “Tunda su Mammah ɗin ke aurenki saiki kirasu ki sanar musu kin iso su nema miki wajen zama. dan ba zaki zauna a gidan nan ba. Lokacin da nake lallaɓaki kizo domin gaishesu matsayinsu na iyayena kai tsaye kike cemin bakison zuwa inda suke. To suma yanzu basa buƙatarki”.

        Ya ƙare maganar da miƙewa ya fice a ɗakin batare da ko waiwayenta ya sakeyiba.

       Bayansa ta raka da kallo idanunta na wani ƙankancewar bacin rai, ta cije baki zuciyarta na mata zugi da sakejin zargin jiya na dawo mata a rai sabo. Tabbas huɗubar aunty data hauce taso jamata wannan wulaƙancin nasa. Duk da dama bata isa tanƙwarashi ko juyasa yanda takeso ba tunda shima bauɗaɗɗen ne, dan ya fita zafin kai da shegen taurin kai tamkar shine jinin mulkin ma ba itamba.

        Tayi alƙawarin bazata ƙara kamanta irin kuskuren dataso tafkawa a yau ba nason kwatanta zubar da kimarta. Dan wani raɗaɗi takeji a zuciyarta idan ta tuna a yanda ta shogo gidan a dole ita wayayya. Bandama shirmen aunty data bata shawarar ba ita kuma ta hau ai ko ba'a faɗaba duk wanda ya ganta yasan wayayyace ita, bawai saita nunama duniyaba kodan jinin mulki dake yawo cikin jikinta da tarihinta.

           Taja ƙaramin tsaki da ɗauka waya ta kira Mammah, labarta mata duk yanda sukai yanzun tayi. Faɗa sosai Mammah keyi kafin ta yanke wayar domin nemansa.

       Itakuma sai ta juya akalar kiran ga auntynta. dan dama da ita suke waya ɗazun daya shigo, itama ta labarta mata komai daya faru da nuna mata gaskiya shawaran data bata na shigowa gidan a yanayin gatse-gatse baiyiba. Dan gashi hakan da tayi yaso taɓa mata kima har a idanunsa, balle ƙannensa da tasan suma kowa ya gumtsi gulma ne dan babu damar yi a gabanta ne ko shi Abdul-Mutallab ɗin dan tasan yanda suke shakkarsa a gidan.

       Itama dai auntyn tata kamar Mammah faɗan ta kamayi kamar Adnan ɗin ne a gabanta. Ta kumace ita ai batace tayi gatse-gatse a gabansu kamar wata sashasha ba ko mara tarbiyya, tadaice ta nuna musu banbancin da da yanzun kawai, daga haka ta yanke wayar itama ta koma neman Yah Adnan ɗin.

      Su dukansu daga can nemansa a waya suka shigayi, sai dai babu wanda ya iya samunsa dan cama ake musu switch off. Mammah tai ƙwafa dan tasan kashe wayar yayi tunda yasan tsiyar daya shuka.

 

         A falo kam a yanda ya fito ɗakin a fusace ya fice abinsa yasa Khalipha dake zaune yana karyawa fahimtar babu lafiya. Duk da dama dai ba wannan ne karon farkon daya fara ganin rikicin yayan nasu da matarsa ba. Duk da shi yayan nasu kan kauce faruwar hakan a gaban idonsa, amma da yake Farah mace ce mai nacin masifa da mita saita kaisa ƙarshe ya yaɓa mata maganar da zata koma rusar kuka. Dama kuma da yawan faɗan nasu ana yinsane akan zamansa gidansu nacan london ɗin, dan kullum zancenta baya wuce sai ya barmata gidanta ya koma hostel da zama.

 

      Hajiya iya na ɗaki tana gabatar da walha dan haka batasan wainar da ake toyawaba. Sai da ta idar ta fito ne ta iske shi da Khalipha ɗin duk basu a falon. Baba Rahi ma ta sake gyara falon tsaf sai tashin ƙamshi yake. A tunaninta yana ɗaki tare da matarsa yasa bata damuba ta koma ɗakin danta ɗan kwanta itama ta huta.

 

  

________________________

 

*_DANYA_*

 

    

       Yau a lissafi kwanaki bakwai kenan da bizne aikin Malam da Inna tayi, hakan yasa tun a daren jiya take zuba ido akan dawowar baba. Sai dai har garin ALLAH ya waye babu shi babu labarinsa. Bata damuba dan tasan akwai yau.

    Aiko yau ɗinma dai tunda gari ya waye idanunta basu huta da kallon ƙofa ba. Da taji an motsa ƙyauren gidan sai ta hau washe baki, sai kuma taga bashi ya shigoba saita haɗe fuska dajan tsaki. Kamar wasa tana zaune a bishiyar tsakar gidan har aka kira azhar. Maimakon ta tashi tai sallar sai ta cigaba da zama wai idan ya shigo ta haɗa duka tayo ai.

     Duk wannan zaman zuba ido da Inna keyi na dawowar Baba Tinene na a gidan tana wanki, ta ƙure waƙa a wayarta da inna bata taɓa tambayarta daga ina ta samotaba. Koda ta tambayi Innar zaman mi take ta sanar mata sai kawai ta hau dariyar shaƙiyanci tana faɗin, “Oh kice tsohon tsimin soyayya ne ya motsa Innarmu”.

     Banza Inna tai mata tunda tasan ba kunyace da Tinenen ba, yanzu saita yaɓa mata wata maganar. Haka ta cigaba da zama a wajen har akai sallar la'asar. Tinene data gama wankinta har tayi wanka tana kwashe kayan da alama fita zatayi a gidan. Buga ƙyauren gidan da akai da masifar ƙarfi ya sakasu dubar hanyar zauren a firgice su duka. 

      A bazata Karima ta shigo gidan jaye da akwati buju-buju da ita tamkar wadda aka ƙwato daga bakin kura. Babu shiri Tinene ta watsar da kayan hannunta ƙasa. Innama ta zabura kan Karimar dake tafiya kamar ma da tangaɗi.

      “Mi nake gani haka ni Asabe. Karima daga ina kike tahe da maraicen nan?”.

     Ina babu bakin amsawa daga Karima, sai ma zubewa datai a ƙasa cikin hakki tace, “Innarmu ku bani abinci yunwa nakeji”.

       Tinene dake tsaye tana kallonsu har yanzun tace, “Tab abu mai wahala anan gidan yanzu Yaya Karima, amma bara naga inada wazobia ko awarar gidan Rashida a samo miki idan bata ƙareba dan maraice yayi”.

     “Nagode auta. Inna bani ruwa”.

Ta sake faɗa tana kaiwa kwance da zare hijjabin jikinta gaba ɗaya ta jefar. Ruwan Inna ta ɗebo mata da sauri ta kawo mata, ta ɗagota daga kwancen da take danta bata sai a lokacin idanunta suka sauka akan sayin duka dake a wuyan Karima da damtsen hannunta ruɗu-ruɗu ga tsohon ciki. Duk da kasancewarta baƙa hakan bai hana fitar sayinba da ƙyau.

      “Na shiga uku ni Asabe waya maki wanga bugun haka ga ciki Karima? Badai sheɗanin yaron nanbane Babawo?”.

      Karima ta sake zamewa ta kwanta cikin tirɓayar jar ƙasar batare data bama Inna amsaba. Ganin Innar zata takura mata tace, “Inna ki barni dan ALLAH, ku bani abinci nide karna matu”.

      Kafin Inna ta samu bakin sake cewa wani abu Tinene ta shigo gidan ɗauke da farar leda da awara a ciki. Kwano ta dauka a wanke-wanke ta juye mata takai gabanta. Cikin rawar jiki Karima ta tashi zaune taja kwanon. Bibbiyu ta dinga haɗa awaran tana turawa a baki. Ganin tana neman shaƙewa Inna tai azamar bata ruwa ta sha. Koda ta cinye saita kuma zubewa tana sauke numfashi wani irin zufa na karyo mata ta ko ina duk da kuwa awaran bamai zafi baceba.

