A Rubuce Take (K'addarata) page 60 Hausa Novel - Novels Elite

A Rubuce Take (K'addarata) page 60 Hausa Novel - Novels Elite

A Rubuce Take (K'addarata) page 60 Hausa Novel - Novels Elite

H U G U M A


*_A RUBUCE TAKE_*

       (K'addarata)

*Arewabooks:Huguma*


Page 60


        Wuni tayi takaici yana cinta,amma kuma da sukayi waya da anty ummee ta tilastata sakin jikinta


"Ke da kike jira kiji albashiri din tafiya dake,me ya kaiki dukka wadan nan abubuwan,dole ki taushi zuciyarki ki nuna masa komai ba komai bane,kuma kiyi dako kar kiyi gaggawar tambayarsa,ha sai in shi ya gaya miki da bakinsa" da wannan shawarar tayi qoqarin gyara dakin yaran,ta kuma tsallaka taje ta gyara nasa,dukda gyaran nata ba wani na azo a gani bane,amma bahaushe yace da babu gwara babu dadi.


             Cikin kwanakin kuwa ta dunga qoqarin yun dukma abubuwan da tasan yanaso,sai abunuwan nata gaba daya suka zama wanu banbarakwai saboda ba saba yi tayi ba,ita kanta da qyar take kai labari saboda rashin sabo,a wajensa shima abun ya zameasa wani iri,saidai shi din hakan yakeso inda ace zata sauya din.


***********Kwana daya rak amma gaba daya jikinta ya zama week kamar wata mara lafiya,randa ta dawo daga makaranta ma wannan dogon wunin kwanciyar tayi,don haka da dare bacci bacci yayi mata qaura,sai taja wayarta kawai ta soma bin charts na groups din da anty deena ta saka a sanyata,tun abun bai wanu burgeta ko mata dadi har ya fara jan hankalinta,a hankali ta dinga bin topics din da suke tattaynawa daya baya daya,tarin uban saqonni saidai dukkaninsu msu amfani ne ga macen auren dake neman gyara rayuwar aurenta,saidai ga widad fa abun kunya ya zame mata,tana karantawa tana jin kunya ita kadai,musamma idan ta tuna anty deena na ciki.


           Bayan tayi nisa ta soma fahimtar wasu abunuwa da suka sanyata cikin nqzari da lissafi,an gadi abubuwa masu yawa da ita bata sansu ba,kuma kallon iskanci take musu,amma kuma taji suna batun lada,dama akwai lada cikin iskanci banda tarin zunubi?,saita maida wayar ta ajjiye gefe tana tuno wasu abubuwa,ta dinga saqa tana warwarewa,wa zata tambaya wanda zaiyi mata bayanin da zata gane da kyau,ta kuma fita daga shakka?,ita kanta anty deena maganganun da taga tayin sai suka weedad ke tunani a kanta,tasan dai anty deena ba 'yar iska bace,to amma.......


            Katsewa tunanina yayi sanda wayarta ta soma wani qaramun ringing mai dadi,ta kalli wayar,kamar ta gane number din,ta jawo wayar ta daga ta sakata a kunnenta.


            A nutse muryarsa a qasa yayi mata sallama,ajiyar zuciya ta kubce mata ba tare data shirya ba,ajiyar zuciyar data sauka a kunnensa,ta kuma sanya tsigar jikinsa zubawa


"Bakiyi bacci ba?"kai ta gyada sannan ta amsa masa


"Eh"


"Me yasa?" Rasa amsar bashi tayi,saboda dai ba zata iya ce masa ga abinda take karantawa ba


"Me tayin kwanan ta shigo?" 


"Eh" ta bashi amsa,don sai da sukayi sallama da ita sannan ta shigo dakinta,saboda ita a falo take kwana,taqi yarda ta kwana dakin widad din


"Yayi,yanzu gaya min dame dame kikayi yau?" Ya tambayeta yana hangen hafsa daga inda yake zaune cikn falonsa,tana nannade wandon kashin da nawwara tayi tana cusashi qasan kujera,ya dauke kallonsa daga kanta ya maida wani gefin,don bayason ransa ya baci.


            Sosai ta narke cikin pillow din,zuciyarta tana narkewa,kewa tana sake cikata


"Bayan kaine....kaine kayi tafiyarka ka barni" ta fada a wanu kugun shagwabe,abinda yayi masifar tabashi,tsigar jikinsa ta zuba sosai,ita kuwa ko a jikinta,saboda tana ganin tayi maganarta ne sak


"Am sorry......bazan sake ba" ya samu kansa da fadin hakan ba tare daya shirya ba,dai dai sanda hafsat din ta qaraso wajen,sai taji kamar kunnuwanta basu jiye mata dai dai ba,waye yake baiwa haquri wai?,ta tambayi kanta,ta tsaya cak tana dubansa,yayi kamar bai ganta ba,yaja cup din coffe daya hada kafin ya zauna ya kurba kadan


"Yanzu kiyi addu'a ki kwanta,akwai school gobe"


"Tom.....sai da safe?" Ta tambayeshi a sanyaye,saboda har ga Allah hirar ta mata dadi,bataso yace ta kwanta ba.


