Kurkukun Ƙaddara episode 18 complete

Kurkukun Ƙaddara episode 18 complete

 

Kurkukun Ƙaddara

💋KURKUKUN ƘADDARA💋


Boss bature✍️


E18


 "Taya kenan zaki iya aiwatar da hakan? Ko kina tunanin zaki iya sarrafa tunaninsu ne? Yaran da ni na raine su da hannu na, na gatanta su, tun da suke basu ta6a shan wahalar rayuwa ba, komai suna samu ba'a abunda ban yi masu ba, matsayin uwa nake a wurinsu, a haka kike tunanin zasu ji maganarki fiye da tawa"? Tsohuce ta yi maganar yayin da take sakin wani irin bazawarin murmushi,

   Wani irin kallon rainin wayau angel tayi mata"Wlh tun da nake arayuwata ban ta6a ganin Muguwar maca ba, Azzaluma kuma macuciya irin ki ba!" 

  Yadda tayi magana batare da jin ɗar ba, ya yi matuƙar girgiza tsohuwa,

  "Wai ke baki jin tsoron Allah? Ki tuna fa komai kike yi Allah yana kallon ki, har kina da bakin da zakice kin basu gata? Kin raine su? Kuma har kike kiran kanki a matsayin uwarsu? Tirr wlh ji nake kamar inyi kakin majina in watsa maki akan fuskarki saboda natsane ki, Wlh nafi son mutuwa ta so dubu dake!" Zuba mata ido tsohuwa tayi tana kallon Ikon Allah,

  Sassauta murya angel tayi Idanuwanta cike tab da ƙwalla tace"Kin cuci rayuwarsu, kin gama dasu, ni banmasan ya zan kwatanta irin cin zalinsu da ki kayi ba, kuma ga dukkan alamu kin sani kike take sani, dan baki yi kama da jahila ba, Kawai salon tsabar mugunta ne, Yaran nan ko nonon raƙuma suka sha iya abunda zasu yi kenan, Ga sunan Wasu kala da su they don't even know anything about the one who created them because you never told them, cos of your wickedness Kin barsu a cikin duhu, sun zo duniya a wahalce kuma zasu koma a wahalce, Idan yau ɗayansu ya faɗi ya mutu menene makomarshi dan Allah meyasa ki ka yi musu haka? Meyasa?.........." kasa ƙarasa maganar angel tayi saboda wani irin ƙuntataccen kuka daya kubce mata, kuka sosai ta fashe da shi, 

  Tsohuwa kuwa ta kafe ta da waɗannan Kwala kwalan idanuwanta nata, masu kama dana ƴan ƙwaya,

   Cigaba da magana ta yi"Idan wani zunubi suka aikata maki, bai kamata ki ɗauki fansa ta wannan hanyar ba, balle ma nasan basu aikata maki komai ba, To kodai cikin danginsu wani ya yi maki badaidai ba, shiyasa kike ɗaukar fansa akansu" ta yi tambayar idanuwanta jawur hawaye duk sun wanke fuskarta,

 Tun da suka soma magana babu wanda ya farka daga cikin masu yin baccin, tamkar wasu matattu,

  Jinjina kai angel tayi"dama nasani bazaki bani amsar tambayata ba, sai dai ki kafe ni da ido kina kallo," ta yi maganar cikin sanyin murya tare da sanya hannunta da dama tana share hawayen dake silalowa,

  Kafin ta ɗaura da cewa"Allah ba azzalimin bawansa bane, Allah zai bi masu haƙƙinsu, inda na gode ma Allah, Mutuwa tana akan kowa, Walau mutun walau aljan, akwai kwanciyar ƙabari akwai kuma hisabi, Ina fata duk kin shirya ma wannan........" Muryar Batool ce ta katse ta ta hanyar kiran sunanta"ANGEL" koda tsohuwa taji muryar batool, Sai ta juya da sauri tana dogara sanda ta nufi ƙopar shiga ɗakinta,

  Har ta kusa shiga ciki muryar angel ta sake katse ta da cewa"Baki san Su ji me muke tattaunawa ne shiyasa kika nemi hanyar guduwa? Allah dai yana a madakata yana jiranmu, kuma inaso ki sani Zanyi amfani da ilmin da nake da shi, da kaifin basirar da nake da shi wurin Sarrafa tunaninsu, Kuma zansa su kar6i addinin musulunci, after that I will fight for our freedom, because no one deserves to live a locked up life!