     Sudai suna tsaye shiru cirko-cirko kowanne da kalar tunaninsa akan wannan al'amari..........

      

      

      

 

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

 

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

 

*_ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_

 

*_ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_

 

*_ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_

 

*_ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_

 

*_ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_

 

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

 

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

 

Kamar haka👇🏻💃🏻

 

Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700

 

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

 

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

 

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

 

*_08085405215_*

 

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

 

  0903 234 5899

 

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

 

*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

 

*_TYPING📲_*

 

 

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

 

 

*Page 24*

 

_________________________

 

 

 

_RANO NET! RANO NET! RANO NET!_

 

_WHO NO LIKE BETA AWUUF THINGS?_

 

_IDAN KAJI GANGAMI DA LABARI....! INA MASU ZUBIN ADASHEN DA BA RANAR DAUKA NA DATA?_

 

_TO KU MARMATSO KUJI, KU KUMA SHARE HAWAYEN KU, MUNZO MUKU DA SABBIN TSARE TSARE NA DATA, WADDA KOWA ZAI IYA SAYA DAI DAI KARFIN SA. A FARASHI MAI RAHUSA_

 

_RANO NET! RANO NET! RANO NET!__

     _(Afford data at chikini price)_

         _MALLAKI DATA A KUDI KALILAN DA RANO NET_

 

_TSAYA KUJI, A RANO NET ZAKA IYA ZAMA RESELLER KO WHOLESALER KAI MA, EH ZAKA/KI IYA ZAMA MA SAYAR DA DATA A FARASHIN SARI MUKE BAYARWA, KAI/KI KAFA KASUWANCIN KU KUMA. DA KUDI KALILAN._

 

_MUNA KUMA SAYARWA AKAN ‘DAI DAYA, KOWANE NETWORK MUNA SAYARDA DATA PLAN DINSA AKAN KUDI KALILAN, MASU FARASHIN SARA KUWA MA KU KUDIN BAI KAI HAKA BAMA_

 

_AIRTEL_

_9MOBILE/ETISALAT_

_MTN_

_GLO_

 

_DUK MUNA SAYARDA TSARIN DATA DINSU. KAMAR MISALI MTN MUNA SAYARDA 1GB.24MB AKAN FARASHIN NERA 300 KUMA YANA KAIWA WATA DAYA, GWARGWADON YADDA KAKE AMFANI DA DATA, 2GB 600, 3GB 900!!_

 

_DUKA WADANNAN TSARIN DATA DAMA NA SAURAN LAYIKA MUNA SAYRWA AKAN FARASHI MAI RAHUSA, WANDA KOWA ZAI IYA YIN TSARIN DAI DAI ALJIHUN SA_

 

_Ranonet.com.ng_

_GA SITE DINMU NAN DAKE YANAR GIZO, KAI TSAYE ZAKI/KA IYA SIYAN NAKA TA NAN. _

 

_KO A TUNTUBE MU TA NAMBAR TARHON MU: +234 803 081 1300/+234 808 540 5215_

 

_KYAU, INGANCI, RAHUSA, ADADE ANA YAWO A YANAR GIZO SAI RANO NET._

 

_RANO NET..!!!!_

 

 

________________________

 

 

*Page 24*

 

...........Koda Farah ta gama surutan haushinta gado ta faɗa daga ita sai towel ɗin da tai wanka tai kwanciyarta batare data tuna ya kamata taje ta gaida matan gidanba. Barcinta tasha sosai kafin ta miƙe saboda shigar kiran salla a kunnenta dan bata da sakaci da ibada. Ruwa ta ƙara watsowa tayo alwalar salla.

      Koda ta fito ta gabatar da sallar kwalliya tayi dai-dai misali ta shirya cikin baƙar doguwar rigar jallabiya mai ƙyau, ɗan kwalin rigar ta naɗa a kanta yanda larabawa keyi dai.

       Farah ƙyaƙyƙyawa ce kamar yanda mijinta ya faɗa. Tanada jiki mai ƙyau ga kuma ilimi, matsalarta kawai itaɗin ƴar gatace ta gani kasheni, ƴar shagwaɓace bugun farko kuma jinin mulki. Dan itace auta a gidansu shiyyasa kowa sonta yake. Sannan ta girmane a Morocco hanun kakarsu dan a wajen haihuwarta mahaifiyarta ta rasu, daga bayane bayan rasuwar kakar tasu itama riƙonta ya dawo hannun Mammah duk da babbar yayarsu taso ita ta zauna a hannunta. Tana da son girman tsiya da miskilanci, dan koshi kansa oga kwata-kwatan yimasa isarta da taƙama takeyi. Sai dai shima da yake gwanine wajen iyawa duk da baɗan masu mulkin bane sai sukeyin dai-dai da juna harma ya kaita ƙasa ta risina tana mitar ya cika baƙin hali.

        Tana son Yah Abdull-Mutallab kamar yanda kowama yasan shima yana sonta. Sai dai tanada matsalar tsananin kishi, wanda da alama ta gadane wajen su Mammah. Dan ita kanta Mammah ɗin ta rabu da Baffah ne saboda kalmar ƙara auren nan daya furta gareta duk da ɗunbin son da take masa har yanzu. Dan ko aure taƙi sakeyi.

      Bayan ta shirya ta feshe jikinta da turarenta masu shegen ƙamshi da ɗaukar hankalin mai shaƙa ta fito. A falo ta sami Khalipha daya shigo zaune yana lunch. Ta ƙarasa inda yake taja kujerar dining ɗin ta zauna itama. Duk da ya girmeta shine ya fara gaidata dan yasanta da son girman tsiya. Babuko kunya ta amsa masa kuwa tana buɗe kulolin dake dining ɗin.

       Yanda take yatsina fuskarta ne ya tabbatarma Khalipha komai bai mataba a wajen. Dan haka yay ɗan murmushi da fadin, “Ki faɗa abinda kike son ci sai a sayo miki idan duk nanan basu mikiba”.

     Kanta tsaye kuwa ta shiga zayyano masa duk abinda takeson ci ɗin. Batare da damuwar komaiba kuwa ya miƙe ya fita dan dama ya kammala nasa cin abincin.

 

     Khalipha na fita babu jimawa su Zinneerah suka shigo gidan. Ita kaɗai ta shigo sashen na Granny cike da ƙarfin hali dan mararta ciwo take mata. Batare data lura da Farah dake zaune a dining tana latsa wayaba ta nufi ɗakin Hajiya iya.

    Farah da tun shigowar Zinneerah ita idanunta suka sauka gareta ta wani bita da kallo a yatsine tanajin rashin son yarinyar a ranta haka kawai. Sai dai kuma mamaki take ita wacece a gidan ma? Dan bata santaba a tarihi da labari. (To anya kuwa ƴar gidan nan ce?) ta ayyana a ranta gabanta na faɗuwa. Yunƙurawa tai ta miƙe zata bita ɗakin Hajiya iyan dan yanda Zinneerah ta wuce bata gaidataba sai abin yay mata zafi taga kamar rainine dan ta lura da yarinyar itama akwaita da nuna isa tun kallon datai mata ɗazun, sai kuma mita tuna oho mata ta koma ta zauna tana yin ƙwafa.

 

       Zinneerah kam da batasan tanayiba tana shiga suka gaisa da Hajiya Iya wanka ta shiga. Bayan fitowarta ta shirya cikin doguwar rigar boyal less da yay mata ƙyau ɗas a jiki, dan ɗinkin ya zauna da ƙyau masha ALLAH. Tayin abinci hajiya iya tai mata. Amma sai tace ta ƙoshi sai anjima. Basu jima da cin abinciba a makaranta. Daga haka ta kwanta a sofa sai barci.