        Murmushi ya sake kubce masa,a hankali ya furta


"Goodnight" sai ya zame wayar daga kunnensa yana kasheta,dai dai sanda hafsat din ta kasa tsaiwa,ta zame ta zauna a kujerar dame kusa dashi


"Wai da waye kuje waya haka?" Sai daya kashe wayar ya ajjiye sannan ya dago yana dubanta,yadan zuba mata ido na wasu sakanni sannan ya saki murmushi


"Qanwarki ce"


"Qanwata ko kishiyata"shine abinda bakibta taji ya kamata ta furta,to amma tana tsoron kada ta barar da tafiyarta,don haka ta hadiye maganarta,sai gefw da tayi da kanta ta tabe baki


"Dole yarinyar ta dinga tsoronka,ya zaka dinga gaya mata maganganun da sukafi qarfi kanta,a haife fa ka kusa haifarta,tunda ka ninka shekarunta harda doriya" ta qarasa maganar tana dawo da dubanta kansa.


         Fuskarsa a sake,saima murmushi daya saki,ya shafa kanshi zuwa kyakkyawan hanarsa dake dauke da gashi baqi sidik daya sha gyara


"Kinason ki gayamin na tsufa kenan fa"


"Kusan haka ne" ta fada tana tabe baki,a nufinta na zare masa karsashinsa da sha'awar komai,murmushi ya sake saki,abu daya ya sani,komai zatayi ba zataji komai daga bakinsa ba,ta manta wayeshi din wajen riqe sirri


"Ki zaro wancan andon kashin ki fita dashi ki wanke,and please.....kada na ganshi a dustbin" ya maida zancan zuwa wani topic din na daban.


          Kunya da haushi suka cikata,ba wannan batyn takeso suyi ba,ita batasan ma ya ganta ba,maganar gaskiya babu agender din wanke kashi yanzu a gabanta,amma dole ta miqe rana cewa


"Kadai dinga mata a hankali tunda yarinya ce,bawai wani abu zata fahimta daga gareka ba" da kallo ya bita yana son tantance da wanne irin sound tayi masa maganar,sai ya maida nayansa jikin kujera,ya lumshe ido yana maimaita maganarta,abubuwa da yawa sunzo kansa a sannan wadanda suka sanya dole murmushi ya qwace masa.


             Dukka abinda ta karanta a daren washegari ta dunga bitarsu a makaranta,kwatsam ranar sunyi missing periods har biyu,sai ajin ya zamana na surutu da hira,abinda ya sake sanyata daukar wayarta taci gaba da dubawa,saidai tana tsaka da dubawar hirar da 'yan bench din bayansu keyi yaja hankalinta,bata suaje wayarta ba amma ta bada kunnuwanta tana saurarensu,hirace ta aure da yawanci ba'a rasa matasan 'yammata da suke ganun sun fara zama seniors da yinta,fiye da rabin hirar ta zame mata kamar wani mabudi kuma amsa na dukka tambayoyinta,ta dinga saurarnsu tana ciro abubuwa masu yawa tana hadawa cikin maganganun data ji a groups daban daban.


             Koda aka tashi daya daga cikin qawayenta ta bata ajiyar hausa novels


"Ki ajjiyemin don allah widad,yayana yazo gutu,doke sai ya koma zan karba,hanani karatun yakeyi,kada yaje garin bincike bincike ya ganosu na shiga uku" a karba din ta tafi dasu gida,da daddare ta buda jakarta bayan ta gama wani assignment zata maida jakar don kada ta manta idanunta suka gano mata litattafan,saita jawosu ta buda tana kallo tare da mamakin meye a ciki da za'a hanata karabtawa,don ita kallon normal kowanne littafi take masa,taji sha'awar duba meye a ciki,ta dauki daya part one ta buda ta fara karantawa.


          Ko page daya bata dauka da niyyar karantawa ba,sannu sannu sai gashi har tajai page na wajen biyar,ta saki murmushi saboda labarin yaja hankalinta,saita kife littafin,ta wuce kitchen ta zuba abinci ta dawo taci gaba da dubawa.


            Sannu a hankali sai gashi ta raba dare tana karatun,sam batasan dare yayi haka ba,don hatta da wayarta ta manta da ita,taje ta samu miscall na abbas kuwa harda sms guda daya,dare yayi don haka bata kirashi ba,sai tayi addu'a ta kwanta,amma kuma bacci ya qauracewa idanunta,tanata bitar abinda ta karanta din cikin kwanyarta,da gaske akwai soyayya irin haka?,soyayyar jaruman littafin ya tafi da ita,ta dinga kwantanta kanta dasu,kunya ta kamata ita akdai cikin dakin,saita kifa kai tana murmushi.


