Rumubun Qaya page 61

Rumubun Qaya page 61

Rumubun Qaya page 61

RQ

      61

***Kwanon dake kan kafarta ta yi jifa dashi saboda tsabar kidimewa. 


"Na shiga uku, dan girman Allah ku fita da ita." Tace cikin k'araji 


"Hegiya ashe kinsan girman Allah." 


Ladi tace tana kwashewa da dariya, 


"Matso ciki Lawwali, tasan ba da wasa muka zo ba. Kwarankwatsa dubu idan baki sanar mana da duk abubuwan da kika dinga aikatawa ba sai kurar nan ta gwaigwayi kafarki."


Ta jawo hannun Lawwali ta turo shi zuwa wajen da Hajiya Zeenat din ta makale idanun ta sun fito waje cikin tsananin tsoro. A dan zaman da tayi da Ladi ta fuskanci mace ce jajirtacciya mara tsoro kuma, duk hargagin da take mata be sa taji tsoro ko karaya ba, burin ta kawai tagan ta a masifa.


"Na roke ke ki girman Allah ki kyale ni, na miki alkawari duk abinda kike so a duniyar nan zan miki Shi wallahi."


"Na sha gaya miki babu abinda zaki iya bani,matsiyaciya ma irin ki, me rayuwa a cikin kudin haram da jinin mutane."


"Zaki gaya mana ko sai na sako miki ita?" Lawwali yace yana zama so serious sannan yayi kamar zai saki kurar da take ta faman fitar da harshen ta


"Zan fada!" Tace da sauri


"Taji uwar bari, yar tasha. Zauna ki nutsu ki fara tun daga farko, kuma wallahi kikayi mana karya sai kin yabawa aya zakin ta."


"Zan fadi komai wallahi, amma kafin nan waye ya saku kamani? Aryan ne ko?"


"Tun yaushe nake gaya miki bamu wani san Aryanu ba, kin ga alamun wai mutane tunda kika zo wajen nan?"


"A ah."


"Toh mu ma aljanu mun gaji da shegen halin ki ne shine muka ga dacewar dauko ki mu kawo ki nan, tunda kin zama annoba cikin al'umma."


"Aljanu?" Tace tsoron nata yana ninninka na da sau dubu


"Kwarai, dan haka kiyi da jiki ki fada mana komai da bakin ki, duk da mun sani amma ta bakin naki muke son ji, kuma na rantse da girman me dukka kika yi karya sai kurar nan ta gwaigwayi kafarki."


"Na rantse zan fada,wannan wacce jaraba ce? Babu me nema na ne?"


"Ko sun neme ki ba samun ki zasuyi ba, alkadarin ki ne ya karya, sai ma kin soma ganin sakayya."


"Wannan masifa dame tayi kama?"


"Da uwarki tayi, do Allah Lawwali idan ba zata sanar damu ba mika mata lanto ta dan gutsiri kaurin shegiya."


"Zanyi." Tace ta zauna sannan ta nutsu sosai ya mikawa Ladi camerar ya nuna mata yadda zata rike aikuwa ta shiga daukar ta tana bayani tiryan tiryan tun daga farko har karshe, sosai Ladi ta yi masifar firgita da matar tsoro ya kamata dan bata taba ganin tsantsar zalunci irin wannan ba, amma sai ta dake kamar bata ji komai ba ta boye yanayin da ta shiga har suka samu duk bayanan da suke so. Lallai Hajiya Zeenat abar tsoro ce, domin samun mara Imani kamar ta zai yi yuwa duk da akwai su sosai amma kuma bata dauka ana irin wannan masifar ba. Ta cuce su ta bata musu rayuwa da lokaci sosai. Jikin ta yayi sanyi kalou ta fice daga dakin bayan tasa Lawwali daure kurar a daidai kofar dakin Hajiya Zeenat din da sau kusan uku suna shuna ta yi balain tsorata.


  Tagumi Ladi ta zabga sai kuma wasu hawayen tausayin Aryan da ahalin su ya saukar mata, da tasan irin wannan kalar rashin adalcin akayi musu da bata bari ko ruwa Hajiya Zeenat din tasha a gidan ba, lallai ma yana da karfin zuciyar da har ya iya kulawa da ita anan din ma. Zame fuskarta tayi real fuskarta ta fito, itace dai mai aikin gidan nasu wanda Hajiya Zeenat ta kora saboda yadda take kula da Aryan din,ashe bayan tafiyar ta abubuwan sun sake lalacewa sosai. 

  Abinda suka dauka Lawwali ya turawa Aryan ta WhatsApp domin dama abinda Aryan din yake so kenan. 



