π™π™π™π˜Όπ™ π˜Ώπ˜Όπ™‰π™†'π™Š.....!! π‘©π’Šπ’π’šπ’ 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆 π‘ͺ𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4

π™π™π™π˜Όπ™ π˜Ώπ˜Όπ™‰π™†'π™Š.....!! π‘©π’Šπ’π’šπ’ 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆 π‘ͺ𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4

 

π™π™π™π˜Όπ™ π˜Ώπ˜Όπ™‰π™†'π™Š.....!! π‘©π’Šπ’π’šπ’ 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆 π‘ͺ𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4

π“π²π©π’π§π πŸ“²

  πŸ«— π™π™π™π˜Όπ™ π˜Ώπ˜Όπ™‰π™†'π™Š.....!!πŸ«—

           π‘©π’Šπ’π’šπ’ 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 π’„π’†πŸ€™πŸ»

π‘ͺ𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣

........Idanun dattijuwar cike da Ζ™walla ta amsa mata da girmamawa. A haife ta haifeta, bama ita ba har wadda ta fita, amma sam bata Ι—aga Ζ™afa wajen cimata zarafi. Wai a hakan ma itafa da sauΖ™i, dan a kaf masu aikin gidan ita kawai ta yarda ta shigo mata Ι—aki ta gyara kota dafa mata abinda zata ci, hatta key Ι—in Ι—akin ita kaΙ—ai ta bamawa amma ko momynsu bata da shi. Rigarta ta kama ta shinshina, babu abinda take sai Ζ™amshi amma ta ce mata tana warin zufa. “ALLAH ya shiryeki Ζ΄arnan” ta faΙ—a cikin tausasawa tana Ι—auke Ζ΄ar Ζ™wallar da suka cika mata ido. Dan duk da wulaΖ™ancin da Lulu ke mata tana Ζ™yautata mata, zata iya cewa duk abinda ta samu na cigaba a aikin nan nata sanadin Lulu ne, ba ita kawai ba hatta Ζ΄aΖ΄anta dake Ζ™auye da Ζ΄an jikokinta suna ci da ga alkairin Lulu, barta dai da shegen rashin mutunci, dan in har zakai lissafin masifaffun mutane a rayuwa to indai Lulu batazo ta farko ba tazo ana biyu. Bata da kirki sam, kuma bata ragama uban kowa sai Daddy da Uncle Yousuf, wani lokacin ma Uncle Yousuf Ι—in ne ya Ι—an fi cin nasararta, dan shi har faΙ—a yakan Ι—an mata da nuna mata kuskure idan tayi, amma Daddy shi komai tayi ma dai-dai yake koda kuwa ba dai-dai Ι—in bane ba....


  Wannan kenan


         ∆•••••∆ ★ ∆•••••∆


     Da ga airport babban kamfanin JiΖ™amshi's ya nufa ransa a Ι“ace. Kai tsaye ofishin Uncle Yousuf yay ma tsinke, sai dai yayi rashin sa'ar samunsa da ga bakin sakatariyarsa. Bayajin zai iya Ζ™ara minti biyar a wajen, dan haka ya ajiye key Ι—in motar tare da amsar takarda a wajen sakatariyar yay Ι—an rubutu ya haΙ—a da key Ι—in. A takaice yace, “Ki bashi idan ya dawo”. Da ga haka ya juya yay ficewarsa. Da kallo ta bisa tana tsarkake sunan ALLAH. Ga dai namiji har namiji sai dai aljihu babu ko sisi. A hankali taja ajiyar zuciya da Ι—an taΙ“e baki...


      Shiko da bai san ma tanai ba tuni ya fice, a Ζ™ofar Companyn ya samu napep. Tsaki ya dinga ja a Ζ™asan maΖ™oshi har yanzu zuciyarsa na masa Ζ™una da kaikawon abinda ballagazar yarinyar can ta masa. Har abada shi *_Aliyu Haydar Mika'il Idris Mawashi_* baiga talaucin da zai sakashi zama ana Ζ™asΖ™antar da rayuwarsa irin haka ba. Zai iya jure kowace irin wahala da Ζ™arfin Ζ™wanjinsa amma ba Ζ™asΖ™anci ba. Shi ba kowa bane, amma har gaban abadan bazai iya zama a Ζ™arΖ™ashin takalmin kowa ba. Da'ace wannan yarinyar namiji ce yau wlhy sai ya kakkarya mata Ζ™asusuwa ya zubar da ita a airport Ι—in nan. Amma ta godema ALLAH data kasance Ζ΄a mace.....

