Rumbun Qaya hausa Novel Page 10

Rumbun Qaya hausa Novel Page 10

 

Rumbun Qaya hausa Novel Page 10

RUMBUN QAYA

           Page 10


©️®️Hafsat Rano


ZAFAFA 2023🔥🔥🔥🔥🔥


****Tunda taga fitarsu ta lallaba ta gudu itama, dan dama hanyar tafiya take nema, bata san me ya hada su da Adam ba amma tabbas ta fuskanci yana cikin damuwa matuka, sai dai yadda yake abubuwan nasa ne sam basuyi mata ba. Bata cika son mutum me zafi ba, ko dan bata taso taga irin hakan ba? Hamman ta dukka basu da zafi ko kuma ita ce basa yi wa? Napep ta samu ya kaita makarantar su Amina dan sun yi daga nan zasu hadu su wuce ta rakata kasuwa, bata taba zuwa kasuwa ba tunda take a rayuwar ta, shiyasa take cike da daukin zuwa ta siyo wa yan gidan su abubuwa da first allawee dinta. Da weekend dukkan su zasu zo har Dadan ta, daga nan suje aga Abby wanda daga wannan zuwan sai kuma fitowar sa, shiyasa take cike da murna dan ji take kamar ta jawo ranar saboda tsabagen zumudi. A gate suka hadu da Aminan ta gama lectures har ta fito ma, dan haka ko sauka daga napep din batayi ba, ta shigo kawai suka tafi. Siyayya tayi sosai tunda kudin nata har da wanda Hamma Hydar ya bata ta hade ta sai musu abubuwa ta siya ma Adda Maimuna har ma da Aminan.

   A gajiye suka dawo dan saboda tsabar wahala ji tayi kamar kafarta zata tsinke, bata san haka wahalar kasuwar take ba sai da ta dandana, amma idan ta kalli abubuwan da ta siyo sai taji dadi ya kamata. Wanka tayi hade da alwala sannan suka zauna zaman cin abinci, shinkafa da wake da salad favourite abincin ta kenan. Da suka gama ta dauko kayan ta nunawa Adda Maimuna sannan ta bata nata da na Hidaya yar autar ta, aikuwa taji dadi sosai tayi ta godiya hakan ya yi mata dadi sosai.

 


***Yana zaune a falon Ya Nabilan tunda suka dawo be ce mata komai ba, kansa na saman pillow rabin jikin sa na saman kujerar sai wayar sa dake ajiye daga gefen hannun sa, abinci ta zubo masa a plate daga saman dinning ta kawo masa hade da ruwa sannan ta zauna a gefen sa. Tashi yayi ya daidaita zaman sa ya kalle ta sai yayi mata murmushi kad'an ganin yadda duk ta shiga damuwa.


"I'm fine fa."


"When last kaci abinci?"


Sama ya kalla kamar me nazari, kafin ya daga mata yan ya tsun sa, yayi mata alamar biyu


"Two days ago?" Ta zaro ido, gid'a mata kai yayi


"Allah Aryan kana da matsala, so kake ka kashe kanka? Kwana biyu baka ci komai ba? Akan me?"



"Abinci fa kika ce, nasha tea ai, ko yau ma sai da nasha."


"Tea, tea, tea! Dama tea din na kirki ne me hadin madara da sauran su, ruwa ne fa kawai sai gayyayyaki, me zai maka dan Allah?"


"Yana taimakawa sosai."


"Kayi sauri kaci kafin ya huce." Tace tana mikewa ta barshi a wajen, yasan ranta ne yake a bace shiyasa ma yayi kokarin daidaita kansa dan ta samu natsuwa. Sai ma yaje ya samu Kamal yaji akan dalilin da zai sakashi kiranta, kaamar dai shi din har yanzu baby ne, yasan kuma halin rikicewar ta, gashi duk yanzu tabi ta damu kanta akan abinda da ya bashi some hours ma shikenan zai wuce kamar yadda sauran suka wuce tunda ya riga yasan ba yau aka fara ba ai.

