AUREN WATA UKU..!
41
©️Sameena Aleeyou…✍🏽*
Duk sai ta daburce ta rasa mai zatai. Ta kasa furta komai sai duban juna da suke su duka biyun… A haka aka turo k’ofan d’akin.. Ba kowa bace face Mommy. Ganinsu a haka yasa Mommy saurin k’arasowa murmushi gauraye da hawaye saman fuskarta. Farin cikinta ya gaza b’uya.
“Haidar. My son.! Alhamdulillah.. Haidar ka tashi..!” Sai kuka ya b’alle ma Mommy. Ta d’aga hannayenta sama tana fad’in “Alhamdulillah.! Allah na gode maka da ka tashi D’ah na. Allah na gode maka..!” Hawaye na gangaro mata tafukan hannayenta tallafe da fuskan Haidar din duka b’angare biyu taci gaba “I can’t believe you are finally here with us again son.. You know, I don’t mind losing everything.. But.. Amma bazan iya rasaka ba Aliyu… Bazan iya jure rashin ka ba..!” Ta daga hannayenta guda biyu sama “Allah na gode maka daka tayar min da D’ahna… Allah na gode maka for giving me such a blessed opportunity to be with my son again..!” Ta k’arashe tana mai rungumo kansa daga nan yanda yake a kwance. Dole duk Wanda ke duban Haidar da mahaifiyarsa su basa tausayi.
Ummul ta share kwallan da suka zubo mata. Ta janye jikinta ta matsa gefe kad’an cikeda farin ciki musamman yanda taga farin ciki Ya mamaye Mommy.
Mommy ta dubi Anisa da shigowarta kenan tace maza ta kirawo Likita. Cikin sauri Anisa wacce itama farin cikinta had’ida mamaki Sun gaza b’uya ta shiga jinjina akai tana fad’in “Sure Mommy. Right away.!”
Koda Likita ya shigo tambayoyi ya soma masa yanda ya fara da tambayarsa meye sunansa.
Shiru Haidar baice komai ba sai kallon da yake binsu dashi d’aya bayan d’aya. Zuciyar Mommy yai wani irin yankewa ganin irin duban da Haidar ke masu tamkar Wanda bai tab’a saninsu a rayuwarsa ba. Duba irinta rashin sani.
Mommy ta soma girgiza Kai tana duban Haidar tana duban Likita “Dr.. Meke faruwa da D’anah..? Why can’t he say anything..?”
Dr yai k’ok’arin calming Mommy kafin ya dan soma ‘yan dube dube dangin su ido da k’irji ma Haidar dake nan kwance yana musu kallon rashin sani musamman Mommy.
Mommy ta dubi Haidar ta kuma dubi Dr “Likita sanar Dani meke damun D’ana.?”
Dr ya girgiza Kai kad’an had’ida furzar da huci kafin ya maida dubansa ga Mommy “I’m not sure if he’s having a temporary memory loss.. But there are some testes he has to undergo ta haka zamu iya fahimta matuk’a baiyi magana ba har na tsawon dak’ik’ai.”
Mommy ta lumshe idonta hawaye suka gangaro mata. Taci gaba da duban Haidar tana hawaye take girgiza Kai.. Ta rungume kan Haidar cikin k’irjinta hawaye naci gaba da gangaro mata. Mai zai faru idan Haidar ya mance ta.? Mai zai faru idan D’anta bai kuma tuno ko wacece ita ba. Just when she thought rayuwa ta basu daman kasancewa tare a karo na biyu kwatsam wann tashin hankalin ya Kunno Kai.. Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un.!
Cikeda tsananin tausayi Ummul ke duban Mommy da Haidar hawaye na gangaro mata. Allah sarki Mommy ta jira farkawan D’anta ta sanar dashi how much she loves him sai gashi ya farka amma ba Lallai ya kuma sanin ko wacece ita ba.. Kai Lallai rayuwa abar tsoro ce.
Anisa ce ta kamo hannun Ummul itama guntun hawaye ne cikin idonta “Let’s go Ummul. Let’s wait outside.. Mommy needs some time with her Son alone.”
