Makauniyar Kaddara Hausa Novel page 31 - 35 - Novels Elite

Makauniyar Kaddara Hausa Novel page 31 - 35 - Novels Elite

Makauniyar Kaddara Hausa Novel page 31 - 40 - Novels Elite

MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

*Page 31*

  ________________________

 

 _*LAVENDER RESTAURANT..*_

   _(Palace of mouthwatering food/delicacies)_

 

_IDAN KUKAJI GANGAMI DA LABARI, INA MASU SON INDA ZASU SAMU INGATACCEN ABINCI MAI DADI DA LAGWADA? KAI BA ANAN MUKA TSAYA BA, INA SABBIN AMARE? MAMAs, YAYYU? DA KANNEN MU MASU SON KOYAN GIRKUNAN YAN GAYU NA KASAR NIJERIYA DA KETARE?_

 

_*TO KU MATSO...! AT LAVENDER RESTAURANT GOTS YOU COVERED. ABINCIN KASASHE DA DAMA MUKE KOYARWA,,COME LETS UPGRADE YOUR FOOD TIME TABLE, MATSO KUSA YAR UWA GA DAMA DA ZAKI CANZA YANAYIN ABINCIN GIDAN KI, KOWA YASAN IYA SARRAFA ABINCI NA TAKA RAWAR GANI A GIDAJEN AURE. KAI KO BUDURWA CE INDE KIN IYA GIRKI ZAKIGA KOWA YANA HABA HABE DAKE.._*

 

_*UNCLES, DADDIES, BROTHERS., NEWLYWED HUBBYS..! KU ZO KU YIWA ‘YAYAN KU, MATAN KU DA KANNEN KU RAJISTAR WANNAN HARKA TA KOYAN GIRKI.._*

_*Lavender catering school zamuyi practical class. zamuyi 30 dishes continental,snack & desserts, traditional dishes, drink. Fee din 40k NE. phone number WhatsApp and call 09080299283  akwai discount na 5% ga mutum uku farko wadanda sukai register aranakun independence 1/10/2021  to 3/10/2021 Nigeria @ 61_*

_*ZA’A FARA CLASSES RANAR 14/10/2021. WATO SHA HUDU GA WATAN OKTOBAR DA MUKA SHIGA YAU._*

_*GIRKE GIRKE GUDA 30😫😨AKAN DUBU 40 KAWAI, HARDA BONUS NA SNACKS, DESSERTS, TRADITIONAL AND MODERN DRINK, GARGALIYA DA ZAMANI🥂WATA DAYA CHAS ZA’AYI ANA KOYAN GIRKE GIRKEN. _*

 

_*KU SAKE KARANTA WANNAN BONUS DIN👇🏾RIGIJI GABJI_*

 

_*Nigeria @ 61 _*

_*COOKING COMPETITION!!!_*

 

_*from lavender Catering ina masu son koyon girki ga dama zaku shiga gasarmu ta girki bayan kunyi register damu akan 10k,wanda yazo  na 1zai shiga ajin mu free hade da wasu prize din na 2 da na 3 kuma zasu bayar da rabin kudine  da wasu prize suma saura kuwa  zasu ayi musu ragin 5% da wasu prize wannan gasa zamu yita ranar lahadi ne 3/10/21 zamu rufe registration na gasar ranar asabar_*

 

_*LAVENDER RESTAURANT: NA GARIN KANO, CLASSES DIN AKWAI PRACTICAL AND ONLINE CLASS GA WANDA KE NESA_*

____________________

*Page 31*

..............Farah na kammala bin dokar AK na komawa ɗakinta shiri tai ta fita zuwa gidan Mammah, a garin suke amma ba'a street ɗaya suke ba. Su Hajiya iya basusan bata a gidanba sunata hidimarsu. Sai dai su duba lokacin salla su tashi suyi su koma tebirin hira. Sai da Khalipha ya dawo shima ya zauna suka ɗora cike da farin ciki.

       Sunata zuba idon ganin dawowar AK gidan amma shiru, dan har lokacin dawowarsa aiki ya wuce babu shi. itama kuma Farah ɗin dawowar Khalipha gidan ya fahimtar dasu ta fita. Dan mai aikinta ta gama duk wani aikinta na wannan ranar ta tafi itama. Sai ya kasance sai su kaɗai ne a gidan kawai. Gajiya ta saka su Zinneerah kwantawa da wuri suka bar Yah Khalipha da Hajiya iya zaman jiran shigowarsa amma shiru.

     Hankalin Khalipha ne ya fara tashi, duk da yasan bawai wani abune ya samu yayan nasu ba, bazai wuce dai ɓacin rai ya hanashi shigowa gidan ba. Miƙewa yay ya fita domin zuwa can ma'aikatar tasu ya dubashi ko yanacan idan bai tafi gidan Mammah ba, tunda yaga gimbiyar gidan da alama itama tana can. Zuwanta canɗin kuma bawai zai haifar da ɗa mai ido ba ga Yayansu, dan sai ta masa haɗin da sai Mammah ta ɓata masa rai musamman daya kasance itama akan abinda bata farin ciki da shine tunda itama Farah ɗin ai karatunta take bi. Tun farko an nuna mata su ɗin basu da muhimmanci da mutunci shiyyasa take kallonsu a hakan

 

       Kusan a lokaci guda AK da Khalipha suka ɗora hannyensu akan handles ɗin ƙofar, shi da nufi fita, shi kuma da nufi shingowa. Sai dai AK dake ƙoƙarin shigowar ya samu nasarar turo ƙofar. Baya Khalipha yaja yana sauke ajiyar zuciya. Hakan yasa Yayan nasu binsa da kallon mamaki.

      “Lafiya kuwa? Ina zakaje?”. Yay maganar yana kallon agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa da duban Khalipha ɗin.

     Cikin damuwar ganin yanayinsa Khalipha yace, “Yayanmu dama kai zanbi hankalin Granny duk ya tashi da rashin dawowarka akan lokaci.

      Duk da damuwar dake tattare da fuskarsa da zuciyarsa sai ya saki guntun murmushi kawai yana miƙama Khalipha ɗin kayan hannunsa. Shi kuma ya hau zame coat ɗin saman sult ɗinya yay hanging ɗinta. Takalman ma ya zame ya ajiyesu a ma'ajiyarsu ya saka Slippers ɗin shiga cikin gidan. Batare da yanzuma yay maganaba ya nunama Khalipha hanya alamar suje.

       Tunda suka shigo falon idon Hajiya iya na a kansa. Shima inda take ya nufa kai tsaye, batare da yayi maganaba ya zauna kusa da ita yana sauke numfashin gajiya da lumshe idanunsa. Hannunsa hajiya iya ta kamo cikin nata tausayinsa da ƙaunarsa na ratsata. Batare da ta damu da sanin matsalarsaba ta fara magana cikin lallashi.

        “Bansan yaushe ka fara zama mai rauni hakaba Moddibo? Dan nidai moddibo dana sani ada mai yawan haƙurine da juriya da kawaici akan al'amuran rayuwa. Sannan ba komai yakema zafi ba sai yayi nazari akansa”.

       Lumsassun idanunsa dake cike da gajiya dason yin barci ya buɗe yana ɗagowa zaune sosai, ɗayan hannunsa ya ɗora kan nata yana dubanta cike da sonta da ƙaunarta. cikin muryarnan tasa mai tarin kamala da rashin sakewa yace, “Har yanzu Moddibonki na a yanda kika sanshi Granny. Abinda kike tunanin ba shine damuwarsa ba”.

       “Miye damuwarka idan ba matsalar matarkaba to Moddibo?”.

       “Haba Granny, ni yanzu har akwai wata matsala ta Farah da zata sakani a matsala? Wlhy sam ba itace tushen damuwataba. Ɗazunma ta taka sahun ɓarawone kawai shiyyasa kika ganni kamar a cikin zafi. Wani ɗan matsalane akan business insha ALLAH kuma komai zai dai-daita ki tayani addu'a”.

      Sosai Hajiya iya ta gamsu da maganarsa. Dan tasan shi mutumn kai tsaye da bai iya ɓoye-ɓoye ba ko ƙarya akan abinda ba haka yakeba. Tunda yace ba Farah bace matsalar da gaske ba itaɗin baceba. Ajiyar zuciya ta sauke tana sake kammo hannun nasa cikin nata. Da kulawa tace, “Muna muku addu'a a koda yaushe Moddibo, kuma zamu ƙara insha ALLAH. Duk wanda ya manta da ALLAH shike ambato yaya zaiyi”.

        Murmushi yayi dake bayyanar da gajiyarsa mai sanyi, ya jinjinama Hajiya iya kai yana duban Khalipha dake murmushi shima, “Hakane Granny, shiyyasa a koda yaushe nakeson kasancewa a tare dake. ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsahon rai mai amfani”.

        “Amin ya rabbi”. Ta faɗa tana murmushin itama da shafa kwantaccen sajensa.

      Mikewa yay yana faɗin, “A gajiye nake Granny, bara naɗanje na kwanta ina baƙin naki ne?”.

       Khalipha ne ya bashi amsa da cewar, “Tab Yayanmu ai duk sunyi barci. dan Beauty ma da tafi kowa ragantaka tariga kowa kwanciya”.

       Kallon Khalipha yay gira a ɗage kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa. Gaba yay a binsa murya a cinkushe yace, “Sai da safenku nidai nayi ciki”.

      Da ALLAH ya tashemu lafiya suka amsa Hajiya iya na nufar ɗaki, shima Khalipha sai ya miƙe ya nufi nasa ɗakin bayan ya kashe komai na falon.

 

 WASHE GARI

        Hajiya iya ce ta tashi su Bahijja da ƙyar domin yin sallar asuba. Dan har yanzu akwai tarin gajiya tattare dasu. Suna idar da sallar ma tsaresu tai sukai zaman yin azkar. Kowa yana tura baki gaba yayi sannan suka koma suka sake kwanciya. Bata hanasuba dan tasan akwai su dason barci dama.

       Barcinsu suka sake kwasa sosai, dan basu farkaba sai kusan tara shima hajiya iya ce ta tadasu. Bayan duk sunyi wankan haɗuwa sukai suka gyara ɗakin sannan suka fito falo inda hajiya iya take. Fitowarsu dai-dai da shigowar mai aikin Farah. Cikin girmamawa ta gaida Hajiya Iya. suma su Zinneerah ta dubesu tana musu sannu da zuwa dan jiya tsoron uwar ɗakinta ya hanata musu.

    

 

   ★★

 

         A ɓangaren Farah kuwa. Koda ta fita gidan a jiya kai tsaye gidan Mammah ta tafi, sai dai tayi rashin sa'ar iske Mammah ta wuce ƙasar China jiya akan harkokin business ɗinta. Hakan baisa ta damuba ta shige tsohon ɗakinsu da Adilah tai kwanciyarta. Dan ita tana ƙasar U.S yin wani course na shekara ɗaya da rabi.

      Mama Zaliha da suke kira da Mahma ce kaɗai a gidan, itama Yayace gasu Mammah anan gidan take zaune tun bayan rasuwar mijinta acan Morocco. Takaicin halin Farah yasa taƙi tambayarta miya kawota gidan har sai safiyar yau. Bayan ta idar da sallar asuba ta sami Farah a ɗakin nasu itama ta idar da sallan tana karatun Al-Qur'ani. Zama tai a bakin gado tana kallon ɗiyar ƙanwar tasu da gata ya maidata kamar wata shashasha. Tabbas ta yarda da maganar hausawa da sukance gata mugun ciwo. Dan kuwa shine yayma Farah katutu har bata banbance fari da baƙi a cikin al'amuranta.