***Tura kofar yayi da hannu daya da babu abincin a hannun sa ya shiga da sallama. Tashi tayi zaune tana amsa sallamar sannan tana kokarin gyara rigar jikinta da ta dan ya mutse. Akan bedside drawer ya ajiye dan karamin tray din yana kallon fuskarta da yanayin walwalar ta. 


"Tashi kici abinci." Yace yana zama a gefen. Zaman ta gyara sannan ta dauki tray din ta sauke shi k'asa ta zauna a gabansa tana kallon kayan ba tare da ta taba ba. Zamowa yayi ya zauna a kusa da ita ya bud'e ya saka mata fork yace taci. Bata ce komai ba ta dauki fork din ta soma cin stir fry spaghetti da minced meat me dan karen dadi. Ganin ta fara ci ya sashi komawa saman gadon ya dauki wayarsa ya kira Ya Nabeela.


"Yanzu nake shirin kiran ka." 


Tace tana zaune tare da Dr Farouk yana dinner a tsakiyar falon su


"Nima abubuwan ne suka yi min yawa na manta, thanks for the food."


"Nasan dama kun gaji sosai dole,kira zanyi nace ina kanwata wai? Shiru an dauke min ita ba wani bayani dai?"


Kallon shashen da take zaune yayi sai yayi murmushi kad'an mara sauti, Ya Nabeela ba abokiyar maganar sa bace irin wannan amma da sai ya bata amsa. Abu daya kawai ya sani shine ta dawo kenan, yan kwanaki kawai zasu kara su fice daga k'asar gaba daya sai kuma an gansu. Dstriya Kawai tayi jin yaki magana ta kuma tabbatar da ba zai yin ba dan tasan halin sa, dama kuma Dr ya fada mata an ga Aryan din a passport office yaje renewing sannan yace zai kawo Raihanan itama, wani abokin sa a passport office din ne ya gaya masa tun last two weeks ma. Sallama sukayi bayan ta tambayi jikin Ammyn sannan tace zata shigo gidan gobe tare da Khadija Matar Kamal su dubata sannan su taya Raihana zama. Ajiye wayar yayi ya dan leka plate din sai yaga taci sosai, dadi yaji domin baya son yanayin da yake ganin tan. Mikewa tayi a hankali zata dauke plate din ya hanata ta hanyar rigata dauka.


"Allow me please, your majesty!" 


Yace yana sakar mata tsadadden murmushin nan nasa. Murmushin ta samu kanta da yi domin taji dadin yadda yayi maganar. Dauka yayi ya fita ita kuma ta yafa mayafin ta, ta fito zuwa dakin da Ammyn take ta tarar tana baccin ta a nutse. A gabanta ta durkusa tana kallon fuskar ta hawaye na bin fuskar, bata san wanne irin godiya zatayi ma Aryan din ba, soyayyar sa da matsayin sa ya karu sosai a wajenta har tana jin zata iya zama dashi a kowanne irin hali. Ya dan dau lokaci a dakin tana jin kamar tayi kwanciyar ta a bayan Ammyn amma kuma sai ta tuna zai bukace a kusa dashi tunda ita Ammyn bacci take kuma ba lallai ta farka ba kwata kwata ma sai zuwa safiya, tasan kuma Hamma Hydar da Hamma Lamido zasu dinga dubata sai kawai ta tashi bayan tayi mata addu'a ta jawo kofar ta fito ta koma dakin. Babu kowa a ciki,yaga lokacin da ta shiga dakin Ammyn shiyasa kawai ya haye sama bayan ya samu sakon Lawwali ya hau kan aikin kawai a gaggauce. 

  Shiru shiru be dawo ba, ta tashi tayi shafai da wutri sannan ta zauna tana yiwa Ammyn ta addu'a ta dade a zaunen sai gashi ya shigo, babu haske ko kad'an a corridor din alamun sun kwanta su Hamman ta, sai hasken dakin kawai yayi tunanin ma ko bata dawo dakin ba tana wajen Ammyn amma ga mamakin sa sai ya ganta a zaune akan abun sallah.   Mikewa tayi ta nannade abun sallar ta ajiye ya karaso cikin dakin ya tsaya a gabanta. Hijab din jikinta tayi niyyar cirewa amma sai ta fasa tayi tsaye tana jiran me zaice.


"Baki bacci ba? Na zata fa kina wajen Ammy."


"Yanzu na dawo." Tace dan kar ya gane zaman jiran sa take yi har ta gaji.


"Zaki koma ne?"


"Eh." Tace kamar da gaske take. Sai ya langabe kai


"Ba zaki tayani kwana ba?"