Ummul duban Anisa kawai take tana Jin zuciyarta na wani irin yankewa.. Tamkar rak’umi da akala haka tabi Anisa suka fice daga d’akin.
Kan Mommy na kife gefensa tana hawaye taji hannun Haidar saman nata.
“Mommy.!” Taji ya furta a hankali cikin murya irinta majinyata.
Ta d’ago tana dubansa yayinda Idanun Haidar ke kallon sama.
“Aliyu..!” Ta furta a hankali tana dubansa “Ka.. Kana iya magana..? Ka gane ni..? Ka.. Ka ambaci Mommyn ka.!”
Still idanunsa na duban sama yake fad’in “Even back then.. Lokutan da kike hukunta ni bisa laifin da ba nawa ba ban tab’a mance ki ba Mommy.. And do you know why.?!” Ya k’arashe yana mai karkato da fuskarsa suna fuskantar juna shida ita. K’walla ne tab cikin idonsa yayinda hawaye suka ci gaba da gangaro ma Mommy.
Haidar yaci gaba “Because you are my mother.! Ban tab’a tunanin rejecting d’inki matsayin mahaifiya ba. Haka ne.?”
Mommy taci gaba da hawaye yayinda Haidar yaci gaba da jinjina Kai siririn hawaye na gangaro masa “Koda ace wann D’an talikin yaron babu abinda yake mafarki da buri sama da soyayyar ki da kulawarki.. Not once have I ever looked down on you..!” Ya lumshe idonsa siririn hawaye ya gangaro masa.
Mommy ta lumshe idonta hawaye suka gangaro mata. Tana tuna rayuwar k’unci da ta ba ma d’anta ba tareda tayi la’akari ba.
Haidar yaci gaba da jinjina Kai yana duban mahaifiyarsa “Dukda duka wad’ancan abubuwan da kika mun.. Dai dai da rana d’aya Mommy ban tab’a danasaninki matsayin mahaifiya ba.. Ban tab’a hanaki yanke wani hukunci na rayuwata ba.! You dictated my whole life.. Karatuna..! Aikina.! Daga k’arshe har aure na Mommy… Kece kika zabo matar kika kuma yi a lokacin da kike so koda auren ya kasance k’ark’ashin yarjejeniya.! Koda ban kasance wann D’an da kike so mahaifinsa yayi alfahari dashi ba. Ban tab’a taka wani dokanki ba sabida ina ganinki matsayin mahaifiya.!” Suka ci gaba da duban juna hawayen Mommy na k’aruwa.
Haidar ya maida dubansa ga duban sama “Amma daga lokacin da na dubeki da kallo na k’ask’anci.. Na Miki kallon tir da zama mahaifiyata. Na kulle ki a kurkuku Mommy.. Na fad’a Miki kalamai masu tsanani Wanda duk rayuwar da mukai lokutan baya ban tab’a fad’a Miki irinsu ba.!” Sai ya d’an girgiza Kai kad’an “Ummulkhair..!” Ya furta a hankali kafin yaci gaba “Thanks to her na fahimci ke d’in Mahaifiyata ce. Kuma ba’a tab’a iyaye irin haka a zauna lafiya.!” Ya Kuma duba Mommy kafin yaci gaba “Na fad’a Miki kalaman ne cikin b’acin rai bayan kin sanar Dani labarin yanda kika salwantar da ahalin mahaifina... D’anuwana ko ‘yaruwata dake ciki bai zo duniya ba da kuma matar mahaifina da batada hakkin komai..!” Yaci gaba “Na mance cewa dukanmu ‘yanadam ne.. And we all have our shortcomings. Na mance cewa we all make mistakes and We are far from being perfect…!” Yaci gaba da duban Mommy daga nan yanda Yake kwance “Watak’ila na shiga hurumin da ba nawa ba..! She was right Mommy… Khairy was right, I shouldn’t have looked down on you.! I shouldn’t have locked you up in jail..! I shouldn’t have said all those horrible words to you.” Ya d’an karkato sosai yana duban mahaifiyarsa. Hannunsa na matuk’ar rawa ya d’aura saman na Mommy. Mommy ta dago da idonta masu zuban ruwa tana duban Haidar da kuma yanda ya d’aura hannunsa saman nata.