         Sai da Farah takai aya sannan ta rufe Al-Qur'anin tana duban Mahma. Cike da girmamawa da shagwaɓanta ta gaidata kamar yanda ta saba. Mahma dake dubanta da kulawa itama tace, “Miya faru kikazo nan kika kwana auta?”.

      Baki Farah ta tura gaba idanunta na cika da ƙwalla. Kanta tsaye cike da gadaranta tace, “Mahma na baro masa gidanne su zauna shi da dangin nasa”.

      “Kimin magana a warware zanfi fahimta fiye da bani ita a dunƙule. Ko kina nufin har yanzu matsalar zuwan Kakar tasane bai kareba kuma?”.

       “Ni bashi bane Mahma, ai nace dai na haƙura wannan, amma yanzu dan tsabar wulaƙanci shine ya ƙara kwaso min ƙannensa da wata yarinya da bansanma miye alaƙarsuba aka kawo batare da ya sanar min zuwansuba”.

      “Humm” Mahma ta faɗa tana murmushi da girgiza kanta. Sai da ta gama yima Farah kallon nazari na kusan sakkani arba'in kafin ta gyara zamanta da ƙyau. “Farah anya kuwa kinsan mikikeyi? Gaki dai mace mai tarin ilimin addini dana boko, wayayya wadda ALLAH yayma baiwa kala-kala da ni'imomi, sai dai kuma shashasha ce. Wai sai yaushe zaki daina biyema Hindatu da Zakiyya ne? Farah kinsan ko muhimmancin nuna darajar dangin miji da mutuntasu ga miji kuwa? Kodan kina ganin kullum Hindatu na aibanta dangin Abdul-Mutallab shiyyasa kike ganinsu kamar marasa daraja a idanunki? Bara na faɗa miki gaskiya idan zaki ɗauka. Hindatu mahaifiyarsa ce, zai iya jurewa ya shanye yakumayi haƙuri akan duk wani tarkace da zata jingina danginsa da shi koda yanajin zafin hakan. Keko matarsace duk da kina ganinku jini ɗaya da kuma fawar da kike samu ga mahaifiyarsa zai iya ajiyeku akansu wlhy. Shin bazaki godema ALLAH da ni'inar da yay miki na samun miji irin Abdul-Mutallab mai kawaici da haƙuri ba. Dan wlhy na tabbatar badan soyayyar da yake miki ko tirsasawar hindatu a garesaba yake ƙyaleki. Haƙurinsa da sanin ya kamatansane kawai ke rinjayarsa wajen baki uziri kafin ki kaisa bangon da bazai iya jurewaba. Idan kuma kikai wasa zakiyi nadama a lokacin da guri ya ƙure miki ki kuma rasa samu damar gyara komai. Saboda zuwan wannan yaran kawai ya isa nuna miki gudin halinki yasa ya guji ya faɗa miki ki sanarma mahaifiyarsa ta hanashi, kinga kuwa sai ki dawo hankalinki da irin masu halinki dan mata da yawa sunada wannan bazan halin shiyyasa da yawa duk son da mazansu ke musu sai kiga yana raguwa harsu fara tunanin ƙaro musu abokiyar zama koda kuwa babu haka a tsarinsu. Ni nasan babu wani ilimin zama da miji da baki dashi Farah. Dan kuwa idan da dama ma sai dai ki koyar da wasu. Amma tun zuwan ƙaninsa gidanku kin watsar da komai na ingatacciyar rayuwar aurenku. Kin maida hankalinki wajen kawo ƙararsa kullum da kushe danginsa da nuna ƙyamatar su kusancesa. Anya baƙya tunanin cewa akwai matsala? Baƙya tunanin hankalinsa zai iya fara karkata bisaga ƙudirin dangin nasa nason ƙara aurensa. Yanzufa cikine dake, amma ki duba ko'a jikinsa. Yanda ya nuna murnarsa da farin cikinsa akan wancan cikin da kika samu ya zube bai nunaba akan wannan. Banama tunanin ya sanar da kowa a cikin dangin nasa, tunda dama wancan karon hanashi faɗa musu kukayi wai sai dai suji kin haihu. Sai gashi baki haihunba kuma sabida ALLAH ya rubuta cikin ba zaunanne baneba. Wlhy ki dawo hayyacinki, ki dawo da ingattacciyar rayuwar aurenki kamar farko domin cigaba da damƙe zuciyar mijinki. Duk wannan gantali da shirmen naki babu inda zai kaiki sai komawa baya a garesa. Dan kullum sabbin halayyarki dusashe taurarenki yakeyi a wajensa. Ki dinga daurewa wajen danne wannan zafin kishin naki da kika gada kodan tsare martabarki. Wlhy duk yanda kuke zaton kunada kishi na damaku na shanye. Amma tunda nai haƙurin zama da kishiyoyi har biyu a lokacin rayuwar aurena ya kamata kuma ku saduda. Dan rayuwarma nawa takene baki ɗaya. Daga randa UBANGIJI ya bukaci ganinka dole ka amsa kiransa koka shirya kobaka shiryaba. Duk wata dukiyarka da suna da ilimi da mulki da nasaba da koma miye da kake takama dasu bazasu amfanar dakai da komaiba sai ƙyawawan halayenka da ibadarka. Dan haka sai kisan inda ke miki ƙaiƙayi kibar wannan shirman da kika ɗakko mara hanyar ɓillewa ki koma Farah ɗinki dana sani ada mai hankali da sanin yakamata akan rayuwar aurenta. Ki kuma tashi ki shirya ki koma gidan mijinki tunkan ya fahimci kinbar gidan. Ki kuma kama kanki akan zaman dangin nasa. Ki kiyayi yawan kawo kararsa dan kina zubar masa da kimarsa a idanunmu alhalinsa dan kece sheɗaniyar. Dan wlhy idan Hindatu ta dawo naji kin kira wayarta akan wata matsalar danginsa da kaina zan saka Abdul-Mutallab ya ƙara aure......”

      Da sauri Farah ta ɗago ta duba Mahma idanunta na kawo hawaye. Mahma tace, “Kalleni da ƙyau da gaske nakeyi, dan ko ita Hindatun sai dai tazama ƴar kallo bareke da kike matsayin ƴa. Idan zakije ki kama kanki kije ki kamasa kafin na saitaki a layin daya dace da ke tunda ke shashash ce. shin gata haukane ma kenan?”.

         Cikin kuka Farah tace, “To amma Mahma shima idan yazo kimasa faɗa ya daina min ihu banaso. Sannan ya daina nunamin kamar danginsa sun fini a wajensa tunda nima dai ƴar uwarsace kuma jininsa mafi kusanci”.

       “Naji zan masa. Amma sai naga gyara daga gareki sannan.”

       “Insha ALLAH zan gyara, kuma zanyi duk yanda kikace”. A karan farko Mahma tai murmushi da kamo hanunta jikinta. Tace, “Yauwa kokefa ƴar albarka. Amma duk kin wani susuata kanki tamkar wata shashasha wadda batasan ciwon kantaba da mutuncinta. Karki sake kiyi saken da Abdul-Mutallab zai kufcemiki dan zaki dawwama a dana sani har ƙarshen rayuwarki kuwa”.

     Kanta ta jinjinama Mahma cike dajin daɗin nasiharta tana kwantar da kanta a bisa cinyarta. Sake kwantar da murya Mahma tayi ta lallasheta sosai da ƙara mata shawarwari sannan ta sakata tai wanka ta shirya, ko breakfast batai zamanyiba ta kamo hanyar dawowa gida zuciyarta fal tsare-tsaren dawowa da martabar aurenta daga yau kamar yanda take ada kafin zuwan Khalipha daya susutata saboda rashin son ganin dangin AK raɓe dashi bisa huɗubar Mammah............

       

     

 

 

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

 

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

 

*_ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_

 

*_ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_

 

*_ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_

 

*_ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_

 

*_ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_

 

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

 

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

 

Kamar haka👇🏻💃🏻

 

Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700

 

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

 

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

 

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

 

*_08085405215_*

 

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

 

  0903 234 5899

 

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

 

*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

*_TYPING📲_*

 

 

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

 

*Page 32*

___________________

 

 

_*LAVENDER RESTAURANT..*_

   _(Palace of mouthwatering food/delicacies)_

 

_IDAN KUKAJI GANGAMI DA LABARI, INA MASU SON INDA ZASU SAMU INGATACCEN ABINCI MAI DADI DA LAGWADA? KAI BA ANAN MUKA TSAYA BA, INA SABBIN AMARE? MAMAs, YAYYU? DA KANNEN MU MASU SON KOYAN GIRKUNAN YAN GAYU NA KASAR NIJERIYA DA KETARE?_

 

_*TO KU MATSO...! AT LAVENDER RESTAURANT GOTS YOU COVERED. ABINCIN KASASHE DA DAMA MUKE KOYARWA,,COME LETS UPGRADE YOUR FOOD TIME TABLE, MATSO KUSA YAR UWA GA DAMA DA ZAKI CANZA YANAYIN ABINCIN GIDAN KI, KOWA YASAN IYA SARRAFA ABINCI NA TAKA RAWAR GANI A GIDAJEN AURE. KAI KO BUDURWA CE INDE KIN IYA GIRKI ZAKIGA KOWA YANA HABA HABE DAKE.._*

 

_*UNCLES, DADDIES, BROTHERS., NEWLYWED HUBBYS..! KU ZO KU YIWA ‘YAYAN KU, MATAN KU DA KANNEN KU RAJISTAR WANNAN HARKA TA KOYAN GIRKI.._*

 

_*Lavender catering school zamuyi practical class. zamuyi 30 dishes continental,snack & desserts, traditional dishes, drink. Fee din 40k NE. phone number WhatsApp and call 09080299283  akwai discount na 5% ga mutum uku farko wadanda sukai register aranakun independence 1/10/2021  to 3/10/2021 Nigeria @ 61_*

 

_*ZA’A FARA CLASSES RANAR 14/10/2021. WATO SHA HUDU GA WATAN OKTOBAR DA MUKA SHIGA YAU._*

 

_*GIRKE GIRKE GUDA 30😫😨AKAN DUBU 40 KAWAI, HARDA BONUS NA SNACKS, DESSERTS, TRADITIONAL AND MODERN DRINK, GARGALIYA DA ZAMANI🥂WATA DAYA CHAS ZA’AYI ANA KOYAN GIRKE GIRKEN. _*

 

_*KU SAKE KARANTA WANNAN BONUS DIN👇🏾RIGIJI GABJI_*

 

_*Nigeria @ 61 _*

_*COOKING COMPETITION!!!_*

 

_*from lavender Catering ina masu son koyon girki ga dama zaku shiga gasarmu ta girki bayan kunyi register damu akan 10k,wanda yazo  na 1zai shiga ajin mu free hade da wasu prize din na 2 da na 3 kuma zasu bayar da rabin kudine  da wasu prize suma saura kuwa  zasu ayi musu ragin 5% da wasu prize wannan gasa zamu yita ranar lahadi ne 3/10/21 zamu rufe registration na gasar ranar asabar_*

 

_*LAVENDER RESTAURANT: NA GARIN KANO, CLASSES DIN AKWAI PRACTICAL AND ONLINE CLASS GA WANDA KE NESA_*

 

____________________

 

 

 

Page 32

 

............Shigowarta gidan yayi dai-dai da dawowar Khalipha daga yo musu takeaway daya fitayi. Kamar koda yaushe shine ya gaisheta sabida halinta nason nuna isa. Koda ta shigo gidan ta kalli ko'ina sai taga yamata yanda takeson tsaftarsa duk da an cika matashi, dan Farah mace ce mai tsafta, sannan duk wani abu da mace keyi dan ganin ta faranta ran miji Farah ta iyashi. Matsalarta kawai zafin kishi da hawa kan karatun su Mammah naƙin danginsa, dan tunda Khalipha yazo gidan ta dainama Adnan mafi yawan abubuwan da take masa na kulawa, ita burinta kawai Khalipha yabar mata gida. Shiko ya fita taurin kai yay kunnen uwar shegu da ita.