"Um um, wajen Ammy zanje ni." Tace tana kewaye shi zata wuce. Riko ta yayi yana kokarin hana kansa yi mata dariya domin ya riga ya gano ta tun daga yadda ta amsa masa da farko.


"Wajen Ammy zani."


"Wajen Ammy zani." Ya kwaikwayi muryar ta yana murmushi.


"Muje ki tayani wani aiki a daki na, idan muka gama sai ki dawo wajen Ammyn ko?"


D'aga masa kai tayi sannan tace


"Zan dawo ko?"


"Emana, me zaki zauna kiyi a chan? Zaki dawo ai dole."


"Ok." 


Tace a tunanin ta da gaske yake da yace zata dawo din, rashin rigar jikin sa ya hanata sakewa dashi har taji tana son komawa dakin Ammyn. Saman suka haye hannun sa a jikin nata zuwa bedroom din nasa da yake shi kadai a bud'e a saman. Murd'a kofar yayi ya dan yi baya ya bud'e hannayen sa yace


"Ladies first." Shiga tayi a nutse ya bi bayanta gami da rufe kofar hade da danna lock dinta yadda babu me iya bud'e ta sai shi, dama security door ce tunda duk abubuwan sa a dakin suke. 

  Kallon yadda dakin yake a hargitse ya ajiye riga chan takalmi chan ga shi ya barbaza takardu a saman gadon sai system dinsa dake a kunne jone da wayar sa. Wuce ta yayi zuwa gaban gadon ya hau tattara kayan dake kai. Sauran kayan ta hau kwashe masa tana tayashi suka kwashe komai suka saka shi a muhallin sa yayi sauran sai computer kawai da wasu papers. Gadon ya haye yace tazo ta gani ta matsa gaban gadon ta tsaya tana leka system din. Dagowa yayi ya kalle ta yayi murmushi kawai yace


"Zauna anan." 


Zama tayi tana kallon jikin system din ya cigaba da jujjuya mouse din ba tare da ta gane abinda yake ba, be dau lokaci yana yi ba ya tattara ya rufe ya dauki system din ya dora ta akan reading table dinsa ya jona ta jikin socket ya wuce toilet. Fitsari yayi ya sake wanke bakin sa da mouth wash sannan ya fito ya tarar da ita tsaye tana jiran ya fito ya bud'e mata ta tafi. Towel ya dauka ya goge fuskar sa tana tsayen ya dauki body spray ya fesawa jikinsa sannan yace ba tare da ya kalle ta ba


"Cire Hijab din mana bakya jin zafi ne?"


"Ai wai tafiya zan dama."


Murmushi yayi gami da taune lips din k'asa ya girgiza kansa kawai yazo ya wuce ta ya kashe hasken dakin gaba daya. Kirjinta ne ya buga ta hau wara ido tana waigawa. Takowa yayi har inda take tsaye sannan ya riko ta gaba daya jikin sa ya zare mata Hijab din dake jikin ta ya jefa shi kan sofa, ya d'aga ta chak ya nufi kan gadon nasa da ita.


"Taf..fiya fa zanyi." Tace cikin in da in da, ya dire ta a saman gadon sannan ya dora mata dukkan nauyin sa yana jin har sai da tayi yar Kara


"Me yasa kike da tsoro ? Umm?"


"Tsoro? Ni ba tsoro nake ji fa, tafiya zan."


"Ba wani, ina ganin yadda idanun ki suke shigewa da tsoro, me nayi?"


"Ba komai."


"Ba wani, tsoro na kike ji bayan ni babu abinda nayi miki, infact nine ma ake wahalarwa da rayuwa dan an ganni bawan Allah babu ruwana."


"Me nayi maka?"


"Gashi nan, kinsan dai ai ba haka miji da mata suke rayuwa ba ko? Kina ji kina gani Ya Nabeela ta hanani ke, kamar ma dadi kike ji har wata kiba kikayi ta musamman."


Ya taba saman wuyan ta zuwa saman kirjinta.


"Ni Allah ba ruwana, yanzu fa wajen Ammy zanje."


"Um um ni ba in da zaki. Anan zamu kwana Hydar suna k'asan babu abinda zai faru."


"Toh d'aga ni."


"Ina da nauyi ne?"


Gid'a masa kai tayi


"Haka zaki dinga daukata."


Da sauri ta kalle shi, dan hasken da ya hasko daga corridor din wajen window ya bata damar ganin fuskar sa. Daga mata gira yayi sannan yace


"Gwara ma ki saba da nauyin."