“Please forgive me Mommy..!” Ya k’arashe muryarsa na shaking sosai. The sincerity in his voice was clear.
Sai Mommy ta rungumosa daga nan yanda yake kwance saman gadonsa. Cikin kuka take girgiza Kai tana fad’in “Baka mun komai ba Aliyu.! Tun tasowarka ni ce na cuzguna maka na bak’anta maka rayuwa sabida son zuciya....! Tabbas abinda mutum ya shuka shi yake girbewa. Na cutar da Fannah da abinda ke cikinta dan na samu dawamammen farin ciki a cikin gidana. Shi kuma alhaki kwikuyo ne. Sai na samu akasin haka tsawon shekarun nan. Ban samu wann farin cikin ba. Bakada laifi ta ko wace fuska Haidar kuma banji ciwon abinda ka mun ba sai ciwon abinda ni na jima ina maka. Na aza maka nauyin zunubaina bisa kafad’unka ba tareda hakki ba.” Ta numfasa hawaye na kuma gangaro mata “Aliyu D’anah ina matuk’ar k’aunar ka.. Ina rok’on Allah ya bud’e Zuciyar D’ah na ya mun kwatankwacin kaunar da nake masa.!” Ta k’arashe hawaye da murmushi saman fuskarta.
Ya rik’e hannun Mommy cikin nasa sosai “I would pick my mother to be my mother again in any and every life time..
Farin ciki ya gaza b’uya a fuskar Mommy cewa da Haidar yai zai zabe ta matsayin mahaifiya a kowace rayuwa ya yaye mata wani burden da take kwana ta tashi dashi.
Daddy dake daga k’ofa Akan idonsa komai ta faru.. Murmushi out of nowhere ya subce masa ganin ahalinsa cikin yanayi mai ban sha’awa da bai tab’a gani ba. Kasa shiga d’akin yai sai ya juya ya fice yana jin zuciyarsa na masa wasai.. Koda ace baida k’warin gwiwan tunk’aran ahalin nasa a yanzu. Ganinsu haka cikin farin ciki Ya wadatar masa. Yana Jin wani annashuwa da sakinah da ya jima bai tsinci kansa ciki ba tsawon shekarun.
Koda ya isa company ma Alhaji Gimba ya fuskanci relief da farin ciki da abokin nasa ke ciki.
Alhaji Gimba ya murmusa yana duban Daddy alamun da magana a bakinsa.
Kafin yakai ga furtawa Daddy ya katsesa “A fad’a maka Haidar ya farka..?” Yai maganar har lokacin dai murmushi ne saman fuskarsa.
Alhaji Gimba ya kuma murmusawa “Ka fad’a mun wann the moment labarin ya same ka. Har ka mance.?”
Daddy ya d’an shafi goshinsa “Aff haka fah..”
“Ya baka zauna can ba.! Ai da kayi zamanka.. I have everything under control here.”
“Kwaise tana can.” Ya fad’i jikinsa a dan sanyaye wann karon. Dan har kawo wann lokacin Mommy bata daina sha masa k’amshin da ta tsira ba. Kallo guda zaka masa ka gane duk baya wani hayyacinsa.
Shiru Alhaji Gimba ya d’an yi kafin ya numfasa yace “Ka k’ara mata lokaci abokina.. Ita mace fah duk girmanta sunanta mace. Kuma su mata rauni ne dasu… Ba wuya an janye wayonsu da kalamai da kyautatawa.. Nan da nan sai kaga Sun sauk’a daga dokin fushi.. Amma fah idan aka kaisu mak’ura kalamai da lallama basa aiki nan take.. Toh fah wann karon kaine zakayi hakurin da ita.”