  Tsawon mintuna tsohuwa bata motsa ba, kuma bata juyo ta kalli inda angel take ba, can dai taci gaba da dogara sandar, har samu ta shige cikin ɗakinta taja ƙopa ta rufe,

   Fashewa da wani sabon kukan angel ta yi, da sauri batool ta sauko daga saman gadonta, tazo gaban gadon angel ta zauna daga gefenta,

  Muryarta aruɗe take faɗin"Sister what's wrong with u? and why are u crying"? Kallonta angel tayi da idanuwanta da suka rune, muryarta a karye tace"Batool ina kuka ne saboda ku" 

  "But why"? 

"it will be hard for you to understand me, even if i tell you, so just forget about it," cikin shessheƙar kuka ta yi maganar,

  Dafa shoulder ɗinta batool tayi"Pls ki faɗa mun meyasa kike kuka sabo da mu"?

  "Baki ga tsohuwa ba"? Angel ce ta yi mata tambayar, girgixa kai batool ta yi"Banganta ba, tazo ne? Ita ce ta saki kuka"? 

  Girgiza kai tayi"A'a, Mubar maganar, inaso zan shiga toilet," daga haka ta zuro da ƙafarta daga saman gadon ta sauko, ta nufi toilet ɗinsu, Ta tafi tabar batool da tunanin dalilin kukanta, meyasa ta ke yin kuka saboda mu? ta yi ma kanta tambayar da bata da amsarta,


Tunda ta shiga Cikin toilet ɗin taci burki ta tsaya Idonta na akan Window nan dake a jikin bango, wadda ta ƙwallafa ma rai akan son Fasa glass ɗin jikinta, don ta samu damar dura wa Cikin kurkukun.


  Hannu tasa ta share hawayen dake akan fuskarta, Cikin zuciyarta ta soma yin magana"rana ta farko dana tsinci kaina cikin gidan kurkukun nan, A ƙagare nake dana nemi hanyar da zan fita daga Cikinsa, Amma Ayanzu bana sha'awar Barinsa batare da waɗannan bayin Allahn ba, Kuma batare da ƙwaƙƙwarar hujja da zan yin amfani ba, wurin ganin na tarwatsa duk wani shirinsu, Zanbi komai asannu domin Cimma nasara, Bi'iznillahi,'


   Angel yarinya ce mai kaifin basira Fiye da tunanin mai tunani, wayan dake gare ta yafi ƙarfin shekarunta, wasu ɗabi'un nata da halayanta sam ba irin na yara bane, she's genius"


    Lokacin da ta fito daga wankan, A tsaye ta samu Batool tana jiran na ciki ya fito ta samu ta shiga itama tayi wankan" Kallon juna su ka yi,


  Murmushi Batool ta sakar mata tare da cewa"tun ɗazu nake jira na ciki ya fito in samu nima in shiga in yi wanka,

  Angel tace"Wani ya shiga sauran toilets ɗinne"?

  Jinjina kai batool tayi"Eh, Hanna ce ta shiga ɗaya, ɗayan kuma Danish ne da deeja suka shiga Ciki," Har wata zabura angel ta yi jin abunda batool tace"What! danish da deeja ne suka shiga atare? Saboda me"?

  Fuskar batool asake tace"Dama idan babu wuri kuma uziri ya kama mu, mutun biyu suna amfani da toilet ɗaya......." 

tunkafin Batool takai ƙarshen maganarta, Angel ta yi gaba zuwa ƙopar sauran makewayin, Rai a matuƙar 6ace takai hannu tana Bubbuga ƙofofin tamkar zata Fasa su,

  "zaku fito ko saina 6alle ƙopar"? Tana huci ta yi maganar, Bama tasan wanne suke a ciki ba,

  Kusan atare suka buɗe ƙofofin toilets ɗin, na biyun Hanna ce ta leƙo kai, Na ƙarshen ne Deeja da danish suka fito, wani matsiyacin kallo Angel ta shiga binsu da shi from head to toe, hannun shi na a ruƙe da rigarshi, ita kuma iya rigarce har guiwarta, wandonta na hannunta,

  "lafiya kike bubbuga mana ƙopa"? Fuska aɗaure deeja ta yi mata tambayar"

 Dakuwa angel ta sakar mata"Ungo nan, Ku dukanku ku kar6a ku raba," 


 Kallon juna su ka yi don basu fahimci me take nufi ba, Runtse ido tayi zuciyarta na tafarfasa ta ambaci"Allahu ajirni fil musibati...... 

 Batool sai faman tamyarta take yi lafiya? Meya faru"? Ware idanuwanta ta yi akan fuskar deeja da ta danish, sae faman lumshe eyes ɗin shi yake yi, da alama bacci bai ishe shi ba, Sam tarasa ta ina zata fara, wato su awurinsu ba laifi bane idan mace da namiji sun shiga toilet ɗaya, tun zuwanta bata ta6a sanin suna yin hakan ba, Sai yau da take ji awurin batool ta kuma gani da idanuwanta, 


  Cizon lips ɗinta tayi tamkar zata fasa su, Cikin fusata ta nuna Deeja da hannu"Zoki wuce, Ki jira idan ya gama ki shiga" maƙe kafaɗa deeja tayi"babu inda zanja, meye naki aciki? 

