Kurman Baƙi Page 3 Complete by Huguma

Kurman Baƙi Page 3 Complete by Huguma

 


https://chat.whatsapp.com/HeRo2w8C8gdG0Et1lqafjk


*_KURMAN BAƘI_*



*H U G U M A*


Page 03



            Yara biyu ne a gaba suka fara shigowa,mace da namiji wanda dukkansu ba zasu wuce shekara goma da hudu ba. Macen itace babba sai namijin. Farare ne sosai kamar yadda yanayin fatar mahaifiyarsu zainab take. Daga bayansu sauran yaran maza biyu suka shigo. 'Yan biyu ne identical masu kama da juna sosai. Rirriqe labulen sukeyi suna shigowa a hankali da alama babu sakewa sam a tattare dasu. Tunda sukaga qofar maman nasu a kulle hankalinsu ya gaza kwanciya,duk da qarancin shekarunsu amma dai dai da rana daya basa qaunar su shigo gidan su samu mahaifiyarsu bata nan.


                Zainab daketa fadin tashin kintsa falon ta watsa musu harara


"Shegu masu shegen baqin hali,duka duka shekarunsu basu wuce a qirga da yatsu ba amma sun iya nunqufurci da shegen gulma da sanabe irin na uwarsu" ta fadi idanunta a kansu kamar zasu fado,har yanzu tana jin dacin haifar yaran a dai dai lokacin da take ganin cewa itace da gida,a sanda dukka lissafinta ya gama bata ta gama mallakar saleem mahaifiyarsa da kuma danginsa,ta haifa masa abinda ya jima yana mararin samu wato 'YA'YA,sai gashi a dare daya ruqayyan ta gigitata da wata irin ba zata da bata shirya mata ba.


"Don uwarku ku koma idan ba zaku shigo ba" ta fada cikin daka tsawa tana jan tsaki. Tsam al_hussain ya riqe hannun al_hassan yana mele baki alamun zagin data masa ya taba ransa. Yafi al_hassan zuciya sosai,sai kawai ya figi hannun dan uwansa suka fice zuwa babban parlor din da ya hade qofofin falukan da suka samarwa da kowaccensu sassanta.


"Kinga shegen yaro?" Zainab ta fada cikin mamaki tana binsu da kallo. Tun yanzun yaran suke da wani irin hankali da saurin fahimtar abu,tana tunanin gaba zaiyi wuya basu zame mata tarnaqi ko alaqaqai ba.


"Zakaci ubanka zanga ka dawominne" ta fada tana daga murya don ta tabbatar suna falon a zaune.


"Mama yunwa nakeji fa gaskiya" babbar diyarta haneefa ta fada tana yamutsa fuska


"Iyalan ci da baku da aiki sai cin abinci,yo nima banci ba tun safe,ki bude lunch box dinki ki cinye sauran abinda ke ciki kafin na gama kintsa gidan na dora" ta fada tana ci gaba da hidimar gabanta. Ita a yanzu ma bata abinci take ba,maganinta kawai take kasa kunne taji me delivery yace gashi ta afa ta tabbatar ya isa cikinta. Yunwa ba yau ta saba zama da ita ba.


"Mama dumamen abincin jiya ne fa dama kika zuba mana,kuma wallahi tun kafin azahar shinkafar ta jiqe,sai abincinsu alhassan muka ci"


"Kut" zainab din ta fadi tana dakatawa da abinda takeyi bayan ta waiwayo


"Uban waye yace kuci musu abinci?,ban hanaku ba?" Ta fada cikin fushi tana kaiwa yarinyar mari. Tun ranar da yaran suka taba yabon girkin ruqayya a gabanta saleem ya tayasu taji ta tsani duk wani abinci da zai fito daga gurinta,duk kuwa da cewa girkin dare hadawa sukeyi,hasalima tare sukeci a babban falon gidan.