Daddy ya dan dubesa sai ya furzar da huci a hankali.. Ya kishingida cikin kujera yana mai lumshe idonsa.
**
A can asibiti kuwa Hisham ne yaje duba Haidar.
Yana zaune gaban gadonsa ya k’ura masa ido fuskarsa fal damuwa.
Haidar yai gajeren tsaki “Kasan dai bana so ayita kallo na.. It irritates me..”
Hisham ya Kai masa punch a damtsensa maras ciwo. Haidar ya dan saki k’ara yana fadin “You are such a jerk you know.!”
Hisham ya girgiza Kai “You are the real jerk here Haidar.! This isn’t a joke.. I mean, You almost killed yourself in that accident.. I know you so well.. Idan ranka ya baci tuk’i kake ba tareda kana sanin ina kake zuwa ba.!”
“Kana tunanin akwai b’acin ran da zaiza nai yunk’urin kashe kaina..? Hisham akwai wata cikin motar nan. And she happens to be my wife.!”
Saida Hisham ya dago ya kallesa jin ya ambaci Ummul da matarsa.
Haidar yaci gaba “You know me.. I wouldn’t put someone in harms way.. Koda ace ni mutum ne da ya yak’i ahalinsa tsawon rayuwarsa…” Yana jinjina Kai yake fad’in haka kafin yaci gaba “Abinda nake tunani shine… the accident was planned. Someone planned it.!”
Gaban Hisham ya yanke ya fad’i amma sai ya dake . Ya dan girgiza Kai kad’an yana karantar Haidar d’in “What do you mean.? Kana so kace kana zargin wani da shirya maka had’arin.? Kamar ya kenan Haidar.?”
Ya dan rage girman idona still yana duban Haidar d’in “Wait don’t tell me har yanzu zargin ahalinka kake da yunk’urin kasheka.. My goodness Haidar.. Wai har yaushe zaka watsar da wann tunanin ne..? Sai yaushe zaka watsar da makaman fad’anka Akan ahalinka. Until when Haidar.?!” Ya k’arashe cikeda nuna kulawa kaman dai ko Yaushe.
Haidar ya tsaresa sosai da ido “Someone tampered with my brakes.!”
Hisham ya dan girgiza Kai “But.. who could have done that.? I mean all your life you thought ahalinka sune mak’iyanka.. Dukda cewa kanada b’oyayyun mak’iya masu son ganin bayan ahalinka da family business dinku.. Ina nufin masu kai maka suka a company da media.. But basu tab’a yunk’urin kasheka ba.. “
Katsesa Haidar yai da fad’in “What if I have a new enemy..? What if someone’s holding a grudge against me..? What if someone wants to take their revenge on me.!?”
Cikin sakanni Zuciyar Hisham ke bugawa dan gani yake Haidar Ya gama ganosa ne.
Daidai lokacin akai knocking a k’ofa.. Mommy ce ta shigo fuskarta d’aukeda murmushi.
Hisham ya mik’e cikin k’ok’arin bama Mommy da Haidar waje. Ya gaida Mommy had’ida mata sannu da jikin Haidar kafin ya maida dubansa ga Haidar. Sallama Yai masa tareda fatan samun lafiya had’ida k’arawa da zasuyi magana.
Mommy tabi bayansa da kallo fuskarta d’aukeda murmushi. Shi d’aya ne abokin da zata iya cewa ta sani na Haidar.. Dukda ba wani saninsa tai sosai ba tasan wajen aikinsu d’aya kuma he’s very fond of her son.. Tasan duk Wanda zai hak’uri da halayyan Haidar Ya zauna dashi irin haka sai Wanda yake masa soyayya na gaskiya tsakani da Allah. Tana ji Har cikin ranta he’s a good influence for her son.
Farin cikin Mommy gaba d’aya ya gaza b’uya. Ta kasa zaune ta kasa tsaye. Tamkar k’wai hannun jariri haka take ririta Haidar. Gaba d’aya jinsa yake Awkward dan shi tun tasowarsa zai iya cewa babu wata alak’a mai kamanceceniya da wann tsakaninsa da mahaifiyarsa.