         Samun komai yanda takeso yasata batayi ƙorafi ba ta shigo cikin kame kai da tsare gida ta gaida hajiya iya. Yanda take cika da batsewa yasa suma su Jamal gaisheta suna ƙoƙarin kama kansu.

     Ko kaɗan hajiya iya bata nuna mata komaiba ta karɓa mata gaisuwarta hardasu tsokana. Batare data kula tsokanar da Hajiya iyan kemataba ta nufi ɗakin AK tana harar Zinneerah da ƙudirta abubuwa masu yawa akanta. Dan har cikin ranta tanajin kishin zamanta a gidan fiye dasu Bahijja. Bakomai yasata jin sassauci akan su Bahijjan ba sai sanin uba ɗaya suke da AK babu wani maganar aure a tsakaninsu. Sai dai kishin cika mata gida da sukayi. Zinneerah kuwa tasan babu uwar da suka haɗa na shaƙiƙanci shiyyasa takejin zafinta. Itafa sabida shegen kishinta ko ƙawayenta bata yarda su raɓeta balle suzo mata gida. Tafi ganewa ayi catin ko waya yafi sauƙi ƴar nesa-nesa. Suma fahintarta yasasu janye jikinsu gareta suka bita yanda takeso duk da wasunsu ma sunyi aure. Tsaron nata kuma baisa wasu a cikinsu gagarar bibiyar mijin nataba acan waje batare da sanintaba. Danma shi AK ɗin na ƙoƙarin taka musu burki dan ba ɗaukar wargi ko shirme yake ba shima ɗin aƙidarsa tayi yawa.

 

     Tsaye ta samesa gaban Mirror yana fesa turare. Ta bishi da kallo cike da so da ƙauna da kishinsa mai yawan gaske, wanda ita kanta batasan adadinsaba. Sosai yayi ƙyau cikin pitch suit ɗin nasa da suka dace da kalar fatarsa mai sheƙi da ɗaukar idon mai kallo. Ga abu mafi soyuwa a gareta tare dashi shine kwantaccen sajensa da sumar kansa dake dai-dai misali dan ba tarata yayba da yawan tsiya. Tana nan dai-dai misali.

    Duk da yaji shigowar tata bai fasa abinda yakeyiba. Sai da ya ajiye gwangwanin turaren ya gyara zaman tie ɗinsa sosai da ƙara kwantar da sajensa sannan ya juyo gareta yana zuba mata manyan idanunsa masu cikar gashi da haske. Gasu da kwarjini masha ALLAH tamkar ba namiji ba. Haddace kowanne kalar kallonsa da ma'anarsa ya sakata risinar da kanta ƙasa. Kafinma yay magana tace, “I'm very sorry, bada niyyar kwana najeba zazzaɓine ya rufeni acan ka tambayi Mahma ma”.

         Janye idanun nasa yayi kawai yana girgiza kansa. Ya ɗauka agogonsa ya hau ɗaurawa batare da yace mata komaiba. A hankali ta tako garesa tana kama hanun da ɗage wanda yake ƙoƙarin ɗaura agogon dashi. Sakar mata yayi babu musu ta ƙarasa saka masa. ta sake ɗaukar wasu kalolin gwangwanayen turaren ta fesa masa tana ɗan murmushi, kafin kuma ta rungumesa cike da so da ƙaunarsa.

       Ajiyar zuciya suka sauke a kusan tare. Ya lumshe idanunsa da zagayeta da hannayensa shima yana lumshe idanunsa. Dan da gaske shima yayi kewar tata. Tunda suka dawo daga 9ja taƙi kwantar da hankalinta waje guda ta nutsu kullum da shirmen da take tashi musu dashi a gidan. danma wani abun tana shakkarsa shiyyasa take tsoron aikatawa. Fatan da addu'arsa shidai dama a kullum ALLAH ya gyarata ta koma Farah ɗinta daya sani ta baya mai tattalinsa da son farin cikinsa akoda yaushe.

      Ɗagota yayi yana mai tsare ƙyaƙyƙyawar fuskarta da kallo mai cike da ma'anoni masu yawa. “K baki gajiya dakai ƙarar mutane kullum wajen iyayenki?”.

       Cikin marairaice murya da shagwaɓa duk da ranta fal yake da tsantsar takaicin zaman su Hajiya iya gidan ta sake narke masa. “Ai dai nace kayi haƙuri, kuma kaima kasan a yanayin da nake shiyyasa nake shiga saurin fushi”.

        Kansa kawai yaɗan rausayar yana sauke idanunsa akan cikinta. Sai kuma ya ɗaura hannunsa saman cikin  tare da ranƙwafawa ya sumbacesa sannan ya ɗago. “Dolene inzo naima babyn nan gargaɗi ya bar rikitamin ke kina bani ciwon kai”.

      Karan farko tai ƴar dariya da sake rungumesa tana maijin tsananin daɗi. Dan tunda ta samu cikin nan bai taɓa nuna kulawarsa kamar ta yau ba. Kodan ta kasa kwantar masa da hankaline oho, dan wancan cikin daya zube lokacin da aka sanar masa da samuwarsa tamkar zaiyi hauka dan daɗi, yabi ya rinƙa tattalinsa da nuna zaƙuwar ganin ya fito duniya. Daya zube ɗin kuwa hardasu ƙwalla yayi, yabi ya shiga damuwa sosai, sai zuwan Khalipha gidan ne ya sakashi komawa normal life ɗinsa. yayinda ita kuma suka fara samun matsala daga nan.

        Shima ƙaramar dariyar yayi yana ɗagota. “Uhm kinga barni naje mu gaisa dasu Granny inada meeting 11am”.

     Duk da zuciyarta ta sosu da zancensa sai ta daure ta kanne, koba komai anci mata lokaci ai tunda gashi lokacinta sai ta raba dasu. Da basa gidan kuwa itace zata kasance da shi har lokacin fitar tasa ta cika. A tare suka fito dan tayi alƙawarin sai dai suci lokacin nasu tare itama dan bazata barmusu ba.

 

         A dining suka iske su Hajiya iyan zasuyi zaman karyawa da abincin da Khalipha yaje ya sayo.  Mai aikin Farah kuma ta shirya musu shi a dining tamkar a gidan aka girka shi. Khalipha na daga tsaye bayan Granny suna magana dan shi fita zaiyi. Juyowa yay saboda jin ƙamshin turaren yayan nasu da takun sa da baya ɓoyuwa ga duk wanda ya sanshi. “Barka da asuba Yayanmu”. Ya faɗa dai-dai suna ƙarasowa wajen.

        Hannunsa AK ya kamo cikin nasa yana faɗin, “Halan yanzu ka tashi kake kiran asuba likita?”.

      Fuskar Khalipha da murmushi yace, “Ai ni harma fita nayi naga gari Yayanmu, kai nedai nake tunanin yanzun ka tashi shiyyasa na faɗa”.

        Kafin AK ɗin yace wani abu Granny dake kallonsu cike dajin daɗi da sha'awar yanda shaƙuwarsu take wanzuwa cikin ƙanƙanin lokaci tace, “Ni nama zata yau bazai fitaba ganin har wannan lokacin bai fitoba. Bayan kuma nasansa shi baya saɓa lokaci”.

        Kallonsa ya maida ga Hajiya Iyan tare da jan kujerar kusa da ita ya zauna. “Yau meeting kawai nake da shi Granny shiyyasa na koma barci bayan sallar asuba. Ina fatan kin tashi lafiya?”.

        “Lafiya lau na tashi, sai dai waɗanan akkunayen da suka cikani da surutu jiya”.

      “Ai kece kika gayyatosu”. Ya bata amsa idonsa na sauka akan Zinneerah dake facing kujerar daya zauna. Tun zuwansa wajen tai ƙasa da kanta tana juya cokalin hannunta cikin abincin da sam ba daɗi yake mataba, wai a hakanma sai da Khalipha ya zaɓo musu wanda yasan zasu iyaci suji daɗinsa tunda ba sabawa sukai da abincin nan ba.

       Janye idanun yayi cike da basarwa yana ɗaukar tea ɗin Hajiya iya ya fara sha. Hakanne ya bama Jamal damar fara gaidashi. Sai Meenal ma ta gaisheshi. Itama Bahijja haka. Zinneerah ce ƙarshen gaishesan batare data yarda ta kalli inda yakeba.

     Dukansu amsa musu yay kamar yanda ya saba cike da rashin sakewa. Hakan da yayi yayma Farah dake bayansa tsaye daɗi, tai wani ƙasaitaccan murmushi da ɗora hannunta kan kafaɗarsa tana sake matsowa jikinsa. Cike da yanga da ƙasaita tace, “Za kaci wani abune anan ɗin?”.

      “No, shayin Granny kawai ya isheni”. Daga haka ya maida hankalinsa kan hajiya iya ya fara magana ƙasa-ƙasa batare da kowansu yaji mi yake faɗa ba. Hakan kuma sai ya soki zuciyar Farah tabar wajen fuska a haɗe. Khalipha ya danne dariyarsa da ƙyar yana binta da kallo, tana gab da shigewa yace, “Kunga nikam bara na wuce school zanyi latti”.

      Ɗagowa AK yayi ya dubesa. “No ka jira na kammala mu wuce tare kusa da school ɗinku zanje nima”. “Okay thanks you Yayanmu”. Khalipha ya faɗa yana jan kujerar data rage ta dining ɗin ya zauna.

      Farah ko dake ƙoƙarin shigewa ɗakin jin zancen nasu ya sakata dakatawa. Kamar zata juyo sai kuma mita tuna oho mata ta cigaba da tafiya harta shige ɗakinta tana taunar lip ɗinta na ƙasa da ƙarfi.

    Sosai zamansa shi da Khalipha a wajen ya saka Zinneerah shiga takura, garama Khalipha tana ɗan sakewa da shi. Amma wannan shugaban tsare gidan da ƙasaitar gaba ɗaya tare mata iska yake idan yana a waje. Sai dai kuma takan tsinci kanta cikin jin daɗi dan tana kallon little ɗinta tattare da shi. Yanzunma murmushi ta sake a bazata saboda faɗo mata a rai da Little yayi, dan hutun nan na kwanaki huɗu da tayi ba ƙaramin shaƙuwace ta sake shiga tsakaninta da yaron ba. Har takai tanajin kamar ta ɗakkosa su taho tare.

    AK da sarai yaga murmushin nata ya ɗan kafeta da kallon sakanni a kaikaice ya ɗauke kansa, a ransa kuwa tambaya yake komi ya bata suga?. Baida mai bashi amsa dan haka ya miƙe dayin ɗan hugging Hajiya iya ta gefe ya sumbaci hannunta daya kamo. “Kimin addu'ar cin nasara, dan zamane mai muhimmanci zanje Granny”. Ya ƙare maganar idanunsa na faɗawa cikin na Zinneerah data ɗago a bazata. Yanda ya juya idanun da wani salo ya sakata saurin maida nata ƙasa ta risinar zuciyarta na matuƙar harbawa.