             Zagi ta shiga dura mata abinda ya sanya yarinyar sakin kuka ta miqe tana zubda jakar makarantar da flask din a wajen tayi dakinsu da gudu. Hakan bai hana Zainab ci gaba da masifa ba kamar zata ari baki,da da hali dukan tsiya zata yiwa haneefa din a yau,saidai ta tabbatar muddin ta taba lafiyarta kamar a kunnen mahaifinta,abinda kuma tasan bazai haifar mata da d'a me ido ba,tana son yau ta gyara wasanta ba zata bar wani abu na rashin jin dadi ya wargaza mata shirinta ba,dole yau tayi kaffa kaffa da komai.


              Dan qara speed na motar tayi hankalinta yana kan lokaci. Tasan tabbas zuwa yanzu yaran sun dawo,bataso hakan ba amma uzurin da ya riqeta dole ta gama kafin ta taho.


             Shigowar motar tata yaja hankalin yaran, suka watsar da abinda sukeyi suka rufo da gudu gurinta. Tana qoqarin bude murfin motar amma sun hanata saboda yadda sukayi tsaye a bakin qofar suna murnar ganinta. Murmushi ta saki tana dubansu zuciyarta na karyewa. 'yan awanni kadan tayi bata gidan,amma dukka hankalinsu ya tashi,ina ace yau mutuwa tayi ta barsu?. Cikin taqaitattun mintunan da ta qara bata nan yaran har sun fara fita a kamanninsu,sunyi wasa a farfajiyar gidan sun vodeyAllah,suit din uniform din tasu sun cikata da qasa da ruwa abinsu,kada ma kayan alhussain yaji labari.


"Yanzu don Allah ba zakuji kunya ba ifti ta ganku a haka?,ummm?" Ta fadi tana dan duban yarinyar tata dake daure cikin wata jaka da aka maqale a seat din motar. Jikkunansu suka kalla kafin su qyalqyale da dariya. Alhassan yace


"Momy ni jikina bai baci ba sosai,ni zan dauketa"


"Allah momy na rigashi zuwa" alhussain ya fada yana qoqarin tureshi.


"Duk ba wanda zan bawa 'yata,me yasa baku shiga gurin maman haneefa kun zauna ba?" Ruqayya tayi musu tambayar tana fidda jakarta tare da saka iftihal a kafadarta


"Ba zaginmu tayi ba ta kuma yi mana tsawa" alhussain ya fada yana tura baki gaba. Waiwayawa tayi ta kalli yaron,har cikin ranta taji ba dadi,hakan yana nufin ko babu ranta ba zata iya riqe yaran ba kenan,ta kuma san irin salon zaginta,bata iya qanqanin zagi ba,fadan kullum sai sunyishi da saleem kenan,domin yace bazai lamunci zagin da take kuntumawa ba,ba zata lalata masa yara ba.


"Aiki take kuka dameta,muje ciki ku cire uniform kuci abinci" sai ta saka yaran a gaba suka wuce cikin gidan tana biye dasu a baya da jakunkunansu.


              Bata samu nutsuwa ba sam sai da maganin ya iso,ta zauna ta farkeshi ta duba sannan tayi amfani dashi kamar yadda matar ta gaya mata. Sakin wani murmushi tayi tana saka dukkan lurarta ga jikinta,ta fara lissafe lissafen irin canje canjen da akace ta sanya ran zata ji


"Hmmmm,yau da sabga,ruqayya yau zaki qunshi baqincikin da sai ya kusa ajalinki" ta fada a sarari tana dariya. Tabbas yau zata aiwatar da komai ne da gayya saboda ta qona ranta yadda ya kamata,ta fanshe tarin baqinciki da bacin ran da take qunsa mata kowacce safiya da irin baqin kinibibinta.


          Duk yadda taso taga ta kammala komai ko don ta faranta ran saleem din yadda yasan yafison yazo ya sameta amma ta kasa,jiki dukka da zuciyarta a haka suke,ta riga data saba,zallar son jiki kasala da rashin son yin aiki sun zame mata jiki,sai data bata lokacin da girkin ma bata dorashi ba sai la'asar liqis.