Ya d’an soma yunk’urin mik’ewa Mommy ta k’araso da sauri tana k’ok’arin taimaka masa take tambayarsa mai yake so.
A hankali yake furta “Is ok Mommy.. I can manage..”
Mommy ta gyara masa pillow ya kishingid’a sosai. Tana dubansa tana sakin murmushi…
Gani tai sai kalle kalle yake kaman yana neman wani abin ko yana so ya tambayeta wani abu.
Ta matso ta dafa hannunsa kad’an “Akwai abinda kake so ne Son.. Should I call the Dr for you..? Kana jin wani ciwo ne..?”
Ya d’an girgiza kai kad’an “Where is she..? Why isn’t she here..?!” Magana yai a hankali amma bai san Ya fito fili ba.
Mommy ta girgiza Kai kad’an tace “Wace kenan..?”
Ya dan dubi Mommy kaman bazai ce komai ba sai Ya tsinci bakinsa kai tsaye da furta “Khairy..!”
Farin cikin Mommy ya k’aru. Sai tace “Oh.. Ai Sun tafi tareda Anisa ta kaita gida. Nace ko zata d’ebo maka wasu kayyakin da zaka buk’ata. Amma nasan Watak’ila ma suna hanyar dawowa.”
Baice komai ba sai Ya d’an kuma yunk’urin mik’ewa alamun yana son sauk’owa daga saman gadon.
Mommy tai saurin tallafosa tana tambayarsa mai yake so.
Ya d’an dafa gadon yana fad’in “I need to use the bathroom..”
Mommy ta soma k’ok’arin dafa masa tana fad’in bari ta taimaka masa.
Ya girgiza Kai cikeda kokari mai nuni da jarumta “You don’t have to worry Mommy.. I can manage..”
Ta girgiza kai a’a Haidar Bakada wani k’arfi fah.. Duba ka gani..”
Daidai lokacin su Ummul da Anisa sukai sallama.
Mommy tai hamdala tana fad’in “Gwara da Allah Ya kawo ku. Maza k’araso Ummul ki taimaka ma mijinki..”
Haidar yai saurin katseta “I said I can manage, Mommy..”
Girgiza Kai Mommy tai “So kake ka fad’i ka kuma jin wani ciwon…?” Ta k’arasa ta kamo hannun Ummul da tai sororo ga zuciyarta da bai daina tsinkewa ba. Ta dank’a mata hannun Haidar cikin nata “Assist your husband.”
Bata tsaya sauraron komai ba ta janye Anisa da tai mutuwan tsaye nan wajen tana kallon yanda Mommy ta saka hannun Ummul cikin na Haidar.. Bata ankara ba sai ji tai Mommy tana janyota tana fad’in ta shige su basu waje.
D’akin ya rage saura Ummul da Haidar. Ya kuwa tsareta da ido fuskan nan a murtuk’e kaman ba shine ya gama jajenta ba.
Ta had’iyi abinda ya tsaya mata da k’yar dan tinda yai regaining consciousness bayan gaisuwa da tai masa basuyi wani magana ta fatan baki ba.
Takai idonta kan hannunta yanda Mommy ta had’e da na Haidar waje guda. A hankali ta soma k’ok’arin zame hannun amma sai taji ya matse hannun ya hanata abinda take k’ok’arin yi. Ta d’ago ta dubesa ita d’in yake duba har lokacin babu wani walwala saman fuskarsa.
Hannunta taji ya janyo ya zagaye bayansa dashi ya d’aura saman waist d’insa.. Ta kuma dubansa cikin fad’uwan gaba. Har lokacin bai janye ido daga barin dubanta ba.. Bata kuma ankarewa ba saiji tai ya d’aura hannunsa guda saman kafad’arta yayinda hannunta guda ke saman waist d’insa irin dai yanda ake taimaka ma maras lafiya idan zai tafiya..
Maimakon ta soma takawa sai shine dai yai yunk’urin tafiyar Kai kace itace maras lafiyan.