       Barci tayi sosai, dan bata farkaba sai bayan sallar la'asar da Hajiya Iya ta tadata. Toilet ta shiga ta ɗan gyara jikinta ta fita zuwa falo cin abinci. Yanzu kam mafi yawan yaran gidan sun dawo. duk suna ma a falo zaune suna hira har Granny. Sai matar yayansu baƙuwar ɗazun dake zaune gefe ta haɗe fuska tamau kamar tanajin warinsu.

    Cikin ƙarfin hali tai mata barka da yamma. Batare da sauraren amsartaba ta gitta zata wuce saita dakatar da ita. Juyowa Zinneerah tai gareta fuskarta ɗauke daɗan murmushi. A ɗage sosai Farah dake ƙarema Zinneerah kallon sama da ƙasa tace, “Kema anan gidan kike?”.

      Kai Zinneerah ta ɗan jinjina mata kawai batare datace kimaiba.

    “Uhyim! Amma ban sankiba ni”.

Kallonta Zinneerah tai cikin ido kamar zatai magana sai kuma tai shiru fara'ar fuskarta na raguwa. Dan tsaf ta fahimci dizgata matar Yayan nasu da taji suna kira da Aunty Farah ke neman yi. Itama Farah ɗin da har yanzu ke mata kallon wulaƙanci da isa duk da kuwa babu wani abin kushewa tattare da Zinneerah ɗin, dan duk da take ƙyaƙyƙyawa babbar yarinya babu abinda zata nunama Zinneerah, itama idan dirin jikinne ALLAH ya bata, musamman ma yanzu da take a kan ganiyarta na kammaluwar sirrikan budurci, sannan jikinta a mulmule yake dan ba siririya bace bakamar Farah ɗin. Ga fatarta kalar ɗaukar hankali gamai kallo. ta buɗe baki zatai magana Hajiya iya ta katseta dan dama ta saka musu idone taga mi Farah ɗin zatayi.

       “Tunda ba zuwa cikinmu kikeba ta yaya zakisan kowa. Ke Zinneerah wuce kici abinci”.

     Sum-sum Zinneerah ta wuce dining tana ƙoƙarin maida duk wani ɓacin ran Aunty Farah ɗin daya fara yunƙuro mata. Dan a rayuwa ta tsani wulaƙanci da raini da disgi a rayuwarta. Zata iya jure komai banda waɗannan abubuwan.

     Sosai su Jamal sukaji daɗin abinda Hajiya tayi, itako Farah a fusace ta miƙe tabar falon zuwa ɗakin mijinta. Yi hajiya iya tai kamarma bata ganiba. Ta kuma haɗe fuska dan karma wani a cikin yaran yace wani abu. Daga hakama hirar ta watse. Dan barin falon itama Hajiya iya tayi.

 

         Kusan 6 Zinneerah da tuni suka fice suna can harabar gidan anata hira ta shigo sashen hajiya iya saboda matsa mata da mararta tayi. Bedroom ta nufa inda ta iske hajiya iya na waya. Sai da ta kammala ta dubeta tana ajiye wayar data gama ɗin.  “Fitinar Moddibo dabance wlhy. Inno dubamin ko su Rahi sun wuce?”.

       “Lah Granny ai sun tafi, bakuyi sallama bane?”.

     “Munyi sallama. Na zata basukai ga tafiyar banebam wannan fitinatunne yay kirana yanzu, wai ashe azumi yakeyi amma bai faɗaba tun ɗazu ba sai yanzu. Kuma wai abinci yakeson a haɗa masa. Gashi su Rahi ba tuwo sukaiba yau”.

      Cikin ƙarfin hali Zinneerah tace, “Granny yaya za'ai yanzu to?”.

         “Nima ban saniba to Zinneerah, sai dai ko ke zaki shiga kitchen ɗin ki haɗa masa tunda waccan malalaciyar matar tasa na tabbata ƙila ko shayi bata iya dafawaba balle wani tuwo”.

     Idanu Zinneerah taɗan waro waje da faɗin, “Kai Granny nikuma? Ta ina zai iya cin jagwalgwalona”.

      “Ci kuwa zaiyi harda santi Inno na. Kinga tashima kije kar ya dawo ya samu ba'ayiba ya fara baƙar zuciya danshi baya wasa da cikinsa. Tuwon zaki masa da ɗan wani abun mai sauƙi tunda azumi yakeyi”.

       Zata ƙara magana Hajiya Iya ta girgiza mata kanta. “Kinga babu abinda zai faru, lafiya lau zakiyi insha ALLAH kinji ƴar albarka. nina ai dana idar da sallar magrib zanzo nama tayaki muyi tare”.

    Jin abinda Hajiya Iyan ta faɗa ya sata miƙewa tana fadin to ta fice zuwa kitchen da kwarin gwiwarta. Sai da ta fara karanto addu'ar nasara kafin ta ɗauraye tukunya tasa ruwan tuwo dai-dai misali, dan itama dai tana ganin tuwon zataɗanci ko zataji sassaucin ciwon marar nan da taketa dannewa dan karta tadama hajiya Iya hankali.

      Cikin ƙanƙanin lokaci ta kammala tuwon semo.. data bama nutsuwa sosai gudun yimasa kuskure, sai da ta kammala kwashewa zuciyarta keta ƙara ƙarfafata akan miyar da taketa tunanin masa tunda ta fara tuwon. Ɗanyen kifi ta cira ta gyara tasashi a wuta da kayan ƙamshi da albasa dan rage masa ƙarni. Kafin ta koma ta ɗiba kayan miya zallar attarigu da tattasai sai albasa da tumatur guda biyu kacal ta wankesu suma tasa a blender da ɗan ruwa bamai yawaba can tai musu markaɗe ɗaya da yay kamar jajjage amma yaɗara jajjagen laushi kaɗan. Kifin ta sauke ta tsamesa a ruwan ta buɗesa ta cire ƙayarsa duka ta farfasashi, ta ƙara ɗora tukunya tasa manja a wuta ta zuba wannan fasashshen kifin da albasa da magi ƙwara ɗaya ta rage wutar can ƙasa. Sallamar hajiya iyace ta sakata juyawa tana kallonta. Ta ƙaraso cikin kitchen ɗin tana magana cike da tsokana. “Wai wai, anya kuwa yau kunnen moddibo bazai kai ƙasaba Inno. Irin wannan ƙamshi haka da aka cika mana gida”.

     Dariya Zinneerah tai tana faɗin. “Kai Granny bammafa fara miyanba”.

       “Amma kuma ga ƙamshi ya cika ko ina”  Hajiya iya ta faɗa tana buɗe tukunyar data saka kifin nan dake fidda ƙamshi mai daɗi a cikin manja. “Masha ALLAH miyar mi zakiyi?”.

       “Granny ɗanyen kalkashin nan dana gani da zanyi”.

       “Eh lallai kinyi tunani mai ƙyau, dama ɗazun Rahi tazo dashi wai ko zamuyi amfani dashi a gidanta suke ɗan shukashi”.

     “Aiko gashi yayi ƙyan fita Granny. shiyyasama ya birgeni. Kuma ta taimaka ta tsinkesa tun daga can yankawa kawai zanyi yanzu nasa a wuta”.

      “To bara na tayaki yankawa saiki haɗa miyar”.

    Babu musu ta bama Hajiya iyan, tunda dama tanason ɗan haɗa masa ko fruit salad ne haka da ɗan coconut juice idan zata iya. Ganin kifin ya mata yanda takeso ta zuba kayan miyarta a ciki da daddawa ta ƙara rufewa. Inda suke ajiye kayan fruit taje ta ɗauka komai dai-dai misali ta ajiye gefe, ta ɗauka kwakwa ta fasata itama ta ajiye gefe. Komawa tai ga miyarta taga kayan miyan yaɗan soyu, saita zuba ruwa ɗan kaɗan da kayan ƙamshi da magi amma ba star ba dan yana hana miya yauƙi. Da duk abinda take buƙata na saka miya ƙamshi ta saka ta maida ta rufe a binta da sake maida wutar can ƙasa. Dai-dai Granny ta gama yanka mata ɗanyen kalkashin. Amsa tai tana mata sannu da godiya. Granny ta bita da kallo tana murmushi. Madaidaiciyar tukunya ta samu ta saka kalkashin nan dan babu zancen wankesa shi. Tasa ruwa kaɗan da kanwa ta barsa a buɗe wutar naci daidai misali.