             Yadda ta kacame da aiki a kitchen din ya Sanya nylon din rigar baccin dake jikinta ta soma damunta,ga zafin kitchen din ga kuma rashin yin wanka. Gefe taja tana jan tsaki


"Ni shi yasa duk ababen nan basu dameni ba,me za'a wani yi da rigar bacci" zareta tayi ta azata jikin qofar kitchen din,ta ja zanin jikinta tayi daurin qirji dashi taci gaba da juya miyarta wadda keta kamawa saboda yadda ta raba hankalinta gida biyu,rabi yana ga girkin rabi kuma yana ga wayarta da taketa bin charts na group dinsu dake sake qara mata qwarin gwiwa tare da samun tabbacin yau din daren zai kasance na musamman ne.


                 A nutse ya isa da motarsa harabar da ya saba ajjiyeta,ya daidaita tsaiwarta sannan ya kashe motar yana furzar da iska daga bakinsa a mugun gajiye. 


            Yau tunda ya fita bai zauna ba,ya gaji liqis yadda ya kamata,sunata zirga zirga tsakanin warehouse dinsu da shagunansa,ko abinci bai samu yaci ba,yunwa ce a kwance a cikinsa. 


                 Hannun rigarsa ya tattare yana duba lokaci,ana dab da kiran sallar magariba ne,duka duka bazai wuce mintuna goma sha biyar ba. Hannu ya sanya ya bude motar ya fito hannunsa dauke da ledoji,qarar rufe murfin motar yaja hankalin zainab dake kitchen,ta ajjiye ludayin miyarta da sassarfa ta fito daga kitchen din ta isa window din da yakw sadata da kowanne kallo da ya danganci harabar gidan.


               Kamar zuciyarta zata fado sanda yake nufar sashen ruqayya,abinda tafi tsana kenan a rayuwarta,duk kuwa da cewa ita dinma hakan yake musu,baya taba shallake sashenta idan ya shigo sai ya fara dubata sanann ya wuce wajen ruqayyan yadda al'adarsa take kenan duk sanda ya kasance kece da girki. A nutse ta sauke idanunta ga ledar hannunsa,tanaso tasan meye a ciki?,saidai duk iya qwaqwarta ta kasa tantancewa saboda ledar baqace me duhu babba da qarama.


             Sakin labulen tayi yana jan tsaki,ta waiwayo ga haneefa wadda suketa wasan guje guje,wasan guje gujen da ya qarasa hargitsa gyaran 'yar burum burum din da ta yiwa falon. Tsawa ta doka mata sannan ta narka mata ashar


"Ga babanku can yayi sashensu alhassan,bishi ki ga me ya shigo da shi a baqar ledar hannunsa" yarinyar kamar ba zataje ba,sai kuma ta zumbura baki tayi gaba


"Zakici ubanki da shegen rashin son aike" ta sake binta da zagin idanunta kamar zasu fado saboda harara,sai kuma taja qwafa ta wuce bandaki a gurguje tanason watsa ruwa kafin yakai ga shigowa.


            Wani sassanyan yanayi ne da parlor din wanda ko yaushe baya rabo da shi saboda tsaftar da ya kamashi. Komai na tsaftace ne akan tsari da sanin darajar muhalli. 


            Sassauqar doguwar riga ce a jikinta ta wani yadi maras nauyi ruwan madara me haske sosai,kusan duk shigarta tana yinta ne bisa tsari da favourite colours na saleem din. Alhassan da alhussain na zaune daga qasan carfet saman qananun duddumansu,kowanne jallabiyya ne a jikinsa farare da qananun hulunan tashi ka fiya naci. Kyau yaran sukayi kuma duk wanda ya kallesu dole su bashi sha'awa.