   Abincin ya soma ci a hankali duk da bashi da appetite sam amma kuma hakan zai ci ko dan hankalin ta ya kwanta. Chinese rice ce da chicken breast sai lemon kwakwa me matsakaicin sanyi saboda yanayin sa baya shan duk wani abu me sanyi sosai. Sai da yaci fiye da rabi sannan ya ture ya dauki tissue ya goge bakin sa ya koma ya sake kwantar da kansa a jikin kujerar. Fitowa tayi dan dama bashi lokaci tayi yaci abincin dan in ta zauna ya dinga kawo kabali da baadi kenan har sai ya haramtawa kansa cin abincin kwata kwata. Magungunan sa ta dauko ta mika masa ya karba yasha, tun bayan da Dr Ma'aruf yayi masa allurar nan ya samu natsuwa sosai, kansa da yake masa azababen ciwon nan ma ya rage sosai ya samu kwarin jikin sa, allurar ta riga ta zamar masa kamar masifa dan shi yanzu inhaler ma ba yi masa take sosai ba.


"Aryan?"


Ta kira sunan sa tana tattara hankalin ta waje daya, dan gyara zaman sa yayi dan ya fuskanci magana me muhimmanci zatayi masa ganin yadda ta kira shi da yadda fuskar ta, ta nuna


"Aure ne ya kamace ka a wannan yanayin, be kamata ka zauna haka ba."


"Aure kuma?" Yace yana tashi zaune sosai


"Yes aure, kana bukatar mace Aryan, kana bukatar life partner wadda zata tallafi rayuwar ka,."


Bata fuskar sa yayi nan da nan, kamar wanda akayi ma wata magana mara dadi 


"Mun yi magana da Kamal, tabbas abinda ya kamace ka kenan, domin ba lallai ne mu kasance da kai a kowanne lokaci ba, Aryan ko zama da yunwar nan da kake matar ka ba zata taba barin ka haka ba, zaka samu nutsuwa hankalin ka zai kwanta."


"Kun gaji dani?" Yace yana tashi tsaye


"Bamu gaji da kai ba, amma duk yadda zamu yi maka ba kamar matar ka ba, aure yana cike da tarin ni'imomi da ba zaka gane su ba sai ka shiga cikin sa."


"Bani da wadda zan aura, I don't trust just anyone, ba zan iya ba."


"Zaka iya, just give it a try, zaka gode mana."


"Ya Nabila, bana son kowa a tare dani,bana son zama da kowa, kune dama kawai tunda kuma kun gaji dani shikenan, i will take care of my self, ba sai an taimaka min ba."


"Don't get me wrong, ni iya gaskiya ta nake fada maka, dole dole akwai abubuwan da ba zamu iya maka ba, sai dai matar Ka."


Shiru yayi kirjin sa na bugawa da sauri, menene a cikin auren idan ba tarin nadama ba? Ta ina ma shi zai fara neman mata? Yace mata me kuma? Ba wannan ne shi yanzu a gaban sa ba.


"Kana jina kuwa?"


"Eh, kiyi hakuri ba yanzu ba, ba zan iya ba, naje na auri yar mutane na shiga hakkin ta."


"Shikenan, amma ka bud'e zuciyar ka, may be sai kaga an samu wata ta samu ta shiga zuciyar taka, shikenan ma ba zaka san sanda zaka zo mana da maganar ba."


"Hmm."


 Yace ya koma ya zaune, bata sake ce masa komai ba ta kyale shi dan ta lura ba zai fuskance ta a wannan lokacin ba. Yana gidan har yaranta suka dawo daga school, dan dama su ya zauna zaman jira da tuni ya tafi ya shiga wata sabgar, burin sa kawai ya koma office dinsa ya cigaba da aiwatar da abubuwan da ya fara wanda sam Daddy baya so shiyasa ma yake ta dakushe shi.



***A daidai kofar wani gida dake da karancin hadada har ma da karancin gidaje yayi parking. Fitowa tace ya je ya dawo ba tare da ya shigo ba, a duk sanda suka zo gidan ko cikin harabar gidan bata yarda ya shiga da ita da kafarta take takawa zuwa ciki duk kuwa da gidan ya kasance mallakin ta ne. Sai da taga tafiyar sa sannan ta juya ta shiga gidan.