Muryarsa ta sinkayo yana fad’in “Don’t look at me like you’ve seen a ghost… They say monsters don’t die early.!”
Yai maganar kaman ba shi ba saida ta dan dago ta dubeshi tana mamakin kar dai yaji kiransa monster da ta dingayi sanda yake kwance unconscious. Sai ta tsinci kanta da Jin kunya ta sadda kanta k’asa.
A haka suka ci gaba da takawa Zuciyarta bai daina yankewa ba. Addu’a kawai take cikin zuciyarta Allah ya bata k’warin gwiwa..
Aiko suna shigewa bathroom din ta soma k’ok’arin janye jiki daga nasa..
Cikin in ina take furta “Zan.. Zan jiraka a k’ofa..” Juyawan da zatai ta kunna musu shower akansu.. Haidar ya janyota jikinsa gaba d’aya “What if I fall..?” Ya fad’i yana mai manne goshinsu waje guda su duka biyun idonsu a lumshe. Sosai Ummul ta rintse idonta tana Jin yanda karan hancin Haidar ke gogan nata ga ruwa dake zubo musu.
“Amma.. Amma.. Naji kaman kace ma Mommy zaka iya..” Ta fad’i da kyar cikin k’ok’arin ganin ya k’yaleta ta fice. Amma sai taji ya kuma had’e fuskokinsu waje guda.
Murya na rawa ga ruwa dake jik’asu tace “Mai.. Kake aikatawa..?”
“I’m rebuilding my life..!” Ya furta a hankali saitin kunnenta kafin yaci gaba “Isn’t this what you want..?”
Tai saurin ware idonta tana dubansa zuciyarta naci gaba da bugawa.
Haidar yaci gaba “Isn’t this what you promised Mommy… That you’d help her son…rebuild his life… Are you scared now..?” Yai maganar yana mai kuma rungumeta cikin jikinsa. Cikin sigan rad’a yaci gaba “Are you sure you are ready to invade my sick world..? Don’t you think you are taking too much of a risk..? Are you not scared of a monster..?”
“But you are not a monster…!” Ta furta cikin rawar murya.
“What makes you believe… That… I’m sweet…?” Yai maganar d’umin numfashinsu na gaurayuwa da juna. Kaman zai sumbaceta. Har lokacin idanun Ummul suna lumshe. Ga heartbeat dinta dake k’aruwa.
Ta kasa furta komai sai k’ok’arin cire jikinta daga nasa da tai dan ta gama amincewa yanzu kam duk wasu maganganun da tai sanda yake kwance yaji komai.
“Zan… zan jiraka a k’ofa ta fad’i tana mai tamke tufafin dake jikinta cikin tsananin rawar murya. Kaman zata kifa haka ta fice tana had’e hanya. Haidar yabi bayanta da kallo murmushin da ba lallai ka fahimta ba saman fuskarsa.
Ummul kaw tana ficewa ta jingine jikin k’ofa tana maida numfashi.
A b’angaren su Mommy kuwa Asshe ta iso gari dan haka Kai tsaye ta taho asibitin yanda ta tadda ‘Yaruwar tata.
Suna zaune saman wani kujera a wani hanya da zai sadaka da hanyar dakin Haidar d’in.
Asshe taci gaba “Aunty Kwaise yarinyar nan annoba ce.. Tsautsayi ke bibiyarta.. Ya kamata ayi gaggawan datse aurenta da Haidar… Allah na tuba bamusan dalilin da yasa boka yace mu aura masa mace irinta ba..”
Anisa da karyo kwananta kenan zata nufi d’akin Haidar ta sinkayi tattaunawar iyayen nata. Ta zaro ido waje tana dafe k’irji “Boka.!” Ta furta a hankali. Lokaci guda ta gyara tsayuwarta ta lab’e sosai.