    Fita Granny tai dan an kira sallar isha'i, ita kuma tahau gyaran fruit salad ɗinta dan ɗan kaɗan zatayi ba yanda aikin zai mata yawaba. Saiko gashi ta gama a ƙanƙanin lokaci, tasa flavor na gwaba dana strawberry ta motsa. Kaɗan ta ɗan-ɗana, jin zaƙin ya mata dai-dai ta ɗaukesa tasa a fridge ta dawo wajen miyarta da dudduba. Komai yayi, kalkashinma ya dahu, kashe gas ɗin tayi ta koma wajen gyara kwakwar da zatayi juice itama, tabar kalkashinta dayay kauri sosai yana hucewa. Hakama miyar kayan miyanta tayi kauri yanda ko an haɗata da kalkashin bazata tsinkashiba. Sai da ta kammala haɗa coconut juice ɗinta ta saka a fridge shima sannan ta tattara kayan data ɓata ta wanke tsaf sannan tazo ta juye kalkashin cikin soyayyun kayan miyarnan ta motsa da kyau suka haɗe. Ɗanɗanawa tai taji komai dai-dai yanda take fata duk da dai akwai fargaba tare da ita har yanzun.

      “Inno an gama ko?”. Hajiya iya data sake dawowa ta faɗa tana shigiwa. “Eh Granny duk an kammala, amma dan ALLAH ki ɗanɗana wlhy inajin tsoro”.

      “Haba ɗiyar albarka nasanma komai yayi daɗi. ALLAH ya saka miki da kairan ya baki miji nagari dazai riƙemin ke gam, bar wani jin tsoro”. Kanta kawai ta duƙar tana ɗan murmushi. Sai dai a ƙasan ranta tana tunanin ita data haihu a waje ina ita ina yin aure. tafi ganema ta dage taita karatunta har itama ALLAH ya kaita lokacin da zata taimaki kanta da iyayenta......

       “Inno kinga ga naman kai nan da Rahi tai farfesu kafin ta tafi a haɗa masa dashi, sai akai masa gashi can ya dawo har yay wanka yana jira”. Hajiya iya ta katse mata tunaninta. Amsa mata tai da to tana haɗiye ƙwallar dake neman ciko mata idanu.

      Kular tuwon ta ɗauka tasa kan tire, ta zuba miyar a wani bowl mai murfi na tangaran mai haske, hakama farfesun tasa a ƙaraminsa duk ta ɗora a tiren. Fruit salad ɗin da lemon kwakwar ta fiddo a fridge duk da basuyi sanyi mai tsananiba sunyi dai-dai gamai sha. Fruit ɗin ta saka a bowl fruit salad, juice ɗin kuma tasa a jug da ruwa a wani tiren. Ta kuma gyara ɗan kwalinta cike da ƙarfin halin danne ciwon dake cinta ta ɗauka ta fito ranta fal fargaba.

     Zaune ta samesu shi da matarsa a dining ɗin. Tai sallama ya amsa batare daya ɗago daga latsa tab da yakeba. Farah kuwa bata amsaba saima harara data galla mata na tsananin kishin babu gaira babu dalili da haushin abinda hajiya iya tai mata akanta ɗazun. Ita dai Zinneerah gaishesu tai da masa barka da shan ruwa ta ajiye tiren ta koma ɗakko sauran kayan ba tare data damu da ƙin amsawar tataba.

      Harta gama shirya komai a dining ɗin bai ɗago ya kalletaba. Ta juya zata bar wajen ganin ta gama aikinta taji yace, “Zoki zuba”.

        Dawowa tai da baya cike da ƙarfin hali dan mararta ƙullewa takeyi. Sama-sama take jin tsawar Farah na faɗin, “Kinga dalla kama gabanki zan zuba masa ni tunda inada hannu”. Juyawa Zinneerah tai zata wuce dan taimakontama ita Farah ɗin tayi, amma saita tsinkayi muryarsa a karo na biyu. “Malama ki zubamin abinci nace ko”.

     Jitai kamar ta fasa ihu dan takaicinsu, ta kalli yanda Farah ɗin ke watsa mata harara kamar idanunta zasu faɗo. Shima ta dubesa har yanzu kansa a ƙasa yanata danna tab. Dawowa tayi da baya tunda tasan dai itama matar tasa ai ƙarkashinsa take duk da wannan isar tata da rainin wayo. Batare data sake kallon sashen Farah ɗinba ta fara zuba masa komai tana ajewa gabansa.

       Tana cikin zuba masa lemon kwakwar mararta tai matuƙar ƙullewa. Dole ta ajiye jug ɗin tai saurin zama a kujera tana kifa kanta a teble ɗin dan azaba.

       Karan farko ya ɗago kai ya dubeta. Farah kuma da kishi keci ta daka mata tsawa, “Kujimin ƴar barikin yarinya. bakin gama aikin da aka sakiba miye kuma na zama?”.

     Bata samu amsa daga Zinneerah ba dan bama jinta da ƙyau takeyiba. Shiko tab ɗin ya ajiye da maida hankalinsa gareta cike da nazari, ganin kusan sakan talatin bata ɗagoba yaɗan lumshe idanu ya buɗe akanta. A karon farko na rayuwarsa ya ambaci sunanta cikin muryarsa mai taushi da tarin nutsuwa da rashin sakewa. “Zinneerah are you ok?”.

       Har cikin rai da jini sai da Zinneerah taji fitar sautin sunanta akan harshensa. Ta ɗan ɗago hawaye shaɓe-shaɓe a fuskarsa ta. “Ba komai Yayanmu kaina ke ciwo”. Ta faɗa tana miƙewa tabar wajen.

     Da kallo ya bita kawai, Farah kuma ta rakata da harara tanajan tsaki da faɗin, “Lallai yarinyarnan idan kikace zakishiga gonata zanko juya fuskarki daga gaba ta koma baya a gidan nan wlhy”.

         Goshinsa ya murza kaɗan, dai-dai yana maida kansa ga abincin. Ya ɗan furzar da huci yana ɗaukar juice ɗin data zuba masa kaɗan a ƙaramin kofi ya kai baki. Duk jarabar da Farah keyi akan Zinneerah ɗin bai ma nuna yasan tanayiba balle ya tanka mata. Sai dai a ransa haka kawai yakejin dariya nazo masa.

 

          Zinneerah kam tunda takai ɗaki kwanciya tai a sofa tana riƙe mara dan Hajiya iya na bayi tana wanka. Taja kusan mintuna goma a wajen tana murƙususu harta faɗo a kujerar dan azaba kafin Hajiya iya ta fito.

      “Subahanallahi, Inno lafiya kuwa?”.

      Cikin kuka ta nunama hajiya iya saitin mararta. “Ikon ALLAH, nikam dai wannan ciwon mara daga ina? Keda baƙya ciwon mara mai ƙarfi irin haka amma wannan karon da alama ta canja miki sallo. Kinga tashi kije kiyi wanka da ruwan zafi sosai bara na leƙa su Haneef ko sun dawo, bansan ina Khalipha ya kwashesu suka tafiba tun ɗazun.

       Da ƙyar ta amsama hajiya iyan. Sai dama ta taimaka mata zuwa bayin, ta kuma haɗa mata ruwa mai zafi tace tai wankan tana zuwa.

 

      Ganin yanda Hajiya iyan ta fito da hanzari daga ɗaki Yah Adnan dake cin abinsa hankali kwance matarsa na gefe tana masa hira bayan ta gama bala'in Zinneerah ya ɗago ya dubeta. Tana gab da fita yace, “Granny lafiya kuwa?”.