      Kasancewar babu wanda ya lura da abinda ya faru suka rakashi da addu'ar samun nasara harsu Jamal. Zinneerah dai akan laɓɓa ta fisgo tata addu'ar da ƙyar ta furta. Hayanr fita ya nufa yana saka rigar sanyinsa a saman suit ɗinsa fuska ɗauke da wani ɓoyayyan munafikin murmushi.

 

     Suna ficewa Zinneerah ta saki ajiyar zuciya. A take su Jamal duk suka kalleta. Hajiya iya kuwa ta saki wata ƴar dariyar data basu mamaki itama, sai dai koda suka maida dubansu gareta sai ta basar. Babu wanda ya sake magana dan dokace hakan ga Granny indai anacin abinci. Sai da suka gama ita dasu Bahijja suka gyara wajen domin taimakawa mai aikin da suke ganin kamar aikin gidan ya mata yawa saboda ƙaruwarsu.

 

     Yau ma dai hirarsu suka sha tare da kakarsu. Daga ƙarshe Zinneerah ta bama Hajiya iya tsarabar mmn sadiq tare da saƙon zungureriyar wasiƙa da batasan ta micece ba itama. Hasalima sai yanzu da ake buɗe kayan duk suka gani. Jamal ya ɗauka zai buɗe Hajiya iya ta girgiza masa kai da amsa.

     Babu musu ya bata. Koda ta amsa itama sai ta miƙe taje ta adanata dan tanaji a ranta abune mai muhimmanci a ciki mmn sadiq ɗin ta rubuto, dan dama ɗazun da sukai waya da Baffah yake sanar mata Abbansu Sadiq ya sanar masa yanason ya bashi lokaci zaije har gida suyi wata magana mai muhimmanci. Amma shi yanata juya abin a ransa da tunanin wace maganace haka? Shiyyasama ya sanar mata.

   To a yanzu ganin wannan wasiƙar ya sakata jin maganar da Abban zai faɗama Baffah lallai tanada alaƙa da takardar kenan. Wannan hasashen ya sakata adana takardar sai ta nutsu sannan ta duba dan itama tayi karatun boko duk da bamai tsaho bane a wancan lokacin iyakartama firamare aji biyar aka aurar da ita...............

      

  

 

 

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

 

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

 

*_ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_

 

*_ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_

 

*_ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_

 

*_ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_

 

*_ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_

 

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

 

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

 

Kamar haka👇🏻💃🏻

 

Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700

 

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

 

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

 

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

 

*_08085405215_*

 

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

 

  0903 234 5899

 

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

 

*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

 

          

  *_TYPING📲_*

 

 

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

 

*Page 33*

___________________

 

 

_*LAVENDER RESTAURANT..*_

   _(Palace of mouthwatering food/delicacies)_

 

_IDAN KUKAJI GANGAMI DA LABARI, INA MASU SON INDA ZASU SAMU INGATACCEN ABINCI MAI DADI DA LAGWADA? KAI BA ANAN MUKA TSAYA BA, INA SABBIN AMARE? MAMAs, YAYYU? DA KANNEN MU MASU SON KOYAN GIRKUNAN YAN GAYU NA KASAR NIJERIYA DA KETARE?_

 

_*TO KU MATSO...! AT LAVENDER RESTAURANT GOTS YOU COVERED. ABINCIN KASASHE DA DAMA MUKE KOYARWA,,COME LETS UPGRADE YOUR FOOD TIME TABLE, MATSO KUSA YAR UWA GA DAMA DA ZAKI CANZA YANAYIN ABINCIN GIDAN KI, KOWA YASAN IYA SARRAFA ABINCI NA TAKA RAWAR GANI A GIDAJEN AURE. KAI KO BUDURWA CE INDE KIN IYA GIRKI ZAKIGA KOWA YANA HABA HABE DAKE.._*

 

_*UNCLES, DADDIES, BROTHERS., NEWLYWED HUBBYS..! KU ZO KU YIWA ‘YAYAN KU, MATAN KU DA KANNEN KU RAJISTAR WANNAN HARKA TA KOYAN GIRKI.._*

 

_*Lavender catering school zamuyi practical class. zamuyi 30 dishes continental,snack & desserts, traditional dishes, drink. Fee din 40k NE. phone number WhatsApp and call 09080299283  akwai discount na 5% ga mutum uku farko wadanda sukai register aranakun independence 1/10/2021  to 3/10/2021 Nigeria @ 61_*

 

_*ZA’A FARA CLASSES RANAR 14/10/2021. WATO SHA HUDU GA WATAN OKTOBAR DA MUKA SHIGA YAU._*

 

_*GIRKE GIRKE GUDA 30😫😨AKAN DUBU 40 KAWAI, HARDA BONUS NA SNACKS, DESSERTS, TRADITIONAL AND MODERN DRINK, GARGALIYA DA ZAMANI🥂WATA DAYA CHAS ZA’AYI ANA KOYAN GIRKE GIRKEN. _*

 

_*KU SAKE KARANTA WANNAN BONUS DIN👇🏾RIGIJI GABJI_*

 

_*Nigeria @ 61 _*

_*COOKING COMPETITION!!!_*

 

_*from lavender Catering ina masu son koyon girki ga dama zaku shiga gasarmu ta girki bayan kunyi register damu akan 10k,wanda yazo  na 1zai shiga ajin mu free hade da wasu prize din na 2 da na 3 kuma zasu bayar da rabin kudine  da wasu prize suma saura kuwa  zasu ayi musu ragin 5% da wasu prize wannan gasa zamu yita ranar lahadi ne 3/10/21 zamu rufe registration na gasar ranar asabar_*

 

_*LAVENDER RESTAURANT: NA GARIN KANO, CLASSES DIN AKWAI PRACTICAL AND ONLINE CLASS GA WANDA KE NESA_*

 

____________________

 

 

*Page 33*

 

............A ɓangaren Farah kuwa tabbas a cikin tsananin tashin hankali take. Tana ƙoƙarin dannewa ne kar a samu matsala. Amma lallai zuwan waɗannan yaran gidan nan bazai haifar da ɗa mai ido a gareta ba, dan bawai zuwan nasu bane kaɗai matsalarta. Wannan itace dai-dai gaɓar da zata nisanci gidan nata da mijin ma ta koma zaman Morocco saboda killace ɓoyayyen sirrinsu, dama shirin yanda zasu saka AK maida Hajiya iya Nigeria sukeyi da zaran Mammah ta dawo daga China, sai gashi kuma wasu sun ƙaru. Gashi batama san iya adadin kwanakin da zasuyi ba. bata kuma san randa itama Mammah zata dawo ba.

    A take hawaye masu zafi suka silalo mata. Ta jawo wayarta domin ƙara gwada kiran Aunty Zakiyya. Tun jiya take nemanta amma wayan yaƙi tafiya. Ta tura mata saƙo babu reply. Yanzunma dai switch off.

     ‘Na shiga uku ni Farah, aunty ina kika shigane dan ALLAH?’. Ta faɗa a fili hankalinta na sake tashi. Har zatai wurgi da wayar sai wani tunani yazo mata. Cikin hanzari ta shiga fara neman babbar ɗiyar aunty Zakiyya. Cikin sa'a kuwa sai ga tata ta shiga. A take bakinta ya washe da murmushi, taja wani dogon numfashi ta fesar da ƙarfi.

         Ana ɗaga wayar ko amsa sallamar yarinyar batayiba tace, “Ameera ina aunty?”.

       Cike da shagwaɓa Ameera tace, “Aunty tana ɗaki, yanzu suka dawo daga Niger ita da Daddy”.

        “Niger kuma? Kinga kaimata wayar”.

        Ameera ta nufi ɗakin mamanta tana cigaba dama Farah surutun da ba fahimta takeba sam, burinta kawai taji muryar Aunty......

     “Assalamu alaiki auta”.

Muryan Aunty Zakiyya ta katse mata tunaninta. Batare data amsa sallamarba ta fara magana, “Aunty ina kika shiga kwana biyu, damuwa na nan zata kasheni lokacin mutuwata baiyiba. Wlhy akwai matsala babba aunt, muna kukan targaɗe ga kuma karaya ta samu”.

       Babu shiri aunty dake kwance tana hutun gajiyar da suka kwaso a hanyar Niger ta miƙe zumbur tanama Ameera nuni data je. Koda Ameera ta fita ƙofar ɗakin ta murzama key kafin tace, “Auta miya faru?, kinsa zuciyata na neman bugawa wlhy”.

      “Wlhy aunty ni tawama saura ƙiris ta buga. Muda muke burin tafiyar tsohuwarnan jiya sai ga wasu huɗun sun ƙaru, harda shegiyar yarinyarnan data tureni naji ciwo, aunty kinsanfa wannan watanne ya kamata na taho nan ko naje Morocco.......”

        “Kinga nutsu kimin bayani yanda zan fahimta Farah, wai ƴan gidansu ne suka sake zuwa nan london ɗin?”.

      “Eh”. Ta bata amsa tana jan numfashin kuka. Kafin ta faɗa mata duk yanda sukai dashi akan zuwan su Zinneerah.

         Itama kanta Auntyn hankali tashe tace, “Aiko bazai yuwuba Farah, kinsan dai wannan shine wata na biyar da samuwar cikinki, ya kuma zama dole kibar London dan Abdul-Mutallab ba mahaukaci bane ba. Yanzu babbar matsalarmu da Mammah bata nan, amma na tabbata itama ai lissafin cikin naki na'a ranta bazata wuce satin nanba zata komo nan london ɗin, ki kwantar da hankalinki karki ja ya fahimci wani abu. ko ita tsohuwar ta fahimta”.

        “Aunty taya zan kwantar da hankalina. Wlhy na mugun tsanar yarinyarnan da har yanzu bansan alaƙarsu ba. Dan inaji a jikina akwai aure a tsakaninta da shi, n.......”

       “K dalla rufama mutane baki, wai ke Farah wace irin banzar yarinyace. Ana ga yaƙi kina ga ƙura. Ki fuskanci abinda keda muhimmanci a gareki kin wani zauna tunanin kishin banza da wofi akan yarinyar da ƙilama bata ishesa kallo ba, cayay miki yana sonta ne? Haba dan ALLAH, kishin nan duk muna dashi muma dan ya zame mana tamkar gado, amma ke kam naki ya fara zama na hauka dan kina gaurayashi da zargi. Inda Abdul-Mutallab zai ƙara aure na tabbatar da tun sanda ake dabin ya ƙara tunda baƙya haihuwa daya ƙara ai. Amma yanzu ki maida hankali wajen abinda zai kawo miki mafita kinama mutane shirme bayan ke da bakinki kince yarinyar bama ta wuce shekara sha bakwai ba. Ubanmi zaiyi da sa'ar Ameera shida ke da ke mtsoww, ni kinma bani haushi wlhy sai anjima”. Ta ƙare maganar da yanke wayar.

        A fusace itama Farah tai wurgi da wayar tata zuciyarta na mata zafi da maganganun auntyn ta. Miye laifinta idan tayi kishin mijinta? Ta yaya zata kasa fahimtarta bayan tasan ƙudirin waɗan nan mutanen akanta, ƙilama da biyu suka ɗakko yarinyar suka ajiye saboda mijin nata. Su dan basusan halin wannan munafukar tsohuwar dake nuna kamar bata gane komai amma tsaf idonta buɗe yake. Ita zama ta iya cewa a wajenta AK ya gado nuna halin ko in kula akan abu koda kuwa yana sane.