Mommy ta girgiza Kai tana duban Asshe “A’a Asshe na yada batun boka tuntuni kuma na k’aryatasa kaman yanda Ayoyin Alk’ur’ani mai tsarki ya k’aryatasa a wajaje da dama. Asshe ba shakka munyi kuskure a yanda muka faro Auren Haidar da Ummul.. Amma na gode ma Allah da ya nufeni da tuba ya kuma bud’e min ido na na gane gaskiya dalilin shigowar Ummul cikin rayuwarmu. Sann inada yak’inin Auren Haidar da Ummul Alkhairi ne Asshe. Domin shigowar Ummul cikin ahalinmu shi ya fargar damu gaba d’aya.. Ita d’in ta zamto tamkar wani igiya mai k’arfi da ta had’e ahalinmu waje guda ta d’aure Asshe. She’s an Element of Union.. Na shafe skaru sama da talatin ina fad’i tashi da ganin na had’e kan ahalina sai gashi cikin watanni biyu na zaman Ummul tareda mu Allah ya jefa wann had’uwan ahalin da soyayyar d’ana da mijina da nake buri. Kuma in sha Allah Ummul ko Haidar cikin su babu Wanda zai San ga Manufar aurensu daga farko. An Gina auren ne bisa sharad’in boka domin a raba Haidar da wancan Hatsabibiyar da tai masa sihiri Wanda a halin yanzu ma bana tunanin suna tare.”
Anisa ta zaro ido waje tana Jin sirrin Auren Ummul da Haidar Wanda ba yanda batai ba Mahaifiyarta ta sanar da ita. Dama wann shine dalilin da yasa Kwaise Maitama ta auro ma D’anta D’iyar talakawa da taita mamaki daga farko.? Dama wann shine dalilin da yasa Mommy hak’uri da Ummul da nuna mata unconditional love.? Tirk’ashi Lallai yau akeyinta.
Mommy taci gaba “Asshe kimin alk’awari babu Wanda zai San wancan manufar tamu na farko domin na riga na bisne wancan manufar na lullubesa da tuba na gaskiya. Ummul da Haidar zasu rayu a k’ark’ashin inuwar aure tsawon rayuwarsu cikin yarda Ubangiji aure mai cikeda d’imbin albarka ba AUREN WATA UKU mai k’ayyadadden lokaci Wanda Boka mak’aryaci yaima Ummulkhair alk’awarin mutuwa ciki ba.!”
Anisa sai ta sake baki tana fito da ido waje.! Mutuwa..? Shiru tai tana sauraron yanda Mommy ke zayyano sharud’an boka gameda auren cikeda nadama. Anisa ta kasa rufe baki dan mamaki. Kenan An auro Ummul ne dan ta zamto makarin asirin da akai ma Haidar. Sai yanzu ta gane manufar turaren da Mommy ta bata ta bama Ummul. Sai wann lokacin take fahimtar komai.. So Mommy isn’t as innocent as she thought.. So duk wann soyayyar da Mommy take ma Ummul na k’arya ne tana mata so ne out of guilt tinda ta kawo ta cikin rayuwar D’anta ne dan ta kasheta ta kuma ceci nata D’an. Muryar Mommy ya kuma dawo da Anisa daga duniyar tunanin da ta tafi.
Mommy ta kuma kamo hannayen Asshe “Asshe Alhamdulillah ahalina Ya fara daidaita cikin ikon Allah. Bazan kuma yin wani abu da zai tarwatsa min wann farin ciki da na jima ina fatan samu ba. Haidar da Ummul harma da Engr bazasu San ga manufar auren ba… Asshe idan suka sani ahalina zai kuma tarwatsewa Watak’ila yai rushewar da baiyi ba a baya… Kimin alk’awari kaman yanda muka shirya komai daga farko tare zamu bisne wann magana kuma bazamu sake d’agota ba har abada.” Ta k’arashe tana duban Asshe.
Asshe Tai shiru tana duban ‘yaruwar tata dan dik yanda Anisa ke sanar da ita irin makancewar da Mommy wajen nuna ma Ummul so bata kuma gaskatawa ba sai yanzu “Amma… Aunty Kwaise..”