      Juyowa tai ta dubesu dan ita hankalinta baima kai garesuba. Cike da damuwa tace, “Moddibo Zinneerah ce bata da lafiya. Inason na duba cikin su Moos'ab ne wani yazo ya kaita asibiti kar abin ya ƙara mata tsanani”.

       Shiru yay yana kallonta kamar bazaice komaiba. Ganin Hajiya Iya ta juya zata fita yace, “Granny su da basa nan ki jira na kammala dan zanje wajen Mahmud dama”.

      Dawowa Hajiya iya ta sakeyi tana faɗin, “To Alhmdllh shikenan ma, bara naje ta shirya kafin ka kammala”. Kansa kawai ya jinjina mata yana lumshe idanu da buɗewa alamar amsawar kenan.

         Wani irin kallo Farah ta zuba masa na tsananin takaici da kishi. Muryarta har rawa yake wajen faɗin, “Wai ban ganeba. kaine zaka kaita asibitin kuma?”.

       Idanunsa ya ɗago ya dubeta ya maida ga abincinsa batare daya bata amsaba. A ƙufule ta miƙe tana cewa, “Wlhy to sai dai mutafi tare. Dan bazan yarda ka tafi da wannan shegiyar yarinyar mai kama da aljanu kai kaɗaiba. Ni wlhy bazan iyaba ka shirya mukoma gaskiya”.

     Da kallo ya bita harta shige lungun da ɗakinsa yake. A bazata murmushi ya suɓuce masa ya girgiza kansa da ɗan taɓe baki ya ɗauke kai.

        Harya kammala abinda yake ya miƙe zuwa ɗakin bata fitoba, koda ya shigo isketa yay tana waya. Yasan dai bazai wuce Mammah ko cikin yayuntaba. Dan haka bai tsaya sanin dawa takeyiɗin ba ya shiga toilet. Cikin abinda baifi mintuna uku ba ya fito. Key ɗin mota da ke a bed side drawer ya ɗauka ya nufi hanyar fita ya barta tana wayar har yanzun.

       Yana fita itama ta miƙe ta ɗauka ɗan kwalin abayarta ta bisa tanayin sallama da yayanta da shigowarta ɗakin kiransa ya shigo mata a waya. Shine ta zauna amsawa.

 

        Sai da yay sallama a ƙofar ɗakin Hajiya iya ta amsa masa da bashi izinin shigowa sannan ya shiga. Zinneerah data fito wanka ta gama shiryawa cikin baƙar doguwar riga tana kwance a bakin gadon idanunta a lumshe hawaye na zirara. Kallo guda yay mata ya ɗauke kai ya maida ga hajiya iya data ɗakko mata hula da ɗan kwalin rigar.

          “Haka take ciwon kai?”.

  Ya tambaya kansa tsaye kamar yanda ta sanar musu ɗazun. Kallonsa hajiya iya tayi, “Ciwon kai kuma Moddibo? Zinneerah ce zata zauna yima ciwon kai raki kamar haka?. Ita jarumace ai da kake ganinta, tunda ka ganta haka ai abinda yafi ƙarfin ciwon kanne mararta ke ciwo, kuma da ba haka take mataba”.

       Jin abinda Hajiya iya tace ya sashi janye idanunsa daga kallonta ya maida kan Zinneerah data zumɓuro baki alamar bataso Granny ta faɗa abinda ke damun nataba. Baki yaɗan taɓe da nufar hanyar fita yana faɗin, “ta sameni waje”. Daga haka ya fice abinsa ya barsu da ƙamshinsa........

 

 

 

*_Sauran inji wani yace kaɗanne gobe na rage mudu😂🤒🤒._*

 

 

 

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

 

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

 

*_ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_

 

*_ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_

 

*_ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_

 

*_ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_

 

*_ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_

 

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

 

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

 

Kamar haka👇🏻💃🏻

 

Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700

 

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

 

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

 

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

 

*_08085405215_*

 

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

 

  0903 234 5899

 

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

 

*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

 

*_TYPING📲_*

 

 

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

 

 

*Page 25*

________________________

 

*ZAUREN GIRKI*

 

Abinci na *gargajiya* ...Kuka,Taushe,Danbu, Sinasir,Waina

Abinci na *zamani* ...Afang,Edikaikong, Coconut Rice, Ofada Rice

 *Garabasa* ...Salads,Pancakes, Plantain mosa, Gyaran nama/kifi kafin girki,Shirin/shinfida abinci kan table.

 

• A kowane sati,in shaa ALLAAH, za a koyi miya/abinci daya da kuma wani abu ta karkashin *Garabasa* .

• Duk ranar *Lahadi* za fito da sabobin *videos* guda biyu na miya/abinci da na wani abu daga karkashin *Garabasa* .

• Kowacce daga cikin masu koya zasu bibiya video su kwaykwaya su gwada yin abincin bisa ga umurnin *video*

• Kowane ranar *Asabar* za a yi *Q&A* a inda kowa zai samu yin tambayoyi akan *videos* din satin daya gabata, da inda suke neman karin bayani/gyara akan kokarinsu na gwada abincin *video* da kawunansu

• Ga wace taga dama,daga ranar *Talata* za a iya fara turowan *video* ta kokarin da aka yi na kwoyon abincin da aka kwoyar ta *video* na ranar *Lahadi* .

• Inda akwai me bukatan wani fanni na abinci,ana iya hada *aji(Special Personal Video Classes)* musamman domin wannan bukatan.Anan za a shirya live *video* sessions domin cimma wannan burin

 

• Za a biya dubu biyu *(#2,000)* na watan farko,sannan za dinga biyan dari biyar *(#500)* ta kowane sati ga masu bukatan shiga group dinnan namu mai albarka

• *Zen Commute,account number 0119343451 Union Bank* ,asusunmu

• Duka lokacin da aka biya sai a turomana da hoton teller ko bank confirmation akan wannan number ta *WhatsApp 0817-541-7533*

• Ana iya tuntubammu akan wannan number domin karin bayani; **0817-541-7533(WhatsApp kawai)*                                                                     

ZA MU FARA ZAUREN GIRKI LAHADIN SATIN FARKO TA WATAR SEPTEMBER,IN SHAA ALLAAH!

 

 *MU TSARE MUTUNCINMU,MU KARE MAZAJENMU...MU KOYI GIRKI!!!*

 

_________________________

 

*Page 25*

 

............“Kajimin ja'iri, basai ka tsaya ka kamata ba kuma? Kinga Inno na tashi muje ni na rakaki”.

        Zinneerah da tonon sililin Granny yasata fahimtar shine zai kaita asibitin tace, “Granny dan ALLAH muje da wani cikinsu aunty Abidah ko su Meenal basai shiba”.

       “Keda kike a wannan halin sai kin zaɓi mai tafiya. Kinga maza miƙe karma ya tafi dan shi ba saiti ne da shi ba wani lokacin”.

      Dole ta miƙe Granny ta kamata badan taso ba. Tsaye suka samesu su duka a jikin mota, shi yana waya Farah na tsaye jingine tana danna tata wayar. Batare da hajiya iya ta damu da ganinsu su biyunba ta buɗe gaban motar ta saka Zinneerah shiga. Sai lokacin suka lura da zuwanta. Farah tabi Hajiya iya dake duban inda Yah Adnan ɗin yake da kallo. “Moddibo kuje dan ALLAH, kasan shi mai ciwo ƙosawa ne da shi”.

       Kansa ya jinjina mata kawai batare daya bar wayarba ya buɗe murfin zai shiga Farah da haushi ya kume tace, “Granny ai sai dai ta dawo baya dan tare zamuje”.

      “Asibitin? A'a idan kin bisu ni motsinwa zanji kuma tunda su Jamal basa nan. Kinga muje ciki muyi hira mai sunan ƴan gayu”. Ta ƙare naganar dajan hannun Farah batare data jira abinda tai niyyar faɗaba.

