Abban Sojoji Takun Karshe Chapter 96

Abban Sojoji Takun Karshe Chapter 96

 

Abban Sojoji Takun Karshe Chapter 96

Join this link to follow my tiktok acct👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1

قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖

*Father of soldiers

*🔥TAKUN ƘARSHE🔥

Na biya bash

Masu buƙatar littafin Suyi mun magana direct ta layina amma fa message ta whatsapp kawai,Ko an kira ba'za a samu ba, 08103884440


❤🤍❤


Tun wuraren ƙarfe Goma,Motarsu Abusufyan tayi dirar mikiya acikin jahar Kano,Da kanshi yake yin driving ɗinsu,Jahad na manne a kafaɗarshi tana sharar baccin da bata ƙarasa ba a gida,

  Tunda suka shigo cikin garin murmushi ya wanzu akan fuskarshi,Bakomai yake tunawa ba fa ce irin rayuwar da yayi acikin garin tun lokacin ƙuruciyarshi,

   "Jahad!ki tashi mun ƙaraso fa,"cike da farin ciki yayi maganar,

Sai da ya ambaci sunanta kusan sau 5 kafin ta amsa mashi,tare da miƙewa daga zaune tana yin hamma,ta cikin face mask ɗin dake a fuskarta,

  Buɗe idanuwanta tayi tare da juyawa tana ƙarewa garin kallo ta cikin glass ɗin Motar,hakanan ta dinga jin faɗuwar gaba rass!rasss!lokaci guda kuma tashiga tariyo abunda ya faru acikin rayuwarsu azamansu garin,


NASARAWA G.R.A


Shine Sunan Unguwar da hajiya Ameenatu Wato Gwaggon katsina tayi rayuwa acikinta tare da ahalinta,a hankali motarsu ta shigo cikin unguwar da matsakaicin gudu,A dai dai jerin wasu manyan gidaje na masu hali,Abusufyan ya tsayar da Motar a bakin gate,

   "Daddy wannan gidan wanene'?tayi tambayar tana kallon fuskarshi,

  murmushi ya ɗan yi tare da cewa"Wannan gidan da kike gani acikinsa nayi rayuwa tare da mahaifiyarku,Kuma anan kakan ku Marigayi baba buzu yayi gadi,Allah ya jiƙanshi da rahama,

  Amsa mashi tayi da Ameen,kafin suka fito daga cikin motar,

  "Allah sarki,Kullum idan nadawo a wancan lokacin,Baba buzu nake samu zaune saman benci yana dafa ruwan bununsa,da zarar ya hango motata zai fara yi mun kirari,Ya buɗe mun gate don in shiga daga ciki," acewar Abusufyan,

Jefi jefi mutane ke giftawa acikin unguwar,tun bayan da suka bar kano a lokacin baya,Mijin Gwaggon katsina ne ke zama a cikin gida kafin Allah yayi mashi rasuwa,Tun daga lokacin kuma babu wanda ya ƙara zaman gidan,ko Dr harris idan yazo kano ya kwammace ya kama hotel ya zauna acikinsa,

   Hannu ya zura acikin aljihunshi ya curo key ɗin gidan,Ya ƙarasa tare da zura key ɗin ajikin ƙopar dake manne da gate ɗin gidan,Wurin har ya fara tsatsa,ya ciccije daƙyar ya samu ya buɗe ƙopar,

  Ya ruƙo hannunta suka shiga daga ciki,

   Zuba ma gidan ido tayi tana kallonshi,A ranta tana ayyana irin rayuwar da mahaifiyarsu tayi acikin gidan,Ya haɗu duk da ginin Ya tsufa sosai,akwai fili sosai,Ga wurin buga ball nasu Abusufyan,Ga moto park,da sauransu,

Kaitsaye suka nufi Ƙopar da zata sadaka da Babban falon gidan,ita kuwa ta zuba ido tana ƙarewa gidan kallo,Uwar yanace ta ko'ina yayi datti,ga tarin ƙura musamman ajikin glass ɗin windows dana doors,