  Wata irin gigitacciyar tsawa angel ta daka mata, Saboda tsabar ruɗi a firgice danish Ya koma Cikin toilet din," 

  Da gudu Sauran Ƴan uwansu dake acikin ɗakin suka faɗo Toilet area ɗin,  Haris da su aziza,

  "Meke faruwa ne"? Javed ne yae tambayar, Batool tace"Nima bansani ba, ranta ya 6aci ne saboda na faɗa mata cewa idan uziri ya kama mu kuma babu wuri mutun biyu suna shiga toilet ɗaya shine take fushi,"

  Harara haris ya watsa mata tare da cewa"To ke meye naki aciki da har zaki nuna 6acin ranki akai"? 

  Matsawa angel tayi Saitin inda haris yake a tsaye, Kafin ta soma magana atsanake,

  "Saboda hakan bai dace ba, Koda kuwa Namiji da namiji ne su shiga toilet ɗaya balle kuma Mace da namiji, bazan bari ana aikata 6arna batare dana hana ba, don haka daga rana irin ta yau, idan har na ƙara kama mutun biyu acikin toilet ɗaya, Saina Karanta ma shi charman dudu Cikin shi ya kumbura ya mutu kowa ya huta"


  Jin wannan maganar ta angel yasa hankalin kowannansu ya tashi, musamman deeeja tuni idanuwanta sun cicciko tan da ƙwalla,


  "Ya kike so muyi idan uziri ya kama mu, a lokaci ɗaya"? Hanna ce tayi mata tambayar,

  "Sai ku matse koma menene ku ke ji, idan na ciki suka kammala suka fito sai mutun ya shiga"

   "Ammaaaa......."kasa ƙarasa maganar haris yayi ganin tana nannaɗe hannun rigarta alamar za ta yi dambe, 

  "Abi Umarni na azauna lafiya, Shine kawai idan kuma mutun yace zaiyi mun gardama, yasan me zai biyo baya," 


  Gaba ɗaya duk suka sha jinin jikinsu, juyawa tayi tare da kallon deeja"Ke kuma Munafuka, zoki wuce ki jira idan ya kammala ki shiga, ni dama sam ban yarda  dake ba, da wasu idanuwanki tubarkalla kamar na kwartan mazuru, idan shi yana da ta6in hankali ai ke da hankalinki, Sullu6iyo kawai, zaki wuce kosaina Zubar maki da haƙoran gaba"? Jiki na rawa deeja ta ƙarasa fitowa daga cikin toilet ɗin Taja ƙopar ta rufe,


  Kallon sauran ta yi"Kowa Ya kama harkar gabansa, kuma Allah yasa wani yayi gulmata acikin ku, Aljanata kamila zata faɗa mun ne, daga nan ni kuma zan tofa ma mutun charman dudu" takai ƙarshen maganarta tare da sa kai ta wuce su tamkar damisa, Ta nufi Cikin ɗakin sai da ta shiga ta zauna gefen gadonta, Taci gaba da tiƙar dariya, can kuma ta dakata da yin dariyar hawaye suka soma shararowa daga cikin idanuwanta,

   Hannu biyu tasa ta dafe kanta, wani irin tsananin tausayinsu take ji, har cikin ranta take jin tsananin sonsu da ƙaunarsu, a halin yanzu babu wanda bata so acikinsu, saboda tausayinsu da take ji, ashirye take data taimaka masu wurin gyara rayuwarsu,


Jin motsin shigowar su Cikin ɗakin Yasa ta yi saurin share hawayen dake akan fuskarta, ta kishingiɗa saman gadonta, 


 A jere suka shigo kowa sai satar kallon Angel yake yi, cike da jin tsoronta, Ko zama ba suyi ba, Giants suka turo ƙopa suka shigo Hannunsu ruƙe da kayan breakfast ɗinsu, ba ƙaramin daɗi angel taji ba dama daren Jiya da wata irin matsiyaciyar yunwa ta kwana, 


 Bayan sun ajiye Masu farantan, kamar kullum Jiki na rawa suka Nufi saman Carpet ɗin kowa yayi zaman Cin tuwo, Suka zagaye trays ɗin,

   Sai da duk suka hallara, Hada danish wanda tunda ya zauna Jikin shi keta kerma sam babu natsuwa attare da shi, Gaba ɗaya tsawar da angel ta daka masu ɗazu ta gama gigita shi, 