   Yana tsaye a compound din yana dakon zuwan ta, sai gata ta shigo, su biyu ne tak suke da mukullin gidan dan hatta Adam bata yarda ya san da zaman wajen ba, dan tasan ba zai taba lamutar abinda take aikawata a wajen ba,amma kuma ya zatayi? Dole ta nemawa kanta biyan bukata dan babu wani abun arziki da take samu ta wannan bangaren. Ta dade a cikin harkar kuma bata taba jin dar ko dana sanin kasancewar ta akai ba. 


"Hajjaju kin karaso."


 Yace yana tahowa suka hadu a hanya, saurayi ne wanda a shekarun sa ba zai haura Adam dinta ba, idan ma zai haura din be fi da kad'an ba. Harkar computer ce ta hada su daga nan ta siye shi da wasu mahaukatan kudade har zuwa yanzu da suke rayuwa tamkar mata da miji a gefe daya kuma yana mata aikin da take so. Shiyasa Aryan yake a tafin hannun ta domin duk wani motsin sa tana sane dashi duk da akwai abubuwan da ta kasa samu a wajen nasa har yanzu. Babban burin ta shine samun faifan video din wanda take tunanin yana hannun sa, amma kuma idan ta zurfafa tunani sai taga ai da yana wajen sa da tuni ba maganar ake yi ba, dukkan su a yanzu sun yi taraiyane akan samun disk din wanda yake determining nasarar dayan su akan daya. 


"Na karaso, hope baka dade kana jirana ba handsome." 


Tace tana masa kallon kasa kasa. Irin na tsofaffin yan duniyar nan wanda suke san duniya take kad'a musu gangar shedanci a tsakiyar kansu 


"No ba yawa,ban fi 20mint ba."


"Duk da haka ba zan so hadadden saurayi ya zauna zaman jira na har na 20min ba."


Dariya ya kwashe da ita, ta mika masa hannun ta ya rike zuwa cikin gidan.


"Me yasa baka shigo parlor ba,ka zauna a waje."


"Jiranki nake, ba zan iya shigowa na barki ba."


Murmushi ta saki me taushi sannan ta jefar da jakarta gefe hade da mayafin ta, ta zauna tana kashe masa ido.


"Ya labari Hajiyata, ina fatan dai komai yana tafiya daidai?"


"Ba zaka fara kwantar da tarzomar da ta taso ba? Kafin wannan maganar?"


Dariya yayi, itama tayi dariya yace


"Shawara ce dani akai Hajiya."


Hannun ta, ta kai saman bakin sa da sauri


"Ban hana ka ce min Hajiya ba?"


"Tuba nake ranki ya dade."


"Ina jinka toh."


"Ina ganin duk wani communication da zai wanzu tsakanin ki da yarinyar nan ya zama call ne, banda text message kiran kawai sannan ki dinga recording call din, ni kuma zan san yadda zan nayi editing komai."


"Shisa nake kara sansa, kasan deal."


"Kinga baki bar wani sign ba da har zai iya zama hujja akan mu Hajiya, auw ranki ya dade." Ya kama baki da sauri yana dariya 


"Naji. Zan kuma yi amma dai for now dai mu shiga ciki, hakuri na ya kare." Tace tana mikewa


"Ok muje." Yace yana murmushi suke shiga daga ciki. Allah ya kyauta 



***Kasancewar Thursday yau ya sakata kin tashi da wuri dan ba zuwa zatayi aikin ba, a kaida CDS ya kamata taje wanda ake yi duk ranar Thursday, toh amma bata jin fitar kwata-kwata dan sai wannan satin tayi submiting takardar a road safety akayi mata signing. Tana jin Amina na tashin ta bayan ta shirya taki tashi haka ta hakura ta tafi ta barta, ta kara shigewa bargo dan akwai dan sanyi sanyi a garin. Kiran wayar Dadah ce ta farkar da ita, ta daga cike da zumudin ta. Nan da nan ta wartsake daga baccin jin suna hanya bayan da sai asabar zasu zo, suna Kaduna dama tun jiya yau dan haka tasan kamar yanzu zasu iso Kanon. Dadi kamar zai kasheta,ta shiga wanka a gurguje tazo ta ta hau gyaran dakin nasu, ta gyara ta wanke bandakin tas sannan ta hau shiryawa ta manta ma da wani batun breakfast, kaya tasa masu kyau sosai wanda tasan Dadah zata ganta fes da ita, dan kayan ma sababbi ne ta dinka su. Zuwa tayi ta fadawa Adda Maimuna suka hadu da Muhammad ya shiga tsokanar ta tana ramawa. Dakin ta dawo ta dauki wayar ta, ta dinga kallon lokaci ta kasa zama waje daya ko kad'an. Shigowar kira wayar ta yasa ta saurin zabura ta dauki wayar.