           Washegari babu makaranta good friday ce,wuni tayi tana karatun,wanda a ranar ta gama da part 02 ta shiga 03,sai data qare littafin a ranar ma sannan ta kwanta,nan dinma dai dukka labarin ta dinga tunawa,yadda jarumar ke gudanar da rayuwarta


"Kamar ni da uncle kenan?" Ta ayyana a ranta,da sauri ta girgiza kai,kai anya?,ita kanta wasu abunuwan cikin labarin kunya suka dinga bata,first night dinsu ya dawo mata a rai,sai tsoro ya shigeta,itama wataran haka uncle din nata zaiyi mata?,amma wannan ai iskanci ne,to amma dama akwai ranar da wannan abun zai tashi daga sunan iskanci?,ta tuna haihuwar da jarumar tayi,suna nufin kowacce mace ta haka take haihuwa?.


           A daren qwaqwalwa da tunanin yarinya kala kala ta dinga yi,abubuwa da yawa ta watsar dasu tana ganin bazai yiwu ba,ta rungumi abubuwa da yawa da syka dinga burgeta,har ta dinga kwantata gwadawa.


            Da safe kuwa ta gwada abunuwa da yawa da ta karanta din,duk da tana wasu qarawa tayi,ta gama komai ta hada breakfast dai dai cikinta,din me tayata kwana gari na wayewa take komawa cikun gida tayi ayyukanta,bata dawowa sai wani daren,ko idan bata da abinda zatayi ta leqota su gaisa sannan ta koma,mayar mai gadin gidan ce,tana da matuqar kirki sosai.


         Tana cikin yin breakfast taji sha'awar kiransa kamar yadda taji jarumar littafin tana yi,gabanta ya dinga faduwa sabida rashin sabo,ta dinga jin tsoro tana ganin kamar ba wani abun burgewa bane,saidai duk da haka bata fasa kira ba.


          Lokacin ya shiga wanka,hafsat na zaune daga gefan gadon nasa tana dakon fitowarsa,da sauri kamar wadda aka kirayi wayarta ta dauki wayar tana duba mai kiran


"Weedad" ta maimaita sunan data gani a rubucen cike da mamaki,kanta ya daure da kyau,ita dince ke kiran ko kuma dai idanunta ne,ko wata ce mai irin sunan,saita daga kawai kai tsaye.


          Shagwababbiyar muryarta data zame mata jiki,ta kuma saba magana da ita,da ita tayi sallama


"Ke tsaya" hafsat ta fada da sauri dai dai sanda take ficewa a bedroom din don kada ma ya jiyota.


         Wani mugun faduwa gaban widad yayi jin muryar mommy hafsa


"Ina kwana mommy" 


"Da ban kwana na zaki jini?,wa ya sakaki kiransa ko shi din sa'anki ne?" Mamaki ya bayyana a fuskar widad din,ta dauka ba komai,ta dauka momy din zata ce ta kyauta,saita kasa gane yadda abun yake


"Kiransa nayi mu gaisa mommy,jiya ya kirani ban dauka ba" tashin hankali!!, Ta fada a ranta tana jin yadda fuskarta ta dauki wani irin zafi,zazzafan kishinta da taketa qoqarin dannewa ya taso mata


"Yanzu ke har kisan ki kira d'a namiji kusan sa'an babban wanki koma babanki,ashe baki da kunya kwata kwata,to ba sa'anki bane,idan kika sake kiransa ko kuma ya sake kiranki kika daga saina miki mugun duka,ke bakya tsoron abinda zai sameki?,na gaya miki ba'a sakar musu fuska ko jiki,so kike yayi miki ciki ki mutu ko?" Karon farko taji maganar mommy hafsa din banbarakwai,sai taji kanta ya kulle


"Karna sake ji kuma kada na sake gani,kina jina?" Ta tambayeta a tsawace


"Tom" ta amsa mata jiki a sanyaye,sai hafsat din ta katae wayar tana jan tsaki,taso yarinyar na gabanta,amma bari ya fita,zata sake kiranta ta sake jadda da mata.


        Jiki a sanyaye ta ajjiye wayar, kwanyarta ta shiga rububin lissafin maganganun hafsat din,zuciyarta taqi amincewa da hakan jikinta yaqi karba kuma ranta yaqi gamsuwa,saboda aduk abubuwan data karanta bataga ta inda aka nuna abune mara kyau ba da har mommy hafsat din zata dinga mata fada haka ba,kusan minti goma ta kasa samun nutsuwa,sai tunani yazo mata,sai kawai ta kira anty deena tace bari ta tambayeta.


KI KULANI miss xoxo


DAUDAR GORA Billynabdul


RUMBUN K'AYA hafsat rano


IDON NERA Mamuhghee


A RUBUCE TAKE huguma


_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_


_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_


0022419171

Maryam sani

Access bank


Saiku tura shaidar biya ga

+234 903 318 1070


*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*

09166221261

*Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number*

+227 96 09 67 63

*Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

1 Comments

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post