Daudar Gora book 2 page 95 end

Daudar Gora book 2 page 95 end

 

Daudar Gora book 2 page 95 end

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲     

  ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨

           (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

            𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (95 END)

______________

*_MAAB LUXURY HOME._* _Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini. Ina uwar gida da Amarya, Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*_.

_____________

..........Wata irin mahaukaciyar razananniyar ƙara ta saki lokacin da kibiyar mashin ke sauka a cikin idonta ɗaya. Kafin ta gama dawowa cikin hayyacin azabar data shigeta suka sake soke ɗayan ma. Tuni jikinta ya shiga matsanancin karkarwa ta cigaba da ihun ambaton gumakansu. Na uku kama sai da suka saita maƙogwaronta sannan suka sakeshi. Kakari ta shigayi irin na mai fitar rai. Yayinda al'umma ke ta faman kabbara. Gaba ɗaya Iffah ta juya ta rungume Shahan-shan tsam-tsam ta fashe da kuka. Hannu biyu ya amshi abarsa ya rungume ko tuna ɗunbin mutanen dake a zagaye da su ma bayayi. Ai tuni jami'an tsaro da Ghazi dake zagaye dasu suka musu zobe, yayinda ƙatuwar umbrella ta musu runfa daga sama. Ganin wannan damar ta samu Shahan-shan ya ɗago fuskar sohaa ɗinsa ya manne lips ɗin sa a kan nata cike da ɗunbin so da ƙauna. Murmushi mai sanyi da ƙayatarwa kawai Malikat Haseenat tayi ita da Iyyani....


        Shike nan kuma an shafe da babin Uwar mushirikai itama. Wanda mutuwarta itama kuma yay dai-dai da haihuwar Daneen Ammarah ta samɓalo ƙyaƙyƙyawar ƴarta mace mai kama da babiy. Ai sai bikin al'ada ya cigaba dana murnar haihuwa, yarinya taci suna Arfah. Zo kaga farin ciki wajen Iffah Nina Arfa ɗin ta ta sake dawowa. Daneen Ammarah kuma ta cika alkawari, dan a ranar a gaban kowa ta damƙa Arfa ga Ummu. Ummu tasha kuka matuƙa Mamy na tayata. Daga ƙarshe ta dawo mata da Arfa akan ta bata shawayarwata har yaye. Babiy da Kaka dai nasu murmushi ne hakama Hanash da shima matarsa ɗauke take da ƙaramin cikin itama dan tanata fama ma da laulayi.....



        *_BAYAN WASU SHEKARU_*

         


    Abubuwa da yawa sun faru, wasu masu daɗi wasu marasa daɗi. Wasu a tuna wasu baza'a ma iya tunawar ba. Haka rayuwa ta gada dama. Zuwa yanzu kam zamu iya cewa hankalin Iffah da Tajwar Eshaan ɗinta ya kwanta sosai, dan manyan matsaloli dai sun ɗan ragu musu musamman wanda suka shafi tsafe-tsafe da sauransu. Amma na maƙiya kam har goben-gobe a kwaisu. Dan duk inda bawa yake, komai ƙyautatawarsa ya sani akwai wanda su burinsu kawai cin dunduniyarsa. Ƴar uwa karki damu, kamar yanda Bily bata damuwa. Dammu masoyanmu sun wadatar damu😘. Haka dama rayuwar take dole ka kasance a zagayen abu biyu, (Masoya da maƙiya) idan ka kwantar da hankalinka duka sai su amfanar da kai. Idan har MANZON ALLAH da yafi kowa a halitta, ɗan gatan ALLAH zai fuskanci ƙalubale na maƙiya, masu hassada da kushen abinda yazo da shi daga umarnin UBANGIJI kai waye da bazaka samu kanka da irin waɗan nan mutanen zagaye da kai ba. Kai dai kawai yi abinda zaka iya, kuma ƙyautatama duk wanda ke tare da kai maƙiyi ko masoyi duk zakai alfahari da hakan wataran. Wannan shine abinda su Iffah da Tajwar Eshaan suka haƙƙaƙewa rayuwarsu da zukatansu suka zauna lafiya. Sun ajiye komai, basa ganin komai sai kansu da masoyansu. Sun fi kallon masoyansu fiye da tuna maƙiyansu, suna shimfiɗa mulki a tare cikin gaskiya da riƙon amana, randa suka sami saɓani kuma sukan binne a tsakaninsu suyi haƙuri dan yau da gobe sai ALLAH. Duk inda zo mu zauna take sai ka samu zomu saɓa. 