"Hajiya Zeenat?!" Ta furta a hankali kafin ta daga wayar


"Hello, aunty ina wuni?"


"Raihana ta, kin manta dani ko?"


"A ah Aunty."


"Toh kina lafiya? Ya aikin ya komai da komai?


"Lafiya lou alhamdulillah."


"Babu wata matsala ko?"


"Babu komai Aunty."


"Toh Masha Allah, wani taimako zaki min dan Allah idan ban takura miki ba."


"Ba komai Anty, me za'a yi?"


"Nasan kince min yau bakya zuwa aiki ko?"


"Eh bana zuwa, banje yau ba ma."


"Taimaka min ki shirya, zan turo miki address kije ki duba min Aryan."


"Na'am?" Tace tana zaro ido


"Eh ki taimaka min, Aryan bashi da lafiya kwana biyu kenan, gashi duk yadda zamuyi akan sa mun kasa wallahi, Adam yace min ya sake dake har yana saki aiki a office dinsa, kiyi min wañnan taimakon dan Allah kije ki gano min shi, sannan ki dafa masa shayin nan da aka ce kin iya dafa masa, Kamal ya fada min komai, ki taimaka min dan Allah."


Shiru tayi tamkar ruwa ya cinye ta, ita da take jiran Dadan ta yaushe kuma zata fita daga gida, suzo bata nan kuma sai tace tana ina kenan?kuma taje tace masa me? Bayan tasan halin sa sarai, kuma gidan shi da waye? Bata gane ba


"Zaki iya min wannan taimakon Raihana?" 


"Zanyi." Tace kai tsaye dan bata jin zata taba iya kin duk wani abu da ta nema a wajen ta


"Nagode nagode miki, Allah yayi miki albarka kinji? Ya baki miji na gari wanda zai kula dake."


"Amin."


"Karki damu, idan kinje gidan akwai mutane ba shi kadai bane, akwai maigadin gidan da matar sa su zaki samu kinji?"


Ajiyar zuciya ta sauke, bata tunanin Hajiya Zeenat zata taba cutar da ita ko tayi abinda zai cutar da ita, dan haka zuciyar ta daya ta yafa mayafin ta, ta dauki yar madaidaiciyar jakarta ta saka waya da kudin napep sannan ta fito 





🔥🔥🔥🔥🔥🔥


*_SAK'ON ZAFAFA BIYAR GA AL'UMMAR K'ASAR NIJER_*🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪


_ASSALAMU ALAIKUM MASOYA MAKARANTA LITATTAFAN ZAFAFA BIYAR JAMA'AR NIJER_


_DIMBIN GAISUWA DA FATAN ALKHAIRI A GAREKU_


_MUN FIDDA TALLA MUN BADA NUMBER DA ZAKU TUNTUBA,TO AMMA WANCAN NUMBER DA ZAKU TUNTUBA BA'A SAMUNTA,A HALIN YANZU GA SABUWAR NUMBER DA ZAKU TUNTUBA DON TURA KATI KU SAMU DAMAR SHIGA GROUP NA ZAFAFANKU BIYAR_


+227 90 16 59 91


*Yan jamhuriyyarmu nigeria kuma😂🇳🇬🇳🇬,zaku ci gaba da pyment ne ta account dinmu na*


Maryam sani

0022419171

ACCESS bank


Ku tura shaidar biya ga


+234 903 318 1070


*Katin waya ko VTU zaku tura ta wannan number*


09166221261


Litattafan dai sune kamar haka


RUMBUN KAYA Hafsat rano


A RUBUCE TAKE Huguma


IDON NERA Mamuhghee


KI KULANI Hafsat xoxo


DAUD'AR GORA Billynabdul


*Muna godiya da zabin zafafa biyar*🤝🤝🤝🔥🔥🔥🔥

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post