Shiru tayi bata ce komai ba, ya dan sassauta yadda ya danne tan sannan ya mirgana gefen ta ya jawota ta dawo saman jikinsa gaba daya, yasa hannayen sa ya zagayo su ta saman bayan ta ya riketa da kyau.


"Ke baki da wani nauyi, a haka zamuyi bacci. Goodnight." 


Yace yana rufe idon sa. Kwantar da kanta tayi a saman kirjinsa lamo tana sauraron heartbeat dinsa da take fita da dan sauri, dago kanta tayi daga kai da sauri da niyyar yi masa magana bakin sa da dama yake daidai saitin kan nata ya hadu da nata, cikin wani irin salo ya kama lips din nata ya shiga kissing dinta da sauri da sauri. Gwalalo ido tayi ganin yadda ya soma birkicewa, ya shiga hautsinata ta ko ina yana cigaba da kissing din nata, hannun sa dake jikinta ya shiga zazza gayawa a jikin ta yana bin ko ina da ko ina. Sosai ta kara tsorata domin yanayin sa na yau har ya fiye mata na kullum, da zafi zafi yake komai ya kuma k'asa tafiyar da ita a hankali kansa tsaye kawai domin da gaske ya kai karshe a hakuri, dama irin su ka kalle su kawai amma idan suka birkice maka zaka dauka basu bane ba. Cikin salon da yake mata da yafi karfin hankali da tunanin ta, taji shi sama sama yana kokarin aikata abinda kwakwalwa da gangar jikinta ba zasu iya dauka ba. Kuka ta fashe masa da karfi fiye da wanda take yi a dazun. Be ji ta ba  kwata-kwata, ko da ma yaji ta toh ba zai iya fasa abinda zuciyar sa ke ingiza shi ba, duk kuwa da ya riga yayi ma kansa alkawarin har sai komai ya daidaita, amma ya k'asa, ya gaza hakurin. Muryar sa a matukar shake taji kamar yana karanto addu'ar da manzon Rahma ya koyar damu, anan hankalin ta yayi masifar tashi, ta tuna Ammy, Lamido d Hamma Hydar duk suna gidan, tabbas za'a yi abin kunya idan ta miye ma Aryan, amma kuma ya zatayi? Idan ta ki tabbas zata kware shi, amma kuma ba zata iya ba, hankalin ta ba zai iya daukar azabar da take ji ba, kuma ba zata iya daukar matsanciyar kunyar da zasu shiga ba. Daidai saitin kunnen sa ta shiga gaya masa


"Ammy nah, dan Allah! kayi hakuri. Dan Allah zan mutu wallahi dan Allah, Wayyo hamma na."


Sunan Ammyn ne ya shiga kunnen sa sosai, sai kuma tunanin suna cikin gidan ya fado masa. A wani irin yanayi ya zame jikin sa da sauri, ya mike kamar zai fadi ya nufi toilet ya sakar ma kansa ruwa idanun sa a rufe. Tashi tayi da sauri ta hau lalubar kayanta da yayi mata watsi dasu, da k'yar ta gano rigar tata a k'asan gadon ta saka, gaba daya jikinta wani irin ciwo yake mata da zafi. Bakin ta har wani zum yake saboda a zaba, tana jin karar ruwan a toilet din sai dai babu motsin sa ko kad'an, tasan ba abu bane me sauki a garesa ba, musamman tunda ta riga ya saka rai sosai.amma ya zatayi? Sakkowa tayi idon ta ya sauka akan wayar sa ta dauka ta dan haska tayi wajen kofar fita amma still ba zata iya budewa ba, hakura tayi ta dawo ta zauna akan sofar tana jiran ya fito. Ya dade sosai a ciki har sai da yaji ya dawo daidai sannan ya dauro alwala ya fito daure da towel, ya wuce ya dauki jallabiyar sa ya saka sannan ya dauki sallaya ya shinfida ya tada sallah. Tana zaune har ta gaji ganin bashi da niyyar tsayawa, sai kawai ta koma saman gadon ta kwanta tana curewa waje daya tana leka shi, har ta gaji bacci ya dauke ta. Ya dade akan abun sallar sannan ya nannade ya ajiye yazo daidai saitin kanta yana kallon ta cike da tausayawa. Allah ya rufa asiri da an yi abun kunya, shi kansa ba zai so hakan ta faru ba, yafi so daga shi sai ita yadda zai kula da ita sosai. Be san me ya hau kansa ba har ya kasa controlling kansa ya tafi haka da karfin sa. Kissing saman goshin ta yayi, ta sauke ajiyar zuciya a wahale, ya dan gyara mata kwanciyar ta shiga gadon sosai dan da a gefe take, sannan ya kwanta a dayan side din yana kallon innocent fuskarta.

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post