  Tun da suka fara Cin abinci, Wurin ya yi tsit baka jin sautin komai saina taunar abincin da suke yi, ganin nata ya kusa  ƙarewa yasa ta fara tsantsani, can data lura danish ba wani cin abuncin yake yi ba, tsakurarsa kawai yake yi kamar baisan ci, da yake suna Fuskantar Juna, ta faki idon sauran ƴan uwan nasu, tayi musayar plate dana danish, ko da taga yana kallonta, saita zazzare mashi ido don kar yace zai anshe kayan shi,' lamarin yayi matuƙar ɗaure ma shi kai, yana ji yana gani tayi mashi musayar plate, ta ajiye ma shi nata data kusa Cunye, na shi kuwa a cike yake da abinci, bai dai ce komai ba, Yaci gaba da cin nata abincin data tura mashi, 


Bayan sun kammala, Giants suka tafi da kayan abincin, Ganin Kowa ya nufi gado zai kwanta yasa tayi saurin cewa"Ku dakata" Tsayawa su ka yi tare da juyowa suna kallonta,

  "From now on, when you finish eating food, no one will lie down and sleep, you have to exercise, doka ta ce duk wanda yaƙi bi kuma yasan me zai biyo baya,' 

  Natsuwa su kayi suna sauraronta, Haris ne yai kokarin cewa"Saboda me"?

  "Saboda lalacin ku yayi yawa, idan kuna motsa Jiki zaku yi ƙarfi, "

  "So kike kiyi iko damu"? Kafin ta bashi amsa aziza tayi saurin cewa"pls haris kayi shiru, kada ta karanta mana charman dudu, nidai zanyi abunda kike so angel,"

 Murmushin gefen fuska angel tasaki tare da kallon su batool tace"what about u guys? Zaku yi ko kuwa"? Har suna haɗa baki wurin cewa"eh zamuyi komai kikeso" Kallon haris tayi"kaima dole kayi idan har kana son zaman lafiya, idan ba hakan ba ta kanka zan fara aiwatar da aikina, tare da aljanata kamila,"

  Haɗe girarsa yai fuska a tur6une yace"Ae bance bazan yi ba"

  Ƙumshe dariya tayi abakinta, daƙyar ta samu ta basar da dariyar, ta ɗaure fuska tana hura hanci,

  "Sister ya ake yi toh baki faɗa mana yadda zamu motsa jikin ba"


"U will start running from wall to wall, untill i command you to stop, Idan aka kammala sai ayi Jumping," 


Amsa mata su ka yi da toh, jikin bango suka koma suka tsaya a jere, Kowa ya naɗe hannun rigarshi, 

  Komawa tayi daga bakin gadonta, ta zauna tare da ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya, Cike da bada Umarni Tace"Idan Na ƙirga uku Sai ku fara" su ka amsa mata"Toh"


  "1,2,3, Oya start" Da gudun gaske suka tafi Bayin Allah, Idan suka kai karshen bango sai su dawo sai su koma, har saida su ka yi kusan sau talatin tukunna ta basu hutu, zuƙunnawa su kayi a ƙasa, zufa ta ko'ina ajikinsu, Musamman danish kamar an tsamo shi daga Cikin ruwa, sae nishi suke yi,

  "Lokacin yin jumping ya yi, Maza kowa ya miƙe afara tsalle sau talatin kowa zaiyi duk wanda ya kammala sai yaje toilet ya watsa ruwa," amsa mata su ka yi da toh, ta tsaresu da ido har saida kowa ya kammala tsallan nashi, sannan ta ƙyale su tace kowa ya watsa ruwa azo ayi fira,

  Anan ta zauna tana jiransu, Bayan sun kammala, Jiki amace suka dawo cikin ɗakin Kowa Ya zauna saman gadon shi,

 "Yau kin bamu wahala sister, amma naji daɗin Jiki na" batool ce ta yi maganar, Haris da deeeja sunfi kowa Jin haushin angel, saboda ta sanyasu aikin wahala, danish kuwa tuni bacci ya yi awon gaba da shi, sam basu saba da wahala ba,


Kallon su ta yi ɗaya bayan ɗaya tun daga kan danish dake bacci har zuwa sauran dake ta faman yin gyangyaɗi,


 Gyaran murya ta yi masu gaba ɗaya hankalinsu ya dawo kanta,

  " Jiya kamar Kunyi mun wata tambaya ko'? har suna haɗa baki wurin cewa"tambaya akan me kanan"? Ta gefe ta kalle su "Kun manta? Ku tuna kun tambaye ni wani abu jiya,"

  "Eh, muna so Ki bamu labarin rayuwarki," azeeza ce ta yi maganar,

   "Gobe zan baku labarin rayuwata, Yau inaso Mu tattauna dangane da addini ne, Kallon juna su ka yi kafin suka dawo da hankalinsu kanta,