      Ta cikin mirror Yah Adnan ke kallonsu. Ya danne murmushin dake neman suɓuce masa a fuska saboda rigimar Granny. Daga haka yay horn yana harba motar zuwa gate.

 

         Tunda suka hau hanya baiyi ko tari ba duk da yana jin shashshekar kukan Zinneerah daka ƙudundune kanta cikin ƙafafunta data naɗe sama gaba ɗayanta ta dunƙule a kujera. Sai dai duk kiran wayarsa da akeyi tunda ya gama ta farko bai sake ɗagawaba har suka iso Shira hospital.

     Duk da darene ko ina cikin haske yake kamar ka yarda allura kaga abunka. Sai da ya gama dai-daita fakin yaɗan dubeta ya ɗauke kansa. Wayoyinsa biyu ya ɗauka batare daya mata magana ba ya buɗe ɓangarensa ya fito. Sai da ya rufo murfin ta fahimci ya fita dan haka ta ɗago cike da ƙarfin hali fuska shaɓe-shaɓe da hawaye.

    Tana ɗaura hannunta akan handle ɗin ƙofar da niyyar buɗewa ta fita tunda tasan bacewa zai ta fito ɗinba sai taji ƙofar ta buɗe. Akansa idanunta suka sauka da mamaki, sai dai ganin yanda yaci toka yasata saurin maidawa ƙasa. Gudun kartai laifi ya sata ziro ƙafa ɗaya zata fito ɗayar kuma ta riƙe. Tsareta da ido da yayi ga kuma azabar da takeci yasata sakar masa kuka.

        A ransa yace (sai shagwaɓan tsiya). a fili kam sai ya girgiza kai kawai ya ɗauke kai yana miƙa mata handkerchief. “Malama goge waɗanan hawayen tunda ba satoki naiba”.

         Duk da halin da take a ciki saida tace (bama gara wanda ya satoni da kai ba) amma a zuciya😂. A zahiri kuwa baki ta tura gaba da amsar handky ɗin nasa da keta uban ƙamshin turarensa tahau share hawayen. Shi kuma yay gaba abinsa cikin asibitin batare daya jirataba duk da ya fahimci bazata iya taka ƙafarba dan tun'a gida ya lura dama da ɗingishi ta fito sanda Granny ta kamota.

          Kanta ta ƙara maidawa cikin ƙafafu ta dasa sabon kukan takaicinsa dana ciwo. A haka Nurse ɗin daya turo tazo ta sameta. Itace ta taimaka mata ta fiddota a motar suka fito. Da ƙyar ta taka ƙafar data ƙara riƙewa zuwa cikin asibitin. Suna shigowa a bazata sukaci karo da Khalipha.

       “Kai! Beauty lafiya kuwa? Ke da wa haka?”.

        Bata iya bashi amsaba sai dai ganinsa yasata jin sanyi har cikin rai. Shima bai damu da rashin amsawar tataba ya maida dubansa ga Nurse ɗin. “Sister Sadiya ita da waye sukazo?”.

      Cike da girmamawa tace, “Ogane nidai yace naje na shigo da ita sir”.

    Yasan Yayansu suke cema oga a asibitin. Dan haka cike da mamaki yace, “Yana ina shi ɗin?”.

     “Dr Mahmud office sir”.

“Okay kuje ina zuwa nima”. Ya faɗa yana nufar wani hanya alamar akwai abinda zaiyi.

 

        Sai da Nurse Sadiya tai sallama aka basu izinin shiga sannan ta shigo riƙe da Zinneerah da ganin Khalipha yasaka kukan nata tsagaitawa. Miƙewa Dr Mahmud yayi yana mata sannu, shiko kansa yana duba wani file bai ɗagoba balle ya nuna yasan sun shigo office ɗin. A kujerar dake kallon wadda yake zaune Dr Mahmud yasa Nurse ɗin ta zaunar da ita.

         “Sorry ƙanwarmu kukan ya isa ko?”. Dr Mahmud ya faɗa yana murmushi da kallon Zinneerah ɗin a zuciyarsa yanaji kamar yasan fuskarnan.

       Kanta taɗan jinjina masa tana ƙara takure kanta waje ɗaya a cikin kujerar dan kusancinsu ya sakata jin ta takura, duk ya cika wajen da kwarjininsa. Kallonsa taɗan sata taga har yanzu yana a yanda suka samesa. ta janye tana maidawa ga Dr Mahmud daya jeho mata tambaya.

       “Ƙanwarmu mike damunki ne?”.

Ɗan jimm tai kamar bazatace komaiba dan har sai d Yah Adnan dake saurarensu ya ɗan ɗago ya dubeta ya maida kansa. Fahimtar da Dr Mahmud yay kamar tanajin nauyin maganar saboda AK ya sashi faɗin “To ko dai zamu tada boss a wajen nan ne? Ranka ya daɗe kamarfa........”

     Saurin katsesa tai da cewa, “Cikina ke ciwo”.

     AK daya ɗan ɗago ya dubeta a karo na biyu saiya girgiza kansa kwai kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya sake maida kansa ga takardun hannunsa. Takarda da pen Dr Mahmud ya tura mata, “Idan babu damuwa rubuta anan kawai”.

        Har cikin ranta taji daɗin hakan, babu musu taja takardar ta fara rubutawa tana cije baki. Koda ya amshi takardar ya duba yaga mita rubuta sai baice komaiba ya jin jina kansa yana nuna mata ɗan gadon duba marasa lafiya dake can gefe.  “jeki kwanta acan ina zuwa”.

         Miƙewa tai cike da ƙarfin hali ta nufi gadon ta kwanta. Shima sai ya miƙe ya bita da wani ɗan dogon roba a hannu da syringe. Tambayoyi ya ɗan ƙara mata tana bashi amsa cike da jin nauyinsa. Daga haka ya ɗiba jininta.

     A dai-dai nan Khalipha yay sallama ya shigo office ɗin. Ɗagowa Yah Adnan yay ya dubesa da ɗan mamaki. Amma baice komaiba. Khalipha da hankalinsa duk yana ga yanda yaga Zinneerah ɗin ya ƙaraso yana faɗin, “Yayanmu barka da dare”.

        “Dama kana nan?”.

  “Eh wlhy ban jima da zuwaba. Dr Muneer ne ya kirani mukai wani aiki. Miya samu Beauty ɗin ne?”.

       Wani ɗan luu da idanu yayi da tsatstsare Khaliphan da idanu tamkar baiji miya faɗa ba. Shima Khaliphan sai yanzu ya fahimci katoɓarar da yay na cema Zinneerah beauty ɗin. Ya ɗan sosa gefen wuyansa yana murmushi. “I'm sorry yayanmu”.

        “For what?”.

Ya faɗa cike da salon basarwar tasa yana maida kansa ga file ɗin hannunsa.

      Dariya Khalipha ya ƙyalƙyale dashi yana barin wajen ya nufi can inda Zinneerah da Dr Mahmud suke. “Oh oh sweet sister sorry, dama haka kike ragguwa ashe?”.

        Dr Mahmud ne ya bashi amsa cikin dariya. “A'a Khalipha karfa ka cika baki, dan sai na bata labarin naka rakin kaima”.

       “Lalala Yah Mahmud yi haƙuri kar kaja ta rainani, mike damunta ne? Naga kamar sun shigo tana ɗingishi”.

     Kai tsaye Dr Mahmud yace, “Tana complain ne na mara, inaga zamuyi mata text mugani, duk da ina zargin dai bazai wuce....” Sai kuma yay shiru yana ɗan duban sashen da AK yake zaune.

      Addu'ar samun lafiya Khalipha yay mata yana ɗan murmushi da kauda zancen ta hanyar cewa, “Bara naje da jinin lab to”. Daga haka ya fita. Duk abinda suke tattaunawa Yah Adnan na jinsu. Amma saika rantse ma baya office ɗin, daga ƙarshema waya ya kira har Khalipha ya dawo bai gamaba.