              Sallamar uban ta sanyasu hankulansu yowa kansa,al_hussain shi ya fara yo gaba yana qoqarin karbar ledar hannunsa hadi da fadin


"Abba sannu da zuwa" wadda suka furtata kusan lokaci daya da al_hussain dake daukema abban nasu pillow daga saman kujerar don ya samu wajen zama.


              A duk sanda ya sanya qafafunsa a sassanta yakan jishi tamkar cikin wani muhalli na daban yake ba'a cikin gidan ba. Sau tari yakan tambayi kansa da kansa


"Me yasa ya qaro aure?" Wani lokaci zuciyarsa da kwanyarsa kanyi hadin gwiwar bashi amsar


"Rabo". Kamar ko yaushe a yau ma amsar da ta bashi din kenan,wanda yayi dai dai da ajjiye kaskon turaren wutan dake hannunta,ta kuma sauko daga dining area din yana gyara zaman dankwalin kanta me sulbi tana fadin


"Barka da warhaka" 


"Barka kadai" ya amsa mata yana bin su alhussain da kallo wadanda suka nade abun sallarsu suka wuce dakinsu.


            Hannun 3sitter din da yake kai zaune ta zauna itama,idonsa ya dawo dashi kanta lokacin da ta miqa hannu ta jawo gorar ruwa me matsakaicin sanyi ta zuba glass cup tana miqa masa. Sai da ya saki murmushi sannan ya miqa hannu ya karba,ya shanye tas sannan ya miqa mata cup din


"Na rasa wacce irin baiwa ce dake da har kike gane yunwata da qishirwata ba tare da na furta ba" murmushin ta kuma sakar masa


"Da kallo guda daya tak da zanwa idanunka na gama samun amsar komai" kai ya gyada cikin gamsuwa tare da jin matsayinta yana sake zarcewa wani madaukakin muhalli a zuciyarsa. Kullum wayewar gari sai ya godewa Allah da bai bawa shaidan galaba a kansa a shekarun baya ya ingizashin da zai zama sanadiyyar rasa ruqayya ba,inda hakan ta faru?,yanzu da a wanne gurbi yake a rayuwa?.


"Amma,me yasa ba kowacce mace ke da wannan baiwar ba?" Idanunta ta dan janye daga kansa,jikinta ya bata inda maganarsa keson dosa,don haka tadan juya ido kadan


"Ya danganta da yadd kika zabi ki fuskanci mijinki ko ki mu'amalanceshi,hakanan ya danganta da iya adadin lokacinki da kuma kulawar da kika bashi".


"Sai yaushe zainab zata dinga fahimtar irin wadan nan abubuwan tayi koyi dake ta kuma canza?" Dauke kanta ta sakeyi a karo na biyu. Duk girman matsin da zaya shiga muddin akan zainab ne bata da sha'awar ta shiga lamarinsu,lamarin miji da mata sai Allah,duk yadda take gani a yanzun a wata ranar tana iya ganin sauyin hakan a tattare dashi,duk da cewa zuwa yanzu ta jima da mance wannan lamarin


"Ba'a sassa na kake ba,kada maman haneefa taga ka jima da yawa" ta fada tana miqewa, miqewar da taja hankalinsa har ya gaza dauke dubansa daga kanta


"Au korata ma kikeyi?" Ya jefa mata tambayar da kafin ta bashi amsa turo qofa da shigowar haneefa taja hankalinsu.


             Rarraba ido ta fara yi tsakanin fuskar abban nasu da ruqayyan. Har cikin ranta ruqayyan tana jin babu dadi. Yadda yanayin tarbiyya haneefa take a gidan,akwai sakaci na bala'i daga wajen mahaifiyar da bata cancanci zama uwa ba. Duk da haneefa ta girmewa su alhussain nesa ba kusa ba,amma akwai nisan tazara me yawa a tsakaninsu,tun daga hankalinta zuwa nutsuwarta.


              Tsuke fuska saleem yayi ransa na baci,a tsawace yayi mata magana


*HUGUMA*👑

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post