  "Addini kuma? Menene ma'anar hakan"? Da ruɗi akan fuskar hibba ta yi mata tambayar,

  Tana kokarin buɗe baki taci gaba da magana, Danish dake bacci ya kwatsa wata irin razananniyar Ƙara mai firgitarwa, " gaba ɗaya Hankalinsu Ya koma kanshi, 

   A zubure ya miƙe zaune Ya sanya hannayenshi Biyu ya daddafe kanshi, yaci gaba da fasa gigitacciyar ƙara, Da gudun gaske su haris suka sauko daga saman gadajensu. suka nufi gadon danish, Kowa ya shiga Lallashin shi suna bashi baki,

  Angel kuwa sakin baki tayi tana kallon ikon Allah. lokaci ɗaya ranta ya bata cewar tabbas Danish ba shi kaɗai bane, Meyasa sai lokacin da take ƙoƙarin yin magana kan addini zai farka yana fasa masu ƙara? Da alama anyi hakan ne don a ɗauke masu hankalinsu daga kanta, gashi yanzu gaba ɗaya sun rasa samun natsuwa sun duƙufa suna lallashin shi,

  Wani irin wahalallan murmushi angel tasaki tana kallon ikon Allah, wato da tsiya dai sai an dakatar da ita, jiya an kwaɗe mata kai da sanda yau kuma ta 6angaren danish aka biyo mata, 

  "Danish Pls can u talk to me? kana ganin fuskokin mu? Meya faru dakai? Atare suke jefa mashi tambayoyin nan, Angel ta kasa kunne tana sauraronsu,

  "Danish ka yi mun magana meke damunka? haris ne yae tambayar yana shafa dogon wuyanshi, Sae faman kerma jikin shi yake yi, ga wata irin zufa dake tsastsafowa daga Cikin sumar kanshi, ya runtse idanuwanshi sosai, duk ya ciccije lips ɗinsa,


   Zurfin tunani ta shiga yi, shin wata hanya zata 6ullo masu, tun da nan an toshe ta, sai yanzu ta ƙara yarda cewa akwai wata maƙarƙashiya, bakomai take tunawa ba face Wani American film da ta ta6a kallo na Magicians, a gidan aunty aneelerh, A cikin Film ɗin matsafa ne suke canza ma mutun tunaninshi su sarrafa shi, ko su sanya mashi tsafi a jikin shi, ko kuma suyi amfani da shi,' Jiya daga za ta yi magana an kwaɗe mata kai, kuma bata ga kowa ba, hakanan ta ke zargin tsohuwace kuma ga dukkan alamu zarginta ya tabbata tsohuwarce, sanan meyasa Basa son duk wani abu daya shafi Addini? A lokacin da ta kalli film ɗin ta ɗan shiga ruɗu harta tambayi aneelerh, 

 "Su matsafan ba'a iya yin maganinsu"? aneelerh tace"Allah shi ne maganinsu, idan yaso duk wannan 6acewar da suke yi sai kiga an kama su har an ɗauki mataki kansu, shiyasa ake so mutun ya kiyaye kuma ya dage da neman tsari awurin Allah, saboda su mutanene masu hatsarin gaske, ta kowace hanya zasu iya 6ullo maka," aneelerh tayi mata bayani akansu sosai, Natsuwa tayi tana bin ko'ina na ɗakinsu da kallo, tana ji acan ƙasan Zuciyarta kamar ta manta da wani abu, wanda ta gaza tunawa acikin kwakwalwarta, Aranta tana ji kamar ta ta6a kasance acikin gidan kurkukun ƙaddara, tsayar da idanuwanta ta yi akan red carpet ɗin da suke zama Su ci abinci kanshi, tunawa tayi da maganar aneelerh a inda tace"ɗaya daga Cikin alamomin matsafa, shi ne launin Ja, suna sanya jajayen kaya ko kuma A gidansu suna yawan amfani da jan abu kamar labule haka da sauransu,

  Jinjina kai angel tayi tare da cewa"Tsohuwa tana sanya jajayen kayan, Kuma carpet ɗin ɗakin mu Shima ja ne, kuma duk in aka kawo mana abinci, a saman trays ɗin ana sanya janƙyalle a rufe shi, Menene ma'anar launin jan nan na gidan kurkukun ƙaddara? su Giants suna sanya Baƙaƙen kaya shima launin baƙi bako da yaushe yake kasancewa abu mai kyau ba, dole nayi kokari wurin gano ma'anar waɗannan kalolin guda biyu Black and Red, kuma dole Nayi bincike akan lalurar dake damun danish domin kuwa wannan ciwon nashi Ba Misophonia bace, Kirkirarta a ka yi domin shi kawai, 