     Haka ta cigaba da kai kawo a ɗakin har tsahon lokaci duk da tana jiyo motsinsu da hirarsu a falo taƙi fita.

 

   

 

   A ɓangaren su Hajiya iya kuwa babu wanda ya damu da rashin sake ganin Farah a gidan. Hirarsu suka sha yau ma, salla kawai ke tashinsu har Khalipha ya dawo musu da abinci shima ya zauna aka ɗaura hirar da shi. Babu jimawa shima AK ya dawo gidan. Koda ya shiga yayo wanka shima dawowa yay cikinsu ya zauna ransa fes da farin cikin ganinsu cike da gidansa, abinda yayta fata da mafarkin gani a shekarun baya amma hakan bata kasanceba sai yanzun, duk da ba saka baki yake a hirarba sai ya gadama zaka fahimci yana tare da jin daɗin zaman. Hasalima aikinsa yaketa famanyi a lap-top kamar baya a wajen. Dan shima rashin ganin gilmawar Farah a gidan yasashi tunanin ko bata nan.

         Sai kusan gab da magriba sai gata ta fito da alamun barci ta tashi. Sosai yake binta da kallon mamaki. Itako tayi kicin-kicin da fuska cike da takaicinsa. Kenan har takai ya dawo gidan bazai nemetaba saboda yana tare da ƴan uwansa. Batare da tayi magana ko kula gaisuwar dasu Meenal ke mataba ta juya ta koma ɗakinta hawayen takaici na zubo mata. Da kallo duk suka bita harta shige.

      Fuskarsa na nuna alamun ɓacin rai yace, “Dama tana gidan?”.

     Babu wanda ya iya bashi amsa a cikin su Jamal. Sai Hajiya iya ce tace, “Nima duk zatona ta fice ai, dan tunda kuka bar gidannan wani cikinmu baiji ko motsinta ba. Lafiya kuwa take Moddibo? Ya kanata kaje kaji”.

       Maida kansa yayi ga aikinsa yana gyaɗama Hajiya Iya kai kawai, dan shi bazaiso ɗan sauran mutuncinta ya ƙarasa zubewa a idonsu ba. cikin son danne takaicinsa dason rufa asirinta,  Ya miƙe yana faɗin, “Inaga to jikin natane babu daɗi. Granny wannan babyn naku na bama matata wahala ya kamata ku tsawatar masa”.

      “Kai kai Moddibo kana nufin ciki ne da ita?”. Hajiya iya ta faɗa cike da zumuɗi saboda jin firucinsa.

    Ƙayataccen murmushi ya saki yana kallonta. Hakan da yayi ya saka su Bahijja miƙewa suka hau murna da rawa. Yanda sukai ɗin sai ya sakashi jin ƙarin daɗi a cikin rai, a bazata suka haɗa ido da Zinneerah da take murmushi har haƙoranta na bayyana, ita dai tana daga zaune bata tashiba. Saurin maida nata idanun tai ƙasa tsigar jikinta na tashi, dan yanda yay murmushin ba ƙaramin sake fiddo kamanninsa da Little yayiba. A hankali shima ya janye nasa da raɓasu ya wuce zuwa ɗakin Farah ya barsu hajiya iya na jero godiya ga ALLAH da kirarin farin ciki Khalipha da Zinneerah na amsa mata da amin. Dan su Bahijja shirmen da suke na murna yasa bajin mi hajiya iya take faɗa sukeba.

        Sai da suka bari yaja wasu ƴan mintuna da shiga sannan suka miƙe suma domin zuwa dubata. Sallama suka farayi ya amsa musu da cewar su shigo sannan suka shiga. kusan Zinneerah ce ƙarshen shigowa.

     Farah na kwance a gadon. shi kuma yana zaune kusa da ita gab hannunta cikin nasa. Dan tunda ya shigo zuciyarta ta bata shawaran cewar tai amfani da wannan damar kawai tace bata da lafiya. Hakanne kawai mafitarta gudun samun matsala. Sai kuma akai sa'a shima ya shiga tambayarta mike damunta? Shine ta sanar masa da zazzaɓi ta yini da ciwon kai. amma tasha maganin da Doctor ya bata.

       Kukan da tasha yasa idanunta kumbura dama gata fara. Ta ɗagosu da ƙyar tana ɗan dubansu da amsa sannu da addu'ar da suke mata. Koda idanunta suka sauka akan Zinneerah dake can ƙarshe bayan Khalipha sai da taji wani tuƙuƙin baƙin ciki. Ta janye idanunta dake sake cikowa da ƙwallar jin kishin kasancewar yarinyar a garesu, tanajin tsoron ganin wata mace da aure zai iya shiga tsakaninta da mijinta ta raɓesu, shiyyasa zaman Zinneerah a gidan yafi na kowa damunta a yanzu........

      “Da alama ma dai yinin yau bakici komaiba?. ko kina da buƙatar wani abune a nema miki ƴar albarka?”. Maganar hajiya iya dake shafa mata kanta ta dawo da ita hankalinta. Kafin tace wani abu AK dake jin daɗin kulawar da Hajiya iyan ke nunawa akan matar tasa yace, “Nima abinda nake mata magana kenan kafin ku shigo, ya kamata ko tea tasha”.

      “Banajin cin komai ne ALLAH”. Ta faɗa a hankali cike da shagwaɓa tana kallon AK ɗin da shima ita yake kallo har yanzu hannunsa cikin nata.

       “A'a bazai yuwuba Farah. Zinneerah jeki ki haɗo mata ko tea ne da wani abin dan kinfi waɗanan nutsiwar yin abu”.

     Kai Zinneerah ta jinjinama Hajiya iya da nufar ƙofa. Duk da tanajin Farah na cema Hajiya Iyan ta ƙoshi bata dakataba ta fice. Dan ita dai har cikin ranta tausayin Aunty Farah taji ya shigeta. Ta ɗanɗana wahalar ciki tasan mi akeji, shiyyasa da ance ciki na wahalar da mace sai taji tsananin tausayinta.

     Bata wani zaman ɓata lokaci ba ta haɗa tea mai daɗi dan komai akwai, har kayan abinci akwai duk da ba irin wanda suka sani bane, dan mafi yawansu na gwangwanine da sauransu, taɗan ɗiba mata cake da Khalipha ya kawo musu ɗazun ta haɗa dashi ta koma ɗakin.

       Duk suna tsaye har yanzun, batare data yarda ta kalli kowa ba ta nufi gaban gadon, tana niyyar ajiye tiren a ƙasa ya riƙosa batare da yayi magana ba. Ita kuma batai tunanin shiɗin bane dan haka ta ɗago, saurin sakar masa tiren tayi saboda shigewar idonta cikin nasa. cikin ɗan daburcewa ta miƙe daga ranƙwafowar da tayi a gabansu taja jikinta baya.

        Da wani irin tashin hankali Farah ta tashi zaune tana duban Zinneerah ɗin dan komai akan idonta ya faru, zatai magana AK daya gama karantarta yay azamar katseta. Ganin yanda yay da fuska yasata haɗiye abinda tai niyyar faɗa akan Zinneerah ɗin, da wannan damar ya kalleta cikin ido yana jefa mata gargaɗin ki kama kanki.

       Tare da ɗaukar kofin shayin ya miƙa mata. A cinkushe tace, “Ni nace na ƙoshi”.

     “Ni kuma nace sai kinsha”. Ya katseta a kausashe.

     “Haba-haba Moddibo minene abin faɗa kuma anan, kaga bani ni na bata da kaina. Kai sam baka iya lallaɓa mutumba wlhy”. Hajiya iya da batasan dalilin kaushin nasaba ta faɗa. babu musu ya miƙa mata kofin shayin.

        Akan dole Farah tasha shayin da cake ɗin badan tasoba. Dan har wani ɗaci-ɗaci suke mata a maƙoshi. Musamman da idanunta suka sake gano mata AK na kallon Zinneerah da kanta ke a ƙasa tana latsa wayar Jamal hankalinta kwance. Ita kanta da take mace sai da taga annurin fuskar Zinneerah ɗin musamman yanda hasken wayar ya haskata ga kuma wani ɗan murmushi bisa fuskar tata dake da nasaba da abinda take gani a wayar. Itako Zinneerah ba komai yasata murmushin ba sai hoton Little da take gani a wayar Jamal ɗin.

          Khalipha daya fahimci inda Farah ɗin ke duba rai ɓace ya sakashi cewa suje falo, duk da shi baiga kallon da Yayan nasu kema Zinneerah ɗinba sam. Bama shiba kowama ba lura da AK na kallon Zinneerah ɗin yayiba, dan itama ɗin dai shegen zargi dabin ƙwaf-ƙwaf ɗintane ya kaita ga hango abinda yake neman saka zuciyarta bugawa.

     Fita sukai suka barta da hajiya iya da Yayan nasu. Koda suka dawo falonma Zinneerah shigewarta tai ɗaki acewarta lokacin salla yayi. Tanason kuma tayi tilawar karatu yau dan ta kwana biyu batayiba.

      Suma ganin lokacin sallar yayi sai duk basu zaunaba suka nufi ɗaki, har Meenal dake fashi binsu tayi kawai...........

 

    

 

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

 

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

 

*_ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_

 

*_ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_

 

*_ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_

 

*_ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_

 

*_ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_

 

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

 

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

 

Kamar haka👇🏻💃🏻

 

Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700

 

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

 

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

 

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

 

*_08085405215_*

 

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

 

  0903 234 5899

 

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

 

*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

 

*_TYPING📲_*

 

 

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

 

*Page 34*

 

_______________________

 

*Assalamualaikum warahamatullah taala wabarakatuhu*

08121491609

*Aisha s bayero traditional medicine and herbal reaserch center*

08121491609

 

08121491609

1_maganin sanyi

2_maganin niima set

3_maganin nankarwa

4_maganin kiba babba  8kkkarami

5_maganin hips

6_maganin gyaran  nono

7_maganin rage kiba

8_maganin saka feeling

9_maganin cida kwai

10_zuma yar asali

11_maganin basir kowanne iri

12_hodar niiama

13_maganin mallaka

14_gumbar nonon rakumi 10k boket😨

15_gumbar madara 10k boket😨

16_turaren farin jini

17_kaza Mara kwai

18-turaren mallaka 3step

19_hadin matar minister

20_ kaza me kwai 

 

 

 

Step 2

1.Turaren mallaka me kwalba 

2. Me kunama Dan matsi 3k

3.tuaren goshi

4.turaren girji

5.tauwadar Mata

6.memory

7.kahon mallaka 8.yajin maza  tea din maza

9. Dambun matsi

10. Man ayu 11.man  damo pure daga  zuwa sama

12. Kwallin idonka idona

13 garin Sha daka me kyau

14. Kubewar Mata  gasunan dai da yawa bazan iya lisaafawaba harda na kyakkayin cinyoyin da matse matsi kina shafawa zakiji wasai

 

 08121491609

dadai sauransu serious buyer yabiyoni private

me shawara ta bari saita gama karki batamun lokaci plx

**08121491609

 

_________________________

 

 

*Page 34*

 

............WASHE GARI ta kasance babu inda AK zaije. Khalipha ma sai yamma zaije school bakuma zai daɗeba zai dawo. duk sai da suka shiga sukaima Farah sannu da jiki, sai dai kuma hajiya iya yanda taga Farah ragal yau sai abin yaso bata mamaki, gashi ita dai idonta bai gano mata wani alamun mai ciki tattare da Farah din ba, saurin kaudashi tai a ranta da danganta hakan da kowa yanada irin salon laulayin cikinsane. To maybe itama Farah nata salon kenan tunda gashi duk zamanta gidan bata taɓa fahintar Farah na laulayiba sai a jiya. Koda yake bama tasan dai cikin wata nawa bane. Amma da alama dai kamar yanda take hasashe ƙila bazai wuce ɗaya zuwa biyuba.