        Drip Dr Mahmud ya sakama Zinneerah ya dawo inda AK yake ya zauna suka cigaba da tattauna abinda ya shafesu har Khalipha ya dawo da result ɗin da magunguna daya sayo.

      Bayan Dr Mahmud ya amsa ya duba yace, “Dama abinda nai zargi kenan, bazai wuce harda Imfection ɗin ba, zamuyi treating ɗinsa insha ALLAH zai barta tunda baiyi ƙarfi ba. Tunda ma ka haɗo maganin inaga kai mata allurar nan kawai”.

        Miƙewa Khalipha yay yana faɗin, “Okay ALLAH yasa dai bata tsoron allura to”. Dariya kawai Dr Mahmud yayi, shima bayan ya mata allurar duk da barci naɗan figarta sai ya fita ƙarasa uzirinsa. Yabar Dr Mahmud suna cigaba da tattaunawa da Yayan nasu da ya koma kamar baya office ɗin.

 

★★★

 

        A gida kuwa Farah tamkar zatai ƙaramin hauka a cikin ranta. Tanada kishi sosai wanda ita kanta wani lokacin abun har tsoro yake bata, dan Adnan dai ba taɓa mata alƙawarin bazai ƙara aure yayi ba. Ko lokacin da su Hajiya Iya suka takura masa saiya ƙara aure badan tsayawar Mammah a kansa ba da babu abinda zai hanashi ƙarawar duk da ba nuna mata yanada buƙatar hakan yayiba.

       Tsaf hajiya iya tana lure da ita. Kuma dama da biyu ta hanata bin nasu. Dan haka ta shige ɗaki abunta tai shirin barci ta kwanta tunda tasan dai ba binsu Farah ɗin zataiba a yanzu.

               Kamar yanda ta ƙware akai ƙara wajen Mammah yanzu ɗinma sai da ta faɗa mata tana kuka. Ran Mammah ya ɓaci sosai jin yarinyarma ba'a cikin ƙannensa takeba kamar yanda ita Farah ɗin tace tana tunani. Koda Mammah ta kirasa ashe wayar a nan gida ya barta, bai fita da ita ba, na hannunsa na alaƙar business ɗinsa ne kawai.

     Wannan abinne ya ƙara ƙular da Farah ta dinga kai kawo tsakanin ɗakinsa da falo ita kaɗai dan hajiya iya dai ta shige. yaran kuma da suka dawo basu shigo nanba dan a gajiye suke.

 

         ★★

 

      Sai kusan sha ɗaya ruwan da aka sakama Zinneerah ya ƙare suka nufo gida. Tana a baya ita kaɗai, Khalipha ne yanzu ya amshi driving ɗin, shi kuma yana a gefensa zaune. Babu mai magana a motar dan duk sun gaji kwanciya duk suke buƙata, sai sanyin ac daya takurama Zinneerah, hakan ya sata dunƙulewa waje guda barci sama-sama nason figarta.

         Koda suka iso gidan Khalipha ne ya buɗe mata ta fito, ganin yanda take ɗan tangaɗin barci dana rashin ƙwarin jiki yace, “Ƙanwata kodai na kamaki ne?”.

      Kanta ta girgiza masa a hankali cikin yanayin kasala tana dafe jikin motar dan ji take tamkar zata faɗi. Ɗan matsawa Khalipha yay da ita gab yana ƙoƙarin kai hannunsa zai kamo nata. Yah Adnan dake kallonsu ta gefen ido, amma saika ɗauka gaba ɗaya hankalinsa baya tare da su ya katse hanzarin Khalipha ɗin dake neman kamo hanun Zinnerah, “Besty kaje da takardun nan ɗakinga zuwa safiya idan ALLAH ya kaimu saika dubasu zamuyi magana daga baya”.

     Dole Khalipha ya haƙura daga son taimakon Zinneerah ya juya garesa ya amshi takardun.

     “Kaje kawai sai da safe muma bara mu shige dare yayi. Ke kuma muje”. Ya sake faɗa ciki-ciki yana duban Zinneerah da duk tana saurarensu.

        Dole Khalipha yay musu sai da safe yana nufar sashen samarin gidan. Shikuma ya tasa Zinneerah dake tafiya da ɗan layi na barci suka nufi sashen hajiya Iya. Abin tsautsayi tana tura ƙofar falon da niyyar shiga hannunta ya gota akan handle ɗin saboda tuntuɓe da takalmi da tai.

     Saurin tarota yay ganin zata faɗi, saboda ya rigada ya kawo jiki ita kuma tayo baya. Sai kuma ya ɗagata da hanzari yana miƙar da ita tsaye sosai akan ƙafafunta.

      Ɓoyayyen numfashi ta sauke da saurin yin gaba har ƙafafunta na neman harɗewa. Ya ɗan bita da kallo ƙasa-ƙasa harta shige bedroom ɗin hajiya iya. Janye idanunsa yay da zummar nufar nasa ɗakin shima yaci karo da gimbiya Farah mai zamani hakimce cikin kujera tacika tayi fam. yanda tai mugun tsatstsaresa da idanu ya bashi tabbacin tunda suka shigo tana a falon kenan.. Sanin halinta yasa bai tanka mataba ya ɗauke kansa yay gaba.

        Sai da yay kusan mintuna biyar da shigowa sannan ta biyosa. Tana shigowa yana shiga bayi. Duk da tsahon lokacin daya ɗauka bai fitoba a tsaye ya sake isketa ta kuma cika fam fiye da farko.

        Hidimar shiryawarsa ya shigayi yanzunma bai kulataba. Sai da ya gama tsaf cikin kayan barci ruwan sararin samaniya sannan. Kamar zai shareta dan takaici sai kuma ya ɗan dubeta ya ɗauke idanunsa. Inda take ya matsa sosai tare da dafe bangon da hannayensa biyu ya sakata a tsakkiya yana zuba mata fararen idanunsa da alamun barci ya bayyana a cikinsu.

       A take dukkan fushinta ya fara rauni dan waɗanan idanun nasa suna ladabtar da ita idan tai laifi. Suna kuma tabbatar mata da ɗunbin soyayyarta a cikinsu idan yaso lallashi. Suna kuma mata kwarjini da girmama kimarsa a gareta a duk sanda shi ɗin yazam mai laifi a gareta.

       A karan farko ya saki murmushi ganin yanda ta lumshe nata hawaye na silalowa. Fuskarsa yakai gab da tata suna musayar shaƙa da zuƙar ƙamshin juna. Kafin ya cire hannunsa guda dake dafe da bango ya saƙalo ƙugunta ya sake mannata da jikinsa sosai yana wani sakar mata numfashinsa da ƙarfi akan fuskarta. A take ta saki nannauyar ajiyar zuya da saka duka hannayenta ta zagayoshi ta ƙanƙame itama.

      Murmushin ya sake saki, batare daya ce komaiba ya ɗauketa cak ya nufi gadon da ita. Yana sauketa bargo yaja ya lulluɓa musu, zatai magana ya rufe mata bakin da nashi. Daga haka ɗakin yay tsit kamar ba ita ta gama cin alwashin karta masa shika shikan rashin mutunci cassa'in da tara ba.

 

______________________________

 

       *_DANYA_*

 

Duk yanda Inna tasoji daga Karima hakan ya gagara. Dan ciwo ta kwanta kashirɓan tun randa ta dawo. Abin kamar wasa sai ga ƙaramar magana na neman zama babba. Tuni Inna ta manta da wani zancen kiranyen dataima Baba saboda ruɗanin halin da Karima ke ciki.