Hankalin angel fa yaƙi kwanciya, Saima ƙara ta shi da yake yi, Babban abunda take ji ma tsoro, Abunda take hasashe ya zamo gaskiya, saboda taji ance matsafa idan suka ɗauki mutun suna amfani da shi ne, Ko su cire sassan jikinshi, Ko su ɗibi jinin jikin shi, idan kuwa har hakane, To kuwa bata ga ta zama ba, duk da tana kokwanto akan hakan saboda su Batool sun faɗa mata cewa ba'a ta6a cutar da su ba, Kuma suna samun abinci, Matsafa ina suka ga lokacin ba mutun abinci, da zarar sun kamo shi kashe shi suke yi bayan sun gama kwashe amfanin jikin shi,


  Duk ba wannan ba, tambayoyi da yawa da take neman amsarsu WACECE TSOHUWA? SU WANENE GIANTS DAKE ZUWA KAWO MA SU ABINCI? A INA GIDAN KURKUKUN ƘADDARA YAKE? TA FARA HASASHEN GIDAN KURKUKUN BA'A CIKIN NIGERIA YAKE BA, ZAIYI WUYA MA ACE ACIKIN GARI YAKE, SHIN SU KAƊAI NE ACIKIN GIDAN KURKUKUN KO KUWA AKWAI WASU MUTANAN? MEYASA AKA HANASU SHIGA CIKIN SHI"?


  ta yi zurfi a cikin tunaninta muryar batool ta katse ta da cewa"Angel har yanzu baki yi bacci ba"! Firgigit tayi tare da kallon batool dake a zaune gefen gadonta hannun ruƙe da fitila, tsananin mamaki ne ya kamata, ganin duk sunyi bacci, ita kaɗaice zaune saman gadonta, batasan tsawon lokacin da ta ɗauka ba, Sai da batool ta fargar da ita, ashe dare ya yi har sun kwanta, ita a yadda tabarsu suna akan danish dake ta fasa ƙara, Yanzu ga danish ɗin nan kwance cikin bargonshi sai bacci yake yi, su azeeza ma duk sun kwanta, 

   "Yansu na farka zan shiga toilet shine na hango ki a zaune, nayi mamaki" murmushin yaƙe angel ta sakar mata tare da cewa"Bana jin bacci ne, ya jikin danish"?

  "Ya ji sauƙi, baki ga ma har yayi bacci ba" tayi maganar tana haska gadon danish ,

 Gyaɗa kai angel tayi"Nima yanzu zan kwanta, kije ki shiga toilet ɗin,"

  Batool tace"ae har na shiga na fito, zan wuce ne na lura dake a zaune"

   Shiru angel ta ɗanyi, ganin kamar tana acikin damuwa yasa batool tace,"Baki da lafiya ne? Ko wani abu na damunki"?

  da sauri angel tace"bakomai, kawai ina tunanin rayuwar duniya ne"

  "Yau da kika samu motsa jiki, ga6o6in jikina sai ciwo suke yi mun, amma yanzu dana ta shi daga bacci sai naji daɗin jiki na,"

 Angel tace"idan kuka saba kullum zaku ji dadin jikin ku, zai saki sosai ba'a son mutun daga yaci abinci ya kwanta, anfi son kadan motsa jikinka, "bayani tayi mata dangane da amfanin motsa jiki, batool tace"Daga yanzu duk in muka ci, abinci zamu dinga yi, bari naje na kwanta" tana kokarin miƙewa angel ta yi saurin ruƙo hannunta, kallonta batool tayi tare da cewa"Lafiya"?

  "So nake na tambaye ki, A gidan kurkukun nan Ana kiwon kaji ne"? Cikin rashin fahimtar zancanta, batool tace"Kiwon Kaji kuma? Meye ma'anar hakan"

  Dafe kai angel tayi"Ina Nufin kaji da ake kawo mana muna ci kusan kullum, Ana kiwonsu ne a gidan nan ne? Still batool bata fahimci zancenta ba, ta dai san kaza da ake kawo masu a soye suci, amma batasan ma'anar kiwon ba,

   "Shikenan tunda baki sani, Amma kin ta6a shiga cikin kurkukun nan? Naga ranar da aka kawo ni, Ni kaɗai nafarka acikin ɗakin nan, Ku kuma daga waje kuka shigo Ciki, Ina kuka je ne"? Ta yi tambayar tana kallonta"

  "Bazan iya tuna komai ba," cike da takaici angel tace"Komai baki sani ba ke, to faɗa mun a gidan kurkukun nan ku kaɗai ne kuke rayuwa a cikinsa"?