      Haka taita saƙawa da kwancewa har AK ya fito ya tuna mata yau fa zai kaita taga likita, yama zata zai iske ta shirya. Lallai ta shafa'a da cewar zataje ganin Doctor yau, amma da yake tsaf take dama sai kawai ta saka Bahijja ta ɗakko mata mayafinta a ɗaki. Dan Zinneerah da Meenal suna ɗaki su basu fitoba, dama ita kaɗaice a falon sai Bahijja da Jamal. Khalipha ma duk yau babu wanda ya gansa. Garama su Zinneerah sun fito sun gaida Farah da jiki sun kuma taya mai aikin gidan da aiki.

           Duk da baiga su Zinneerah ɗinba baiyi maganaba, saima kama hannun Hajiya iya da yay suka fice.

 

★★

 

     Bayan tafiyar su Hajiya iya da kusan awa ɗaya da rabi su Zinneerah suka fito, zamansu babu jimawa a falon sai ga Khalipha ya fito riƙe da waya yana magana alamar video call yakeyi. A bayan Jamal yaɗan ranƙwafo yana kanga masa wayar yanda zaiga mai magana. Cike da farin ciki Jamal ya ɗagama Moos'ab hannu yana faɗin, “Hy Yah Moos'ab”.

    Jin haka yasa Bahijja da Meenal tasowa duk suka dawo kusa dashi, suka sakashi tsakkiya Khalipha na bayansu. Duk da Zinneerah na falon ƙin tasowa tai, sai dai yanda suketa surutu da ihu yasata kallonsu tana murmushi, jin kuma suna ambatar sunan little ya sata jin ɗokin ganinshi amma ta kasa tashi taje garesu duk da Meenal nata kiranta. Daga ƙarshe ma saita miƙe ta nufi kitchen da ake hango komansa ta falon saboda da glass kawai aka rabashi da falon, duk abinda kakeyi acan zakaga na falo shima zai ganka. Shayi ta fara haɗama kanta dan yunwa takeji ko karyawa batayiba yau, sam abincin da ake kawo musu gidan baya mata daɗi, balle yau ma mai aikin gida ta haɗa musu breakfast ɗin tunda babu wanda ya fita tsakanin Yayansu da Khalipha masu sayo musun.

      “Gata nan na biyota da wayar ai Yah Moos'ab, kasan mutunuyar taka da miskilancin tsiya”. Ta tsinkayi maganar Bahijja a bayanta.

          Tana juyowa Bahijja ta kamo hannunta ta ɗora mata wayar ta juya tabar kitchen ɗin tana dariyar shakiyanci. Dansu tuni suka fara harbo jigin Yah Moos'ab ɗin akan Zinneerah, sai dai suna tsoron faɗa ya ci musu kaniya.

       Wayar Zinneerah ta ajiye jikin wani ɗan maƙali dake a basket ɗin da kayan shayin ke ciki, fuskarta ɗauke da murmushin jin kunya ta dubi Moos'ab ɗin dake faɗin, “Gimbiya a rage wannan jan ajin mana Please”.

     “Kai Yah Moos'ab wane irin jan aji ana zaune ƙalau, ina fatan kuna nan lafiya?”.

        “Lafiya lau muke, dan ganima tare da Little Handsome tun safe na ɗakkosa daga wajen Gwaggo yau a gidanmu zai kwana insha ALLAH”.

     Idanu ta ɗan waro na mamaki, “Baka tsorin yay muku kuka Ya Moos'ab?”.

     Maimakon ya bata amsa sai ya karo mata fuskar little ɗin yana dariya. “Hy Gentleman kalla Aunty a waya tana maka magana”. Ya faɗa yana sunama little wayan. Ɗagowa kuwa Little dake kokawa da chocolate yayi ya duba wayar, sarai ya gane Zinneerah dan haka ya washe baki cike da ɗoki yake faɗin, “Aunty! Aunty”.

     Dariya sosai ta kama Zinneerah cike da jin daɗin ganinsa mai tsanani, idonta na tara ƙwalla tace, “Uhm su malami an ƙara wayo ashe?”.

     A dai-dai nan Farah ta shigo kitchen ɗin cike da tafiyarta ta ƙasaita da isa. Dama kuma hango Zinneerah a kitchen yasata shigowa dan tanason jamata winning akan shigo mata kitchen. Wani irin mahaukacin bugawa ƙirjinta yayi lokaci guda har takalmin ƙafarta na neman kadata a ƙasa. Tai azamar dafe kitchen cabinet jikinta na rawa.

    Harga ALLAH da farko ta zata AK ne akan waya saboda yanda Moos'ab ya sakama little wayar kusa da fuska sosai, sai dai data ƙara matsowa taga wannan yarone. Amma duk da haka wani irin jiri-jiri taji yana neman kwasarta saboda ganin matsanancin kamannin. Babu wani neman excuse ta ɗauka wayar cikin hannunta tana faɗin, “Wannan yaron wanene haka?”.

       A yanda tai maganar, da tsoratar da Zinneerah tayi dan batasan da shigowarta kitchen ɗinba yasa Moos'ab maido da wayar kansa yana ɗaukar little ɗin yasa bisa cinyarsa tana ganinsu su biyu. Batare da tunanin abinda zai faɗa zai iya zama matsalaba yace, “Hy Auntynmu yaronmu ne. Bakiga yana kama da Yayanmu ba, shi ya haifa muna baku sani ba”.

     Harga ALLAH cike da barkwanci Moos'ab yay wannan furuci, sai dai ya zoma Farah a bahagon tunani, dan babu shiri ta nema sakin wayar a ƙasa sai da Zinneerah ta tarota ALLAH yasa bata kai ƙasaba. Itako a take takai ƙasan saboda santain tiles dana takalmin ƙafarta. Wata irin gigitacciyar ƙara ta saki wadda ta saka su Khalipha da sam hankalinsu baya kansu maido dubansu wajen, kusan a tare suka kwaso da gudu zuwa kitchen ɗin duk da su basajin mi suke faɗa. Ihun Fara ɗinma dan tayi da ƙarfi ne yasa sukajita, gashi kuma tana ta wajen saitin ƙofa ne ma.

      Shigowarsu tayi dai-dai da kaiwar Zinneerah durƙushe kanta, a kuma dai-dai lokacin numfashin Farah ya bar gangar jikinta alamar dai suma tayi. Ƙara ruɗewa Zinneerah tayi ta shiga jijjiga ta tana shafa fuskarta da kiran sunanta. Suma su Meenal duk ƙasa suka kai durƙushe suka shiga taya Zinneerah jijjigata ta.

     Khalipha da shi kansa yake a rikice duk da ya fahinci suma tayi yama rasa taimakon da zai bata, sai da Jamal yay hikimar ciro ruwa a fridge shima a ruɗe ya mika masa sannan.

     Yana ƙoƙarin ɓalle murfin gorar ruwan Hajiya Iya da AK suka shigo. Kuka da ihun su Meenal ya sakasu nufo hanyar kitchen ɗin cike da sassarfa.

     “Ya ilahi, kuko yaran nan miya faru kuka cika gida da ihu haka dan ALLAH?”.  Hajiya iya ta faɗa tana isowa inda suke.

    Khalipha ne dake ƙoƙarin ɓalle murfin goran ruwan har yanzu ya kasa dan tsabar ruɗewa yace, “Granny Aunty Farah ce ta suma wlhy”.

      “Suma?”.

Cewar AK da shima ya karaso inda suke. Ganinta kwance a jikin Zinneerah da har yau take jijjigata tana kuka ita dasu Bahijja ya sakashi tabbatar da e da gaske suman kuwa tayi, amsar ruwan hannun Khalipha ɗin yayi ya zuba a hannu ya ranƙwafo ta bayan Meenal ya shafa mata ruwan akan fuska har bisa hannun Zinneerah dake shafa fuskar tata.

     A take ta kawo wani irin nannauyan numfashi. Ganinsu a kanta ta miƙe a zabure jikinta na rawa. Babu zato babu tsammani sukaga ta cakumi wuyan Zinneerah ta shaƙe. “Tsinanniya matsiyaciya. Dan ubanki yau sai kin faɗamin wacece ke? Ta gidan ubanwa wancan yaron ya zama ɗan mijina kuma?”.

         Wani irin kakari Zinneerah ta shigayi dan ba ƙaramin shaƙa Farah tai mataba, ga Hajiya Iya na ƙoƙarin janye hannunta dasu Bahijja amma sun kasa. Cikin rufewar idanu AK ya sauke mata mari dan ganin tana neman masa kisan kai a gida, bayan yanzu ya gama ganin yarinyar na kuka iya iyawa saboda shigarta wani hali.

     Azabar zafin mari ya saka Farah sakin Zinneerah babu shiri ta ƙwalla wata irin gigitacciyar ƙara da ta sakasu toshe kunnuwansu babu shiri. Banda Zinneerah datai baya ta zube riƙe da wuyanta tana ƙoƙarin jawo numfashi da ƙyar.

     Saurin riƙota Khalipha yayi, yayinda Hajiya iya kuma ta riƙo Farah da take neman fita hayyacinta saboda gigitar mari da abinda kunnuwanta suka jiye mata yanzu a bakin Moos'ab.

      “Wai nikam mike faruwane haka? Farah ki nutsu ki mana bayani, ya mun tafi mun barku lafiya kuma mu iskeku a wannan harmutsatstsen yanayin abin ban tsoro”.

     Kasa magana Farah tayi, sai jikinta ke wani irin rawa ga hawaye na rige-rigen sauka, yanda ta tsire AK da kallo tana sake hango tsananin kamanninsa da yaron ya sake harmutsa tunaninta, sai kawai ganinta sukai a ƙasa ta sake sumewa.

     Sake rikicewa sukai gaba ɗaya, dan shi kanshi yanzu al'amarin nata ya fara bashi tsoro. Duk da yasan halinta ta iya ɗaukar abu da girma amma na yau ɗin kamar yafi na kullum. Hajiya iya ce tace ya ɗauketa suje ɗaki kafin a ƙara saka mata wani ruwan. Baiyi musuba ya ɗauuta gaba ɗayanta zuwa bedroom ɗinta. Hajiya iya da Khalipha ne kawai sukabi bayansu, su kuma su Meenal suka kama Zinneerah suka tayar zuwa falo.   Jamal kuma ya ɗauka mata ruwa a fridge yabi bayansu zuciyarsa fal mamakin miya kawo wannan tashin hankali haka?. Baida mai bashi amsa, bai kuma zaton samun amsar ga Zinneerah a halin yanzun ba.

 

      A can ɗaki kuwa ruwa aka ƙara shafama Farah ta farfaɗo, sai dai tambayar duniya sunyi mata taƙi cewa komai sai uban kuka take dirza. Data kalli fuskar AK kuma ta hasaso ta little sai ta sake fashewa da wani kukan.