  Buɗe masu ƙopar yayi da key ɗin hannunshi,Yayi gaba tabi bayanshi,Kamar mai jin tsoro haka ta zura ƙafarta ciki,Matsakaicin falo ne,Yadda kasan bola,ledoji,yayi da sauran tarkace a kasanshi,Tiles ɗin kuwa duk yayi dirty kura ta rufe shi,Sofas ɗin dake a ɗakin duk sun gajarce sunyi ƙanƙanta,yadin jikinsu yayi diƙiƙi,

  "Daddy,ina ɗakin da Oumman mu tayi rayuwa acikinshi?ka nuna mun inaso naga ɗakin,"

  Da yatsan hannunshi ya nuna mata bedroom ɗin da abu tayi rayuwa,da sauri ta nufi ɗakin,shima yabi bayanta,A datse ƙopar ɗakin take amma babu key ajikinta,da ƙarfi yasa hannu ya turata,ji kake ƙiiiiiiii,ta buɗe a slow,

  Faɗawa cikin ɗakin tayi tana bin kayan cikinshi da kallo,labulayen duk sunyi ƙura,sun nannaɗe sun cukuikuye,Carpet ɗin bakin kofar ya fita hayyacinshi,Single bed ne acikin ɗakin,sai wardrobe ta bango,itama duk tayi ƙura,book shelve,Da dressing mirror da sauran tarkace,komai yafita hayyacinshi,

   Qur'ani ta hango saman bedside drawer ɗin gadon,

  Tun kafin tayi magana Abusufyan yace"Wancen qur'anin da kike gani na mahaifiyarku Ne,mace ce mai son addini tana ƙoƙari sosai,bata wasa da ibada,da haka ta sace mun zuciyata,"

  Hawaye ne suka soma sintiri akan fuskarta,ƙarasawa tayi gaban drawer ɗin ta sanya hannu tare da shafa al'qur'anin,ta kakka6e ƙurar dake akanshi,ɗago dashi tayi a hankali ta manna mashi kiss,

Kun Karanta wadannan jerin Littafan?

   "Daddy inason qur'anin nan sosai,zamu tafi dashi,"ta ƙarasa maganar tare da buɗe handbag ɗin dake hannunta,ta zura shi ciki,"

  School bags ta hango guda biyu,Anyi hanging ɗinsu a saman bango inda aka bubbuga ƙusa,

  Da sauri ta ƙarasa tare da kai hannu ta curo jakunkunan,ta sauko dasu ƙasa,ta zuƙunna tare da buɗe jakar,Littattafan addini ne cikinsu,Ahlari ne,Tajweed,Fiqhu,da sauransu,ɗayar jakar kuma da ta buɗe Littattafanta ne na boko da take zuwa school dasu,komai nata mai tsari,

  Abusufyan kuwa wurin wardrobe ɗin kayanta ya wuce,buɗewa yayi yana kallon jerin wasu daga cikin kayanta,Uniform ɗin  islamiyyarta ya ɗauko,tare da rungumesu a ƙirjinshi,Sae lokacin hawaye suka shiga zarya akan fuskarshi,

   Bazai ta6a mantawa ba,da rana ta farko daya fara sanyata acikin idanuwanshi,a lokacin tana kan hanyar dawowarta daga school,

   "Jahad,"ya ambaci sunan ta tare da juyawa yana kallonta 

  "Na'am Abba,tayi maganar tare da miƙewa ta ƙarasa gabanshi,

   "Kin ga waɗannan kayan,dasu ne na fara ganin Oummanku,Uniform ɗinta ne na islamiyya,"

  Murmushi ta saki tare da sanya hannu ta kar6i kayan,Rungumesu tayi ajikinta,Sae ta dinga jin tamkar Oumman tasu ta rungume,

  6ata lokaci sukayi sosai suna bincike acikin ɗakin Zainabu abu,

Daga bisani ne Yunwa ta fara kamasu gashi gidan babu abinci,Yanke shawarar zuwa nemo masu abincin yayi,ya barta acikin gidan,Gyara masu ɗakin oummansu ta shiga yi,Taci baƙar wahala sosai,Bayan ta share ɗakin har wanke shi tayi,A kitchen ta samu bokiti da ledar detergent,ga ruwa available,sosai ta wanke ɗakin sai ga tiles ɗin yayi haske sosai,Cire zanin gadon tayi ta ɗauko wani acikin wadrobe,Ta shimfiɗa masu bayan ta kakka6e gadon,ta goge jikinshi,