         Iffah ta ƙara haihuwar ƴarta mace taci suna *_Bilqeesa_* (Dan bazanyi a banza ba sai na ma kaina takwara a ƙasar ruman ehe🥱😂). Ajwaa da Ajwaad sun girma abinsu masha ALLAH. Yara ƙyawawa da ke samun soyayya ga mutane, wasu ko basu da wanda suka tsana kamar su a yanzu musamman ma Miran Ajwaad da kowa kema kallon magajin mahaifinsa. Sai dai kuma babu abinda suka isa yi dan tun ran gini tun ran zane.

    Burin Iffah ya cika akan karatu, inda a yanzu haka ta zama cikakkiyar ƴar jarida koma muce shugabar gidan jaridar nan na *African eye* da mijinta ya kafa. A zahirance dai kamar yanda yake ɓoye kansa a baya itama haka take ɓoye kanta a yanzu. Sai dai rubuce-rubucenta da zaƙule-zaƙulen sirrikan munafukai na matuƙar tada hankalin wasu. Dan a duk lokacin da tai wani rubutu game da wata ɓarnar da akeyi koma ta fitar da muryar wasu da abin ya shafa kusan duniya ɗauka take aita cecekuce musamman da ya kasance bayan kafofin yaɗa labarai a yanzu social media ma na taka rawar gani akan yaɗa abu cikin sauri. Sai ta gama zaƙulowa da tallace mutum mijinta kuma gwarzonta ya zama gaba-gaba wajen hukunta mai laifin idan a ƙasar sa ne. Idan ba ƙasarsa bane zai yi duk yanda zai yi ga shugaban da ke shugabanta ƙasar da mai laifin ya fito dan ganin an hukuntashi, cikin ƙananan lokaci sunan da take amfani da shi yay wata irin amsa kuwa, mutane har zalamar jiran fitar wani abu da ga African eye sukeyi, dan sun san mai amfani ne kuma na gaskiya ne. Takanyi ayyukanta a gida, idan kuma fitar sirri ta kama sukanyi ita da Mijinta harma subar ƙasar batare da wani ya sani ba koda a masarautar ne kuwa. 

       


      ★★...


  Ƙoƙarin kamota yake tana zillewa, ya kwaɓe fuska da ɓata rai kamar gaske. Gwalo ta masa da ga inda take tana cigaba da dariyarta mai narkar da shi. 

     A hankali ya furta, “ALLAH Sohaa karki bari na kamaki, kizo nan na yarda zamu raba 50-50”.

   Kafaɗa ta maƙe masa tana mar-mar da idanu da tura baki gaba. Fuskarta a shagwaɓe ta ce, “Naƙi wayon sai dai na baka 30 na ɗauka 70”.

       “Tunda na fara jin tsoronki ko?”.

  Ya faɗa cikin ɗage gira sama. Baki ta ɗan murguɗa masa itama. “To dama ai tun tuni tsorona kake ji”. Murmushi ne ya suɓuce masa, shi baima san yanda zaiyi da tsiwar yarinyar nan ba. Fitinanniyar yarinya ce ta bugawa a jarida, yara uku har yanzu bata san ta girma ba. Hannayensa ya tura cikin aljihunsa wandonsa har yanzu fuskar tasa da murmushi ya nufeta. “Okay shikenan na yarda 30-70 ɗin, sai dai yanzu yarana najin yunwa zo muje a fara cin abinci amma da sharaɗi”.

       “Nami?”.

   Ta tambaya tana matsawa da baya-baya. Tana ganin ya kusa isa inda take tai yunƙurin sake zurawa da gudu. Wani ɗan tsalle yayi ya cafkota, bai saurari ɗan ihun da take masa na taɓara ba ya murɗe hannun ya amshe ɗan box ɗin dake cikin hannun nata. Cak ya ɗagata ta shiga watsal-watsal da ƙafa. Dariya ya shigayi ganin yanda take kukan taɓara da faɗin ita sai ya bata abunta. Sai da ya zauna akan kujera ya ɗaurata a kan cinyarsa sannan ya dungure mata kai da faɗin, “K yarinyar nan rigimarki tayi yawa, wai nida abuna”.

       Da sauri tace, “Nawa dai, dan 30 ne naka a ciki”.

         “Tun kan kiji sharaɗin nawa ma kin yanke hukunci”.

    “Ka faɗi sharaɗin mana banga wanda bazan iya ba”.

   “Okay haka kika ce?”.

“Eh”.

Ta faɗa cike da ƙarfin gwiwa. Murmushi yayi ya ce, “Okay muje a fara cin abinci mu dawo zamu gani ai”.