       Sanin halin Farah da AK yayi ne ya sashi jan tsaki tare da daka matsa tsawar data sakata shanye gumjin kukan da take ɗin. “Ki nutsu karki maidamu wasu ƴan iska mana, ya ana taroki kina zillewa sai kace wata karamar yarinya?”.

        “Wlhy bazanyi shiru ba, har sai an faɗamin ƴar iskar data haifi wancan shegen yaron da Moos'ab ya kira da naka, har wannan matsiyaciyar yarinyar ke magana dashi ta waya.....”

       A fusace ya zuba mata wani shegen kallo daya sakata haɗiye maganarta babu shiri ta ƙanƙame hannun Hajiya iya dake riƙe da nata. duk da bai fahimci inda zancenta ya dosaba sai da gabansa ya faɗi, juyawa yay ya sauke idonsa akan Khalipha.

      “Mike faruwa?”.

Kai Khalipha ya girgiza masa. kansa tsaye yace, “Wlhy ban saniba Yayanmu, nidai Moos'ab ya kirani ina ɗaki kwance yace na bama su Meenal waya su gaisa. na kawo musu ya gaisa dasu Jamal sai aka kaima Zinneerah wayar kitchen dan tana can kuma tare yake da little. Daga haka bamusan miya faruba sai ihun Aunty Farah mukaji kawai dan ko wucewarta kitchen ma ni wlhy ban ganiba”.

       Batare da yace komaiba ya maida dubansa ga Farah dake kuka har yanzu kamar zata shiɗe. “Meya faru ke da kika shiga kitchen ɗin?”.

        Wani irin kuka ta kuma fashewa da shi, tace, “Miya faru kuwa bayan ganin shegen ɗanka da nayi wanda kake ɓoyemin karna sani, a duk sanda nai maganar kanacin amanata da wasu matan a waje ka balbaleni da bala'in ina zarginka. Sai gashi ALLAH ya tona maku asiri ɗan uwanka yau ya fallasamin, ALLAH ya nunamin shege ɗan ƴar iskar yarinyarnan na waya dashi. Wlhy bansan haka kakeba Abdul-Mutallab, dana gwammaci dawwama banyi aure ba akan ganin wannan baƙar ranar........”

       “Haba kekuwa ƴarnan wane irin kalaman rashin ɗa'a ne haka kike jefar mijinki dasu? Ni wlhy saima yanzu na fahimci daga ina matsalar take, halan yaron nan na wajen Hauwa'u ta gani?”.

          Khalipha ne ya bata amsar cewa, “Eh shine kuwa Granny, dan Moos'ab ne yake can gidan ya ɗakkosa. To inaga sanda suke magana da Zinneerah ita kuma ta shiga kitchen ɗin ta gansu. Amma aunty Farah ya kamata kiyi haƙuri ai miki bayani, yaron nan baida wata alaƙa da Yayanmu sai ta zuminci, kamannine kawai da ga ALLAH b........”

       “Ƙarya kakeyi munafukin ALLAH ta'ala, idan kai kaƙi faɗar gaskiya ai shi Moos'ab ɗin da bakinsa yace ɗansa ne”.

       Hajiya iya da mamakin Farah ke neman kasheta tace, “Shi Moos'ab ɗin ya faɗa miki yaron na Moddibo ne?”.

      A gadarance tace, “Ƙwarai kuwa”.

   Yanda tai maganarne ya saka AK kaima bakinta bugu. sai dai da sauri Hajiya iya ta kare tana faɗin, “Kull da wannan ɗabi'ar, karka sake ka aro halin da ba nakaba kayi haƙuri abi komai a sannu harta fahimta. Kai Khalipha kiramin Moos'ab a waya yanzun nan”.

       Amsa mata Khalipha yayi yana fita falo domin amso wayarsa a wajen su Zinneerah.

 

      Dai-dai lokacin da Khalipha ke ƙoƙarin kiran Number Moos'ab kiran Baffah ya shigo wayar AK. Cike da ƙarfin hali ya ɗaga, sallama yay yana mai ƙoƙarin dai-daita muryarsa dake a cinkushe. Sai dai kuma yanda yaji muryan Baffah sai ya bashi mamaki.

        “Kaga Babana haɗani da Inna”.

“Baffah lafiya kuwa?”.

     “Karka damu lafiya lau, haɗani da ita”.

      Cikin sanyin jiki ya mikama Hajiya iya wayar yana faɗin, “Baffah ne”. Amsar wayar tayi takai kunnenta. Batare da sunsan mi Baffah ya faɗa mataba ta miƙe ta fito daga ɗakin. Hakanne yasa AK miƙewa shima ya fito domin jin ko Khalipha ya samu Moos'ab. Dan shi kaɗai yasan irin hukunci dazai masa idan har yaji gaskiyar zancen.

       Kamar jira suna fita kira na shigowa wayar Farah. Kamar zata share sai kuma ta duba wayar tana sharce hawaye. Wani irin zabura tayi saboda cin karo da sunan Mammah akan fuskar wayar alamar ta dawo kenan..............

 

 

 

*_Hummmm, tofa masu karatu ga wuri fa ga waina. Yanzu aka fara wasan kumuje zuwa😉🐥🐥._*     

       

 

_Kar kuma naji wani yacema aunty Farah wani abu, kokuma na rage mudu ehe_🤒🤕😒☹️😖

 

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

 

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

 

*_ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_

 

*_ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_

 

*_ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_

 

*_ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_

 

*_ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_

 

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

 

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

 

Kamar haka👇🏻💃🏻

 

Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700

 

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

 

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

 

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

 

*_08085405215_*

 

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

 

  0903 234 5899

 

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

 

*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

 

 

          

*_TYPING📲_*

 

 

*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

 

 

*Page 35*

________________________

 

*ZAUREN GIRKI*

 

Abinci na *gargajiya* ...Kuka,Taushe,Danbu, Sinasir,Waina

Abinci na *zamani* ...Afang,Edikaikong, Coconut Rice, Ofada Rice

 *Garabasa* ...Salads,Pancakes, Plantain mosa, Gyaran nama/kifi kafin girki,Shirin/shinfida abinci kan table.

 

• A kowane sati,in shaa ALLAAH, za a koyi miya/abinci daya da kuma wani abu ta karkashin *Garabasa* .

• Duk ranar *Lahadi* za fito da sabobin *videos* guda biyu na miya/abinci da na wani abu daga karkashin *Garabasa* .

• Kowacce daga cikin masu koya zasu bibiya video su kwaykwaya su gwada yin abincin bisa ga umurnin *video*

• Kowane ranar *Asabar* za a yi *Q&A* a inda kowa zai samu yin tambayoyi akan *videos* din satin daya gabata, da inda suke neman karin bayani/gyara akan kokarinsu na gwada abincin *video* da kawunansu

• Ga wace taga dama,daga ranar *Talata* za a iya fara turowan *video* ta kokarin da aka yi na kwoyon abincin da aka kwoyar ta *video* na ranar *Lahadi* .

• Inda akwai me bukatan wani fanni na abinci,ana iya hada *aji(Special Personal Video Classes)* musamman domin wannan bukatan.Anan za a shirya live *video* sessions domin cimma wannan burin

 

• Za a biya dubu biyu *(#2,000)* na watan farko,sannan za dinga biyan dari biyar *(#500)* ta kowane sati ga masu bukatan shiga group dinnan namu mai albarka

• *Zen Commute,account number 0119343451 Union Bank* ,asusunmu

• Duka lokacin da aka biya sai a turomana da hoton teller ko bank confirmation akan wannan number ta *WhatsApp 0817-541-7533*

• Ana iya tuntubammu akan wannan number domin karin bayani; **0817-541-7533(WhatsApp kawai)*                                                                    

ZA MU FARA ZAUREN GIRKI LAHADIN SATIN FARKO TA WATAR SEPTEMBER,IN SHAA ALLAAH!

 

 *MU TSARE MUTUNCINMU,MU KARE MAZAJENMU...MU KOYI GIRKI!!!*

 

_______________________

 

 

*Page 35*

 

............“Babangida duk ka rikitar dani wlhy, gani na dawo ɗaki ni kaɗaice yanzu mike faruwa ne?”. Hajiya iya dake zama a bakin gado ta faɗa.

         Numfashi Baffah ya furzar daga can. Cikin nutsuwa yace, “Inna yanzu muka rabu da mijin Hauwa'u, kamar yanda na sanar miki dama munyi dashi yau zaizo yanada muhimmiyar magana”.

       “Eh ƙwarai anyi haka”.

“Yauwa to Inna, maganar zancen yaron nan ne dai daya tsayamin arai mukayi dashi, ashe yaron ɗan wajen Zinneerah ne”.

      “Uhm ban fahimcekaba dai babangida. Wace Zinneerah kake magana? Inno wai?”.

     “Tabbas ita kuwa”.

Sosai zancen ya daki zuciyar Inno. Har sai da ta janye wayar daga kunnenta ta kalla, ta dai tabbatar da ɗan nata take waya ba wani dabanba dan haka ta mayar. “Babangida tayaya hakan ta faru? Dama Zinneerah ta taɓa aure ne?”.

      “Bata taɓaba Inna. Ƙaddarar rayuwa ce takaita ga haihuwarsa.......   (Anutse ya shiga yimata bayani dalla-dalla kamar yanda Abba ya sanar masa). Sai ga hajiya iya na hawaye shaɓe-shaɓe na tausayi. Dan har cikin ranta tanaji Zinneerah bazata aikata hakan da ganganci ba, dole akwai abinda ya faru dai......

       Baffah ya katse tunaninta da cewar, “Inna harga ALLAH ta ɓoye-ɓoye ya ƙare, shin baƙya wani tunani game da kamannin yaron nan da Adnan kuwa? Adnan ba kama yake da yaran gidannan ba mahaifiyarsa ya biyo komai a kamanni balle muce ƙarfin jini yakai yaron Zinneerah da ɗakko kamannin yaran gidan nan. Shin kodai akwai abinda Adnan ke ɓoye mana ne?. Dan kwanaki sau biyu ana sanarmin shigowarsa Nigeria baizo inda mukeba. Nayi shirune kawai na ƙyalesa dan karna tayar miki da hankali”.

     Babu shiri Hajiya iya ta miƙe tsaye tana ambaton, “Shi Moddibon da kansa?”.

     “Wlhy kuwa Inna, ko lokacin da Khalipha yazo hutu tare sukazo”.

    A take kan hajiya iya ya sake kullewa. Kamar yanda shima Baffah kan nasa yake a kulle. Dan sudai sunyi imani da cewar yanda yaron ya shiga ran kowa a gidan akwai wata a ƙasa. Sannan kamannin kam sunyi yawa, sai dai idan acan kuma dangin hindatu tushen matsalar take ba abinda zukatansu ke karkatar dasu akai bane.

         Hajiya iya da takardar wajen mmn sadiq ta faɗo mata a rai tai masa sallama akan zuwa anjima zasuyi waya bara ta kashe wata wutar.

      Tana katse kiran takardar ta ɗakko a inda ta ɓoyeta, ta sake komawa inda take zaune da ta warware.