“Babu amma Asshe. Inada yak’inin kafin a sallami Haidar daga asibitin nan shida Ummul zasu k’ulla alak’a mai kyau tsakaninsu.. Zasu k’aunaci juna a hankali. Domin da zaran an sallamesa ni Kwaise zan shirya gagarumin bikin na gaske. Za’ayi komai cikin mutunci da karramawa kaman yanda yake a al’ada. Za’a sallami Haidar ne tareda bikin tafiyarsa da matars in sha Allah. Ni da kaina zan tafi wajen dangin Ummul muyi masu gaisuwa a k’ulla alak’a da zumunci mai tsafta..” Ta k’arashe kyakkyawan murmushi saman fuskarta.
A hankali Anisa ta soma jada baya.. Shigowan da batai ba kenan ta soma tafiya jiri na neman kada ita.
Tana fita ta soma neman layin Hisham. Bugu biyu a na uku Ya d’aga.
“Tell me your location.” Abinda kawai Anisa tace kenan…
Hisham na sanar da ita location d’insa tasa kai zata fice sai kuma taja birki ta tsaya kaman wacce ta tuna wani abu. Ji tai ta k’agu ta tunk’ari Haidar da Ummul ta sanar dasu irin Auren yaudara da Mommy ta k’ulla tsakaninsu.
A b’angaren su Ummul kuwa tana nan lamo jingine jikin k’ofan bathroom taji motsin tab’a k’ofan alamun zai fito. Tai k’ok’arin saita kanta tana mai taimaka masa da bud’e k’ofan.
Suka dubi juna sai ta kauda fuskarta kad’an. Gaba d’aya saima ta rasa mai zatai musamman da taga yanda yake dubanta daga nan yanda yake tsaye dafe da garu.
Baice da ita komai ba sai soma takowa da yai. Ta yunk’ura da zummar magana saiji Tai ya kuma kamo k’ugunta had’ida tallafo kafad’an ta guda. Sukai tsaye nan haka suna duban juna.
A haka Anisa ta turo k’ofa taci karo dasu rungume da juna suna duban juna ga jikkunansu duk a jik’e. Takaici yakai Anisa k’ololuwa. Banda sakin huci bata komai. Wai Haidar Maitama ne dai take gani rungume da wann kucakar harma kaman ya makance a shauk’in kallonta baisan an tab’a k’ofa ba balle Ya kula da Wanda Ya shigo. A zuciye Anisa ta janyo k’ofar ta fice, kukan da ta rasa na takaici ne ko na kishin Abun k’aunarta Haidar ne na kufce mata. Haka ta fice tana kuka shar shar take driving. Da alama duk wani effort dinta a banza yake tafiya dan duk k’ok’arin taga Haidar da Ummul basu samu kusanci ba kaman k’ara rura wutan abun take.
Koda ta isa location d’in Hisham bata daina kuka ba.
Hisham Ya tsareta sosai da ido had’ida bata lokaci dan ta fitar da k’uncin dake ranta. Ganin dai kukan Anisa bazai k’are ba dan tinda tazo yanda yake kul take ta kasa cewa komai.
Hisham yai tsaki kad’an “Ke enough please. Ya isa haka mana.! Wai meye kikazo kika saka ni gaba kina kuka.? Ok dama kin nemi sanin yanda nake ne kawai dan ki cika mun kunnuwa da sautin kukan ki. Ai da baki b’ata mana lokaci ba daga ni har Ke tinda idan kinyi a waya ma zanji.”
Anisa ta d’ago tana huci “We can’t let them be happy while we are stuck here just.. Freaking miserable you know..! Wllhi na tsani Ummul.. Na tsaneta.. Na tsani Mommy da taima Haidar AUREN WATA UKU.. Auren karya asiri da ita.. I hope she dies kaman yanda Boka yace.!”
Da mugun mamaki Hisham ke kallonta.. Ya girgiza Kai cikin rashin Fahimta “Mai kike nufi..?!”
SameenaAleeyou📚

Dan allah abamu ⁴⁴
ReplyDelete