  Girgiza kai tayi"A'a bamu kaɗai bane, Kinga wannan numbobin na bayan rigunan mu, akwai me 400," waro ido waje angel tayi muryarta har shaƙewa take yi wurun cewa"Are u serious"? Ɗaga mata kai batool tayi alamar Eh, taci gaba da cewa"idan zan iya tunawa kafin zuwanki, Munyi rayuwa acikin wasu Prisoners ɗin waɗanda Ke rayuwa a killace cikin kurkukun nan, bamu kaɗai bane, muna da yawa," mamaki ƙarara akan fuskar angel ta kuma cewa"Amma ku meyasa aka ware ku daga Cikinsu"? Batool tace"nima bansani ba,"

   "Yanzu faɗa mun, duk wani abu da kika sani game da kurkukun nan," 

  "Bansan komai ba"

"Ke dai ki tuna" shiru batool tayi tana kokarin tunano abunda ta sani, tsawon lokaci kafin ta soma magana

  "Idan aka ɗauki mutun ba'a dawo wa da shi, idan muka tambayi tsohuwa ina ƴan uwanmu suke waɗanda aka ɗauka daga Cikinmu, sai tace mana mu kwantar da hankalin mu, Suna nan cikin ƙoshin lafiya wata rana zasu da....." bata kai karshen maganarba, ta miƙe da sauri ta dauki fitilarta, ko kallon angel ba ta yi ba ta wuce saman gadonta ta kwanta, 

  Zuba mata ido angel tayi Cike da mamakin yadda ta miƙe zumbur ta tafi batare da ta ƙarasa maganarta ba, kodai itama an zungureta ne? Ta yi tambayar a cikin Zuciyarta,


   Kafin ta yi Shirin kwanciya, kamar kullum ta ɗaga hannayenta sama tana yi masu addu'o'i, Hada daddynta kullum ne bata mantawa da shi, Yana acikin ranta..........🥺


*ANEELERH* 


Mami ce zaune gefen gadonta har ta yi shirin kwanciya, jikinta na sanye da Sleeping gown, ta ƙura wa screen ɗin wayarta ido,

  fitowa abie Yayi daga Cikin toilet yana gyara wuyan jallabiyar jikin shi,

   gyaran murya yayi mata ta ɗago tana kallon shi, fuskarta da alamun damuwa tace"Ina ta kiran aneelerh bata ɗaga ba, "

  "Bansan meyasa kika tashi hankalin ki ba, sai kace wadda ta tafi wata uwa duniya,"

  "Dole na damuwa, saboda ni bata faɗamun cewa a can xata kwana ba, kuma na kira layin Uncle bash ɗin tana ta ringing bai ɗaga ba, itama dr Aisha na kira layinta bata ɗaga ba, idan acan zata kwana ae yakamata su kira su sanar dani," 

   Murmushi abie ya saki"Na lura ba ƙaramin ji kike da ƴar nan taki ba, Ko da yake nasan saboda wa kika hana idonki bacci," 

 "Bai wuci kace saboda baby junaid ba, ae dole na damu da jika na, shi kaɗai fa nake da shi kwallin kwal an tafin mu da shi, sai da nace tabarmun shi a wurina, amma ta kafe akan saita je can da shi,"

  "In banda abunki, taya zata tafi tabar maki shi, bayan ba'a yaye shi ba, idan ya yi kuka ya zakiyi da shi"? 

    "Nima ae macace, Kaima kasan ina da abunda zan bashi" Dariya abie yayi a lokacin ya dawo gefenta ya zauna,

   "Yanzu dai ki kwanta kiyi bacci, zuwa gobe da safe, zasu dawo kiga jikanki," 

    Ba don taso ba, ta ajiye wayar Suka kwanta bacci atare,

 

A 6angaren Aneelerh Kuwa, tun Bayan magbrib suka baro gidan Uncle bash, Drivern gidansu Musa ne ke yin driving ɗinta, Tana a zaune Cikin back seat na motar, Jikinta na sanye da Arab gown ta yafa mayafi akanta, Baby junaid na rungume saman kirjinta, Yasha kayan sanyi ajikin shi,


"Ba gida zamuje ba, Gidana nake so ka kaini akwai wasu kaya da zan ɗauka"musa dake driving yace"Amma Ba mu yi da Alhaji cewa zan kaiki gidanki ba,"

  "Eh na manta ban faɗa ma shi ba, ka kaini ba matsala," acewar aneelerh,

  Shi dai hankalin shi bai kwanta da su je gidan nan ba, ganin dare yayi kuma gidan yana a karkashin Binciken ƴan sanda bai son wani abu ya faru,

  "Amm hajiya naga dare yayi yanzu, me xai hana mu bari sai gobe da safe in kaiki gidan'?