      A rana ta uku duk yanda taso ɓoyewa hakan ya gagara. Dan dole ta nufi gidansu Babawo ta sanarma innarsa. Sunyi mamaki matuƙa. Dan shi dai baice dasu Karima tana Danya ba, kuma koda safe sai da sukai waya da shi. Dole Innar Babawo ta ɗakko gyale ta biyo Inna gidanta. Itama hankalinta ya tashi ganin yanda jikin Karimar yay kaca-kaca da sayin duka ga ciki tsoho haihuwa ko yau ko gobe.

       A ruɗe tace ma Inna ta shirya karimar suje asibitin kusada. Bara taje ta nemo ƙanin Babawo ɗin tunda yanada mashin. Daga haka ta fice ita kuma Inna daketa tsinar Babawo ɗin ta shiga kimtsa Karima.........

 

_____________________

 

   

          Hajiya iya batasan su Zinneerah sun dawo gidanba sai da asuba ta ganta kwance a bayanta. Hannu tasa ta shafa mata fuska tare da gyara mata bargo. Itama cike da ƙarfin hali ta nufi bayi yin alwala dan ƙafarta ciwo take mata tun da daddare dama. Da ƙyarma ta iya kai kanta bayin. hakama da tayo alwalar da gyar ta fito. Duk yanda taso gabatar da salla a tsaye hakan ya gagara sai a zaune tayita. Bayan ta idar kuwa ko azkar yau batayiba ta zame ta kwanta a wajan.

 

       Itama Zinneerah farkawa tai, sai dai koda taga Hajiya Iya kwance a ƙasa bata kawo komai a rantaba ta shige bayi kimtsa jikinta. Ganin harta fito Hajiya Iya na kwance a wajen sai abin ya ɗan bata mamaki amma batai magana ba ta hau shiryawa dan wanka tayo. Batajin ciwon komai yau sai rashin ƙwarin jiki. Ta shirya cikin siket da riga na baƙin Material mai adon firanni golden. Ganin Hajiya Iya taɗan motsa ya sata zuwa gabanta ta tsugunna tana gaisheta.

     Hajiya Iya ta buɗe idanu da ƙyar tana duban Zinneerah ɗin. Murmushin ƙarfin hali tayi da miƙa mata hannu ta kamo nata. “Inno na yaya jikin?”.

     Kasa amsawa Zinneerah tayi saboda jin zafi jikin na Hajiya Iya. aɗan rikice ta sake damƙe hannun cikin nata tana faɗin, “Granny baki da lafiya ne?”.

        Kamshinsa ne ya katse Hajiya iya dake ƙoƙarin bama Zinneerah amsa. Zinneerah ma sai ta ɗan dubi ƙofar dai-dai ya shigo idanunsa suka shige cikin nata. Saurin janye natan tayi tana maida kai ƙasa dan wani irin matsananciyar kunyarsa taji saboda tunowa da faɗa masa a jiki datai jiya da dare. Ga sirrinta daya gamaji a bakin hajiya iya kafin su wuce da kuma tabbacin ya sakejin wani wajen Dr Mahmud.

      Shima nasa idanun ya janye yana duban Hajiya iya dake kallonsa a kwance. A take ya gano babu lafiya dan yasan hajiya iya sosai a rayuwarsa. Duk da kuwa zaman da yay a wajenta na shekaru tara ne kacal, sai hutun da yake zuwa mata kuma bayan ya koma London karatunsa.

       Ta inda Zinneerah ke tsugunne ya ƙaraso ya ɗan ranƙwafo kansu yana kai hannu goshin Hajiya Iyan. “Granny lafiya kuwa?”.

        “Wlhy ƙafafun nan ne ke neman takuramin kwana biyun nan Moddibo ”.

      Idon Zinneerah na cikowa da ƙwalla tace, “Amma Granny shine baki faɗaba? Wlhy jikinki zafi dan ALLAH ki tashi muje asibiti”.

     Yanda ta ƙare maganar hawaye na silalowa ga rawar murya ya sakashi ɗan dubanta, kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa. Ɗayan hannun Hajiya iya ya kama shima ya tadata zaune sosai dan tanada jiki itama masha ALLAH.

        Gaban Hajiya Iyan yay wani ɗan tsuggunne idanunsa na sauya launi zuwa damuwa. Dole Zinneerah ta miƙe saboda kusancin da suka samu yayi yawa. Cikin wayancewa tace, “Bara na haɗo miki kunu kiɗansha sai kisha maganinki”.

     Murmushi Hajiya Iya tai tana binta da kallo harta fice, kafin kuma ta sake maido idonta kan Yah Adnan dake mata tambaya muryarsa a ƙasa.

 

      Al'amarin kamar almara sai ga jikin hajiya iya na neman rikicewa a wannan yini, dole Dr Mahmud da Khalipha suka rufu a kanta duk da shi bai kammala nasa karatunba ma. Amma kwazon da yake nunawa yasa ko ƙasar yazo yakanje Shira hospital yay wasu ƴan ayyuka dai-dai saninsa.

        Tashin hankalin ruɗewar jikin ya saka Yah Adnan cewa zai wuce da Hajiya Iyan london a yau. Amma sai Baffah da ake saran zai dawo ƙasar yau ya taushesa akan yay haƙuri yana zuwa shima.

    Badan yasoba dole yabi umarnin mahaifinsa da yake zuwa yamma jikin Alhmdllh ya ɗan ɗaga mata. Duk wanda ya kalli Zinneerah yau yasan tasha kuka. tayi wuni firgai-firgai da ita na damuwa. tabi ta nane a ɗakin wajen Hajiya iya ita dasu Jamal. Ko yayansu ya shigo su su Jamal tsoro na sakasu fita da shakkarsa. Itako duk da tanajin shakkar tasa da kwarjin da yake mata saita fiske abinta taƙi fita.

         Dama tun lokacin da jikin ya rikice tai kiran Maman Sadiq ta sanar mata. Itama hankalinta ya tashi matuƙa dan haka tace zuwa yamma zata shigo tare da yara su dubata dan yanzu duk sun wuce makaranta Little ne kawai a gidan.

 

    Aiko kamar yanda Mman Sadiq tai alƙawari bayan sallar la'asar sai gata tare da Sadiq, Abdull, Aliyu sai Little. A napep sukazo kasancewar Abba baya nan yaje ɗanmusa duba yayansa da baida lafiya shima.

        A gate ya saukesu mmn sadiq tai kiran Zinneerah a waya dan tazo ta shiga dasu. Duk da tana tare da damuwar ciwon hajiya iya cike da ɗokin ganin ƙannen nata da gudan jininta ta fito zuwa hanyar gate. Sai da suka gaisa da maigadi ta sanar masa baƙine zasu shigo.

      “To Hajiya bara a buɗe musu”. Ya faɗa yana ajiye butar hannunsa daya ɗauka alamar zaiyi wani abu. Da gudu su Abdull sukayo kanta lokacin da suka shigo. ganin yanda Little ya biyo rububi a guje shima ya bata dariya. Tsugunne yakai da buɗe musu hannayenta duk suka shige su huɗun. Mmn Sadiq dake binsu da kallon sha'awa taɗan murmusa tana ɗauke kanta. Da ƙyar Zinneerah ta samu ta miƙe tsaye hannunta riƙe dana Aliyu tana ɗauke da Little a ɗayan ta dubi mmn sadiq da faɗin, “Mama sannunku da zuwa kumuje ciki”.

       Kai kawai Mmn sadiq ɗin ta jinjina mata tana mamakin yanda ɗiyar tata ta ƙara canjawa a ƴan kwanakin data dawo gidan. Zuwansu tsakkiyar harabar gidan yay dai-dai da fitowar AK daga sashen Hajiya iya kunen sa manne da waya alamar magana yakeyi, sanye yake cikin ƙananun kaya da suka sakko fiddo zallar ƙuruciyarsa da hutu dajin daɗi, ya cigaba da takowa a hankali garesu suma suna nufarsa duk da Zinneerah jitake tamkar zata faɗi dan har haɗewa ƙafafunta keɗanyi..........

      

   

*_Harda na gobe😫😫🤧_*

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post