       ★Kamar ko yanda ya faɗa yaransu na zaune a falo zaman jiran fitowarsu. Balqeesa dake tsalle-tsallenta ita kaɗai da gudu ta nufesu, a hankali ya kai duƙe fuskarsa da ƙayataccen murmushi dan a rayuwarsa yana matuƙar ƙaunar yaransa, bai haɗa su da komai ba. Hakan kuma bai hanashi tsayawa akan tarbiyyarsu ba. Mulkin al'umma kuma bai hanashi shaƙuwa da su ba, rungumeta yayi tare da miƙewa da ita a hannunsa duk da kuwa takai shekaru shida a duniya. Cikin ƴar muryarta ta ce, “Abbie ina sonka kai da Ammie”.

     Idanunsa ya lumshe fuskarsa ɗauke da murmushi ya ce, “Muma muna sonku mai gadon zinari na”.

         Sosai yarinyar ta ƙanƙamesa tana dariyar jin daɗi. Kallon juna sukai shi da Iffah suna murmushi. Dai-dai nan Ajwaa da Ajwaad suka iso garesu suma. Yara masu nutsuwa da shiru-shiru kamar mahaifinsu. Suma hannu ya miƙa musu alamar suzo garesa. Fuskokinsu ɗauke da murmushi suka rungumesa. Baki Iffah ta zumɓira ita a dole taji haushi. Murmushi yayi itama ya mata alamar tazo. A hankali ta matso jikinsu tana murmushi ya haɗesu gaba ɗaya ya rungume........✍️




      *_🥱To nima dai na haɗaku gaba ɗaya na rungume masoyan albarka ababen alfahari. Alkairin ALLAH da rahamarsa da ni'imarsa sukai gareku ku da zuri'armu baki ɗaya._*



*ALHAMDULILLAHI🙏*


     

      _Ya rabba na gode daka kawoni wannan rana badan iyawata ba ko dabaruna. Ina roƙonka ka yafemin kurakuraina, abinda ya kasance dai-dai a cikin wannan ɗan littafi ya rabbi ka haɗamu a ladan. ALLAH ka amfanar damu amfanin cikinsa, wanda ya kasance mai cutarwa ALLAH ka hanashi tasiri a zukatanmu.🙏_



   Bazan gaji da faɗa ba. Rubutun nan nishaɗine. Fadakarwa ce. Wani lokacin ma harda ban haushi. Wasu abubuwan akan saka ne kawai domin ayi nishaɗi. Ina roƙonku yin watsi da duk abinda bamai amfani ba a ciki.


    _Mungode! Mungode!! Mungode masoyan Zafafa. Alkairin ALLAH ya kai gareku, yanda kuka kasance damu kuma ALLAH ya kasance daku cikin rahama da amincinsa. Yanda kuka somu domin ALLAH kuma ALLAH ya soku haka❤️❤️🙏_



      *_Yanda muka fara lafiya muka kammala lafiya ALLAH ya haɗamu ana gaba cikin lafiya da nutsuwar zukata. Wanda duk naima kuskure ko ba daidai ba dan ALLAH ya yafemin a yayin wannan rubutun ajizanci ne banda burin ƙuntata kowa koda da magana ne🙏. Ngd Ngd sosai masoya ƴan DAUƊAR GORA CONVERSATION, ku ɗin na dabanne a cikin daban gareni. Alkairin ALLAH ya kasance daku a duk inda kuke. Ku na dabanne a zuciyar Bilyn Abdull 😘😘Nikam kune Sohaas ɗina TAURARINA⭐._*




*Bilyn Abdull ce 😘😘🙏*



*_ƙaunarku nake irin trillions ɗin nan🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰😘😍😘😘_*


_🙈🙈Yau sunan magena har yanzu banga kun fara kawo kayan Barka ba 😂😂 fa. Bye bye idan na mutu da ga nan kowa ya yafe min🙋🏻‍♀️🙋🏻‍♀️🙋🏻‍♀️😭🙏🏻_





   

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*


*DAUDAR GORA Billyn abdul*


*KI KULANI hafsat xoxo*


*A RUBUCE TAKE Huguma*


*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*


*IDON NERA Mamuh ghee*



_LITTAFI DAYA: 400_

_LITTAFI BIYU: 600_

_LITTAFI UKU: 800_

_LITTAFI HUDU :1000_

_LITTAFI BIYAR: 1200_


_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_


_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_


_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_


_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_


_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_


_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_


ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN


MARYAM SANI

ACCESS BANK

0022419171


SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 


09033181070


IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA


09166221261


*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*


+227 96 09 67 63


Books biyar  1250CFA

Books hudu  1050CFA

Books uku  850CFA

Books biyu  650CFA

Bookk daya  450CFA


KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.


MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post