 ɗaure fuska aneelerh tayi sam batasan gaddama"meyasa ka ke yi mun magana sai kace wata ƙaramar yarinya? Bani nace ka kaini ba? Ae ba jimawa zanyi ba, akwai abunda nake so in dauko ne Ko minti biyar bazan yi acikin gidan ba,'

 Muryar shi na inda inda yace"Zan kai ki mana kawai dai naga dare yayi ga kuma yaro ahannunki,'

  "Muje kawai nidai" Amsa mata yayi da toh, ya juya sitiyarin motar ya haura saman titin da zai sada shi da unguwarsu Uzair,

Lokacin da suka ƙaraso unguwar tsit babu hayaniya ko gifcin mutun baka gani, kowa ya shige gidanshi, akwai hasken street light ta ko'ina,

  A bakin gate ɗin Gidan, Musa yayi parking ɗin motar, ya fito da sauri ya buɗe ma aneelerh murfin motar, Fitowa tayi hannunta rungume da junaid, Key ɗin gidan yana a hannunta, Dama biyu gare su ɗaya na uzair ɗaya nata, wanda ke a hannun jami'an dake bincike na Uzair ne,


  "Madam kodai in bi ki mu shiga Ciki"? Kallon shi tayi ganin duk ya tsorata"Motar fa wa zaka barma gadinta"? Muryarshi a sanyaye yace"hakane kuma bari na koma Ciki na jira ki, dan Allah Aunty kiyi sauri" murmushi tasaki jin ya canza mata suna, ya kirata da madam ya kuma kirata da aunty, Maimakon sunan da yake kiranta da shi Hajiya,

  Wuce wa ta yi zuwa bakin ƙopar dake a jikin gate ɗin gidan, ta sanya key ta buɗe ta, ta shiga daga Ciki, duk akan idon musa dake a tsaye ya jingina bayan shi jikin motar,


A tsanake take tafiya Cikin Gidan wani irin yanayi take ji atattare da ita, Ko'ina ta shiga bi da kallo, tun daga kan inda suke ajiye motocinsu har zuwa ƙopar shiga falonsu, Bakomai take tunawa ba face rayuwarsu da Uzair, tuni taji hawaye sun wanke mata fuskarta, yau tsawon shekara biyu da watanni kenan, babu su babu alamarsu,

  Hasken electric bulbs ne Ya gauraye gidan, tamkar da rana,


Lokacin da tazo bakin ƙopar falon, ta sanya key ta buɗe ƙopar ta shiga daga Ciki, Ko'ina a gyare yadda kasan mutane na rayuwa acikin gidan,


A saman Sofa ta kwantar da baby junaid dake ta bacci, ita kuma ta shige Cikin bedroom ɗinsu, tsayawa tayi tana bin ɗakin nasu da kallo, sai ta dinga ganin kamar fuskar uzair yana sakar mata murmushi,


Girgiza kai kawai ta yi yayin da hawaye ke cigaba da sauka saman fuskarta, Hotonsu na aure dake manne jikin bango ta ƙurawa ido, Sunyi matuƙar yin kyau, kusan minti biyar kafin ta Hau saman gadonsu ta kwanta tana shessheƙar kuka,

Dama babu abunda ya kawota Cikin gidan tazo ne kawai don ta ƙare mashi kallo saboda kewar Mijinta da tayi,,


Bubbuga mattress din ta dinga yi da hannunta tana kuka tana faɗin Wai ina kaje uzair? Meyasa ka tafi kabarni cikin maraicin rashinka, bayan kasan bana iya rayuwa da wani ɗa namiji idan ba kai ba, dan Allah mijina ka dawo gareni wlh ban gaji dakai ba, ina matuƙar ƙaunarka, kazo kaga Babynmu kyakkyawa da shi, so kake ya taso amatsayin maraya wanda bai da uba? Why uzair? Wata amsa kake so na bashi idan ya tambaye ni dangane da Mahaifinsa? Sai sambatu take yi ita kaɗai tana kuka, sam ta manta da Musa driver dake jiranta, ga kuma Yaro da ta bari a palour shi kadai saman Sofa yana bacci,


Kusan awa ɗaya aneeelerh bata motsa ba, wani irin yanayi mara misaltuwa take jin kanta a ciki, sai faman shessheƙar kuka take yi,


Lokaci ɗaya taji mummunar faɗuwar gaba ras! Tamkar ƙirjinta zai dare biyu, bugun zuciyarta ya ƙaru, Jiki na rawa ta sauko daga Saman gadon muryarta na kerma take ambaton sunan Junaid,


Da gudun gaske Ta faɗo Cikin Falon, Tana ɗaura kanta saman Sofa ɗin data kwantar da junaid, taga wayam babu shi sai dai towel ɗin data nannaɗe shi aciki, A ƙasa aka jefar da shi


(Idan kinsan bakya comment da liking, U should stop reading my book, ✍️

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post