         “Ɗan uwa wane layi muka nufa?”. Mai napep ya faΙ—a ganin har sun shigo cikin anguwar ta fage. Sauka kawai yay daga napep Ι—in maimakon amsa, ya zaro Ι—ari biyu a cikin aljihunsa ya miΖ™a masa. Bai jira mai napep Ι—in da ke faΙ—a masa baida canjin hamsin da zai bashi ba yay gaba abinsa..


       *_Aliyu M Idris Mawashi_* kenan da akafi sani da _Smart Mawashi_ yara da matasa na Ζ™asa da shi kan kirasa Uncle Smart. Abokansa kance Mawashi ko Smart guy, dan sune suka saka masa sunan dama saboda mutum ne mai matuΖ™ar nutsuwa da kuma himma akan komai ga kaifin basira. Ɗa na bakwai a gurin Malam Mika'il Idris Mawashi. Shekararsa talatin da huΙ—u a duniya. Yayi karatunsa na addini dana zamani har zuwa matakin masters. Bayan nan ma yayi wasu couses har biyu. Sai dai har yanzu aiki ya gagara garesa. Uncle Smart mutum ne mai matuΖ™ar nutsuwa, sannan babban hubby nasa a duniya shine Ζ™wallon Ζ™afa. Ya iyata matuΖ™a dan tun yana a secondary yasha ciwoma makarantar su wassani, bayan kammala sakandire Ι—inne ya samu nasarar shiga Kano pillars. Ya buga wasu manyan wassani da suka fara fiddo darajarsa da sunansa wa duniya, sai dai abin mamaki sai komai ya tsaya masa cak, ya zamto in har ya shiga fili domin buga Ζ™wallo sai ya yanke jiki ya faΙ—i sai an kamosa an maida gida kamar wanda ya mutu. Da yawan mutane sun fassara al'amarin da asiri, sai dai shi yaΖ™i Ι—aukar hakan da muhimmanci. Daga baya ma sai ya tattara Ζ™wallon ya ajiye ya koma makaranta bisa shawarar mahaifiyarsa. Duk da haka yakan Ι—an gwada yin Ζ™wallon amma dai ana nan jiya iyau, daya shiga fili sai dai a maidashi gida a sandare. A haka dai ya kammala karatunsa har yay bautar Ζ™asa ma, ya fara neman aiki amma yaΖ™i samuwa duk da takardunsa sunyi Ζ™yau matuΖ™a, abinda zai baka mamaki ma wani wajen har sai an Ι—aukesa daga baya sai suce ba haka ba. Shi mutum ne da ya tsani wulaΖ™anci dan yanada saurin fushi. Sannan mutum ne da baya Ι—aukar raini ga uban kowa duk tsananin wahala. Ya tattara aiki da Ζ™wallon Ζ™afa ya ajiye gefe ya shiga Ζ™oΖ™arin sana'a, sai dai anan Ι—in ma dai komai yaΖ™i zama. Gashi daya fara sai ALLAH ya sanya masa albarka amma abin mamaki sai komai ya tushe cikin Ζ™anΖ™anin lokaci al'amarin nasa dai kamar saka hannu. Yanayin rayuwar gidansu da ake ta kowa nasa ke son ya zama gwani ya sashi bai daina Ζ™oΖ™arin kamo can idan nan taΖ™i ba, a hakanne har takaisa ga samun aikin nan na driver a dalilin wani yayan abokinsa, badan yana so ba ya yarda zaiyi, sai dan tausayama mahaifinsu akan wahala da yay da su game da karatunsu amma a yanzu Ζ΄an uwansa babu mai taimaka masa daga su sai matansu da iyayensu mata. Dan matan Malam Mika'il Idris Mawashi huΙ—u ne cif, hakama Ζ΄aΖ΄a su talatin da biyu ne maza da mata. A yanzu haka wasunsu sunyi aure a mazan da matan, akwai kuma samari da Ζ΄ammata da suka rage musu har ma da Zawrawa biyu.........✍️


       


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*


FURAR DANKO

Billyn Abdul


-ZAFIN KAI

Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo


Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400


Pay atπŸ‘‡


1487616276 

Access Bank

Bilkisa Ibrahim Musa

Sai katura shedar biyanka ananπŸ‘‡


09018600202


Idan katin waya ne kuma saika tura ananπŸ‘‡

09033181070


Ζ³an Niger kuma ga naku. Kuyi magana ta wannan number Ι—inπŸ‘‡


+22799643131


VIPπŸ”₯πŸ’―

Zafin kai 3k

Furar danko 3k

Tabarmar kashi 3k

Bakon munafuki 3k


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*πŸ₯°

Zafafa🫢πŸ”₯




*_ALLAH ya gafartama iyayenkuπŸ˜­πŸ™_*

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post