 

     *_Assalamu alaiki_*

 

    *Alkairin ALLAH da samuwar lafiya mai ɗorewa su tabbata a gareki Gwaggo. ALLAH ya dawo mana dake gida lafiya*

 

       _Gwaggo zan fara da baki haƙuri akan wani abu da muka ɓoye miki game da Zinneerah, munyi hakanne saboda ba abune mai daɗi ba ko farin ciki. Duk da dama dai munyi niyyar sanar daku ɗin harga ALLAH. Akwai ƙaddarar data faɗama Zinneerah wadda itace tai sanadin dawowarta zama a wajena, dan da tana can wajen mahaifinta da muka rabu...................._       _(Ta bada labarin tun aurenta da baban Zinneerah har bayyanarta da ciki a garesu da haihuwarsa kaf bata rage komaiba. Daga karshe ta ɗora da faɗin___). Yaro da mukazo dashi ranar da yara sukace ƙaninsune shine yaron, sunansa Abdul-Mutallab. Dan ALLAH ku gafarcemu da rashin sanar muku wannan labarin tun farko, bamun ɓoye bane dan bamu yarda dakuba. ALLAH ya hukunta sai yanzune zaku sani kawai. ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsahon rai mai albarka da amfani._

 

        Sosai Hajiya iya taja wani irin dogon numfashi mai tafiya a sarƙe. Ko kaɗan bataga laifin mmn sadiq akan ɓoyewarba. Domin ko itace zata iya ɓoyewar bisa dalilai masu yawan gaske. Abinda kawai yake neman jefa zuciyarta a ruɗani irin wanda Baffaah ya shiga anan uku ne zuwa biyu. Shigowar sunan Khalipha a labarin da taimakon da yay ma Zinneerah a Shira hospital, Kamanin yaron da Abdul-Mutallab, dan wannan kamanni yakai ai zaman dogon nazari akansa.

       Sannan har cikin ranta kuma tausayin Zinneerah da ƙarajin ƙaunar yarinyar ya ƙara faɗi a zuciyarta. Yarinya ƙarama kamar wannan ta fuskanci irin waɗan nan manya-manyan jarabawoyi na rayuwa. Amma abin mamaki ko'a labari bata taɓa nunama waniba, hakan na nufin itaɗin yarinyace mai yawan kamun kai da riƙe sirri, insha ALLAH kuwa zatayi wani abu, sai ta ƙwato mata haƙƙinta, dan har cikin ranta son yarinyar takeyi tamkar nata jikokin........

 

 

  Daga ɓangaren Farah da kiran Mammah ya shigoma a waya. Wani ɗan karan daɗine ya tsarga mata. Tai saurin ɗagawa tana kai wayar kunnenta, dan har cikin ranta tana son Mammah kamar yanda itama take nuna mata soyayya.

       Tana ɗagawa ta fashe mata da kuka, a rikice Mammah tace. “Auta lafiya kuwa? Miya faru da kuka haka ni hindatu?”.

      “Babu lafiya Mammah, ina cikin damuwa da tashin hankali. Naje gidan jiya kawai na tarar bakyanan sai Mahma kaɗai, yau kuma sai ga tashin hankalin da yafi na jiyan ya riskeni”.

       Hankali tashe Mammah tace, “Am so sorry baby na. Ai bazan jimaba zan dawo kodan saboda halin da ake ciki. dan yanzu hakama na kammala tura kaya Morocco. Na Nigeria suka rage kawai insha ALLAH. Amma mi kikajeyi gida? Wane kuma irin tashin hankali kike a ciki?”.

       “Ƙannen Yah Abdull ne suka zo jiya, harda yarinyarnan mara kunya data jimin ciwo a ƙafa. Mammah duk bama wannan ba. Wlhy Yah Mutallab ya haifi yaro da wata a waje kokuma yayi aure a ɓoye bada saninmuba”. Ta ƙare maganar da fashewa da kuka.

        “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Farah wane irin maganane wannan? Ya haifi ɗa da watafa? Ke waya faɗa miki? Wacece ita wadda ta haifi ɗan kuma?” Mammah ta faɗa itama cikin tashin hankali.

      “Mammah wlhy nima ban sanba. Yanzun nan naga yarinyarnan tana waya da yaron da Moos'ab, shine Moos'ab ɗin ya sanarmin yaron na Abdul-Mutallab ne, kinga kuwa indai ba'a waje wata ta haifa masa shiba wlhy aure yayi a ɓoye bamu saniba. Indai hakan ta faru mutuwa zanyi Mammah

         “Kai ina!! Duk rintsi bazan bari hakan ta faruba Farah, dan wlhy har abada bazanyi sakacin da Kabeer zai ƙwacemin Abdul-Mutallab ba. Nayi alƙawarin tarkon da suke ganin zasu ɗana masa ya faɗa bazan bari yayi tasiri ba, dan haihuwarki itace kawai raba gardama a tsakaninmu. Kinga kuwa hakan na nufin babu wata mace data isa zuwa ta haihu da Abdul-Mutallab a ɓoyema ban saniba. ki kwantar da hankalinki yau ɗin nan zan baro china kuwa, dan bani da wata nutsuwar zaman yin abinda nazo yi ɗin”. daga haka ta yanke wayar.

         Faɗawa Farah tai saman gadonta tare da fashewa da kuka mai cin rai, ji take tamkar numfashinta zai rabu da gangar jikinta, dan inhar wannan ɗan ya tabbata na Abdul-Mutallab tasan ita kam rayuwarta tazo ƙarshe. Kenan bayan ita ya taɓa sanin wata mace a duniya? Ya taɓa dai-daita farin cikin da yake bata da wata mace? ‘Kai ina wlhy hakan bazai yuwuba’ ta faɗa a fili tana fashewa da matsanancin kuka ta miƙe ta fito daga ɗakin.

        Ficewa tai daga gidan dan ta rantse bazata sake kwana ba sai Mammah ta dawo sunji daga ina aka samo little. Ko kallon su Zinneerah dake falo zaune Farah batayiba ta nufi hanyar fita abinta.

 

        Da kallo suka bita a tsorace. Cikin damuwa Jamal yace, “Gaskiya Yah Moos'ab baiyi tunaniba, miyasa shima ya faɗi cewar ɗan Yayanmu ne bayan yasan halin Aunty Farah da kishi. Gashi nan wannan maganar dashi yake gani yayi akan wasa gashi tana neman zama babba”.

        Wasu hawaye ne masu zafi suka sake silaloma Zinneerah, dan ita a yanzu damuwarta daban da tasu, bataga laifin Farah ba, dan ko ita data haifi little har yanzu ta kasa fita daga ruɗanin kamannin da yakeyi da Yah Adnan. Balle ita dataga komai sama taka yau, ai komi tayi bai kamata aga laifinta ba.

    Tunda ta haifi little yau shine karon farko data tsinci kanta a matsanancin tashin hankali tun bayan barowarta Danya.

 

     Acan kuwa wajen su Hajiya iya an kira Moos'ab dan yayma Farah bayani akan wasa yake mata, Hajiya iya da Khalipha sun fito dan a bata wayar amma suka samu ta fice. Cikin damuwa suka sake shiga, dan ba ita kaɗaiba harsu Hajiya iya ganin kamannin yaron da AK ɗin sukai sosai fiye da kullum a yau.

 

       Hajiya iya ta dubi Khalipha daya yanke kiran tace, “Ina Moddibon yake harya bari ta fita?”.

    Kansa ya girgiza mata alamar bai sani ba. Sai su Bahijja ne suka sanar mata sungafa kamar ya fita.

      “Fita kuma? To lafiya?”.

Hajiya iya ta faɗa. Khalipha da zuciyarsa ta bashi inda Yayan nasu yake yace, “Granny ina zuwa. Inaga yana baya, kinsan shi idan ransa ya ɓaci yafi bukatar ya killace kansa inda babu hayaniyar komai.

    Batare da ya jira amsartaba ya fita shima. Kamar yanda yayi hasashe acan bayan ya samesa yanata kaikawo hannayensa goye a baya.

      Harya karaso gab dashi baisan da zuwan Khaliphan ba, dan harga ALLAH kamanin yaron da shi ƙara gigitashi sukeyi, zai iya rantsewa tunda yaga yaron nan bai ƙara barci mai daɗi babu mafarkinsa ba. Dauriya kawai yake aɗan tsakanin nan har Hajiya iya ta samu lafiya. Amma da tuni ya koma Nigeria dan kawai yaga asalin mahaifin yaron nan shikam. Sai dai kuma abinda ya faru a yau ya ƙara tada masa tsumin ƙwaɗayin son zuwa Nigeria. Ko ita Farah jin gaskiyar zancen ya sakashi yimata uziri, dan inhar shi da yaron ke kama dashi zai iya rikicewa dolene ita yaga fiye da haka a gareta. Musamman daya santa da shegen zafin kishin tsiya, a yanzu babuma abinda zuciyarta bazata hasaso mataba game da yaron kamar yanda shi kansa duk da ance yaron ɗan Gwaggonsu ne zuciyarsa taƙi samun nutsuwa.

      “Yayanmu”.

Khalipha ya kirashi cike da damuwa. Juyowa yay ya kallesa sai dai baiyi magana ba. Khalipha ya ƙarasa takowa garesa, kansa ya ɗan risinar ƙasa saboda abinda zai faɗa.

         “Yayanmu kayi haƙuri, kar abinda aunty Farah keyi ya dameka. Dan ALLAH kumata uziri dolone ta shiga ruɗani kamar yanda muma ɗin muke a cikinsa tun ganin yaron da mukai a Nigeria, kawai dai ita matsalarta bata da nutsuwar zama ta fahimci abune”.

      Karon farko AK ya saki murmushin ƙarfin hali, hannunsa ya ɗora bisa kafaɗar Khalipha ɗin. “Hakane bestie, Farah ta cancanci uziri a wajenmu, sai dai minene dalilin Moos'ab na cewa yaron nawane?”.

      “Wlhy tsokanarta kawai yake Yayanmu, kasanshi duk da baida yawan magana yanada son wasa. Kuma inaga ya manta bataga yaronba a waccan ranar”.

      Kai AK ya shiga jinjinawa yana sauke nannauyan numfashi, ya sauke hannunsa daga kafaɗar Khalipha yana maidasu bayansa ya harɗe. Taku biyu yayi batare daya juyo ya kalli Khalipha ba yace, “Bestie mi zuciyarka ke baka akan kamannina da yaron nan?”.

       Babu shiri Khalipha ya kalli bayan nasa da sauri, haka kawai yaji gabansa ya faɗi, dan inhar gaskiya zai fito ya faɗa to komaima zuciyarsa na bashi musamman idan tunanin Zinneerah ce mahaifiyar yaron yazo masa arai kamar yanda yake zargi. Baki ya buɗe da ƙyar zaiyi magana Hajiya iya data biyo bayansu ta katsesa.......

      “Wai tsayuwar mi kukeyi anan? Yarinyarnan fa bata gidan nan”.

    Atare suka juyo suna kallonta. Takowa AK yay cikin tafiyarsa da babu gareje zuwa inda take, bai kawo wa take nufi ba dan haka yace, “Wace yarinya Granny?”.

      “Matarka mana”.

Ɓoyayyen numfashi yaɗan sauke, a ransa yace ‘da sauƙi’ tunda yasan dai Farah ƴar garice bazata je wani wajeba sai gidan Mammah.

      “Karki damu Granny babu inda zataje sai wajen su Mammah. Ya kamata mujema kisha maganinki”.

     Daga haka ya kama hannunta suka nufi ciki Khalipha biye dasu. Basu sami su Zinneerah a falonba, sai mai aikinsu dake ƙara gyarawa. Har ɗaki ya raka Hajiya iya, ganin Zinneerah kwance a gado su Bahijja zaune jigum-jigum yasa Hajiya iya tambayarsu ko lafiya?.............

 

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post