Hatta glass door din sai da tabi tayi scrubbing ɗinsu,ta goge yanar ɗakin,lokaci guda kamanin ɗakin suka canza,Komai na son gyara,Toilet ta shiga nan ma tataras dashi duk sai a hankali,sae da ta fara gyarashi fess,Sannan ta samu ta ɗan watso ruwa tare da ɗauro alwala,

  Darduma ta dauko cikin wadrobe ta shimfiɗata,ta kabbara sallar azhar,A tsanake tayi sallar tana kammalawa,agalabaice bacci ya ɗauketa saman dardumar,


Wuraren ƙarfe 2:30 Abusufyan ya shigo cikin gidan hannunshi ɗauke da Ledojin da yayi masu take away na restaurant,

  Da sallama ya shiga cikin falon,wuce wa bedroom ɗin yayi,ba ƙaramin mamaki yayi ba,ganin yadda Jahad ta gyara ɗakin tsaf,komai yayi fess,kamar lokacin da Zainabun shi na nan,

  Murmushi ya saki tare da samun wuri kasa gefenta ya zauna,Ya ajiye ledojin,Hannu yasa abayanta ya ɗan bubbugi kafaɗarta"Jahad!tashi muci abinci,"

  Firgita tayi ta farka tana Sambatu"Ya Rafayet,baisan na taho ba...,"

  Ƙiris ya rage yaji abunda tace,

Hannu tasa da sauri ta toshe bakinta,tana kallonshi,Shima kallon nata yake yi,

   "Me kika ce"?girgiza mashi kai ta shiga yi,tana faɗin"bakomai Daddy,Ashe ka dawo,nagaji ne shi ne na ɗan kwanta don in huta,"

  Murmushi yayi tare da cewa"Ae naga aikin da kikayi,kin yi ƙoƙari sosai,"

  "Bari na ɗauko mana plate,"ta miƙe tare da nufar hanyar fita daga ɗakin,

  Sai da tafito sannan ta dafe saitin zuciyarta tana faman sauke ajiyar zuciya,a ranta tace"Allah yaso daddy baiji abunda nace ba,dashi kenan zai gano ni,"_

Tayi maganar tare da yin saurin wuce wa cikin kitchen ɗin,A cikin kwandon wanke wanke ta samu tray da plates tare da cups,gaban basin taje ta wanke su tass da klin da soso,ta ɗaurayo su,bayan ta kammala wankesu saman tray din ta jera su,Ta ruƙosu a hannunta sannan ta dawo cikin bedroom ɗin,

  "Salamu Alaikum"Ta kwaɗa sallama ta shiga ciki,Zuƙunnawa tayi ta ajiye trayn agaban Abusufyan,

  Janyo ledar tayi ta buɗe,tare da sanya hannu ta curo fried meat(tsiren nama)ta jera masu shi asaman tray,hannu yasa ya taimaka mata wurin ɗauko sauran kayan,Cool Drinks ne da sauran kayan maƙwalashe,atare suka shiga ci suna fira gwanin ban sha'awa,bayan sun kammala cin abincin,Abusufyan ya tattara kayan abincin da sukayi amfani dashi,Ya wuce dasu kitchen yabarta zaune tana shan lemu,bayan ta shanye,ta sanya robar a dustbin,komawa tayi saman gadon ta kwanta,cikinta yayi haƙe² saboda cin muguntar da ta yi,wani baccin ne ya sake ɗaukarta,


*Boss Bature*


  ❤🤍❤


Wuraren ƙarfe 3 na rana Sgr ya dawo cikin gidan,Tun bayan da ya fita da safe Ko breakfast bai nema ba,saboda Emergency call ɗin da akayi mashi acan headquater ɗinsu,Jikinshi na sanye da Tank Top,light green,Tare da wandon kaki,Yayin da kunnanshi ke manne da wayarshi,Cikin harshen faransanci yake yin waya,

  Da sauri da sauri ya haye upstairs,direct ya wuce part ɗinshi,tunkan ya shiga ciki ya fara jin daddaɗan ƙamshi nakai mashi ziyara acikin hancinshi,gaba daya yayi tsammanin  cewa zai same ta ne a part ɗin nashi amma baiga Kowa ba Wayaam,Bedroom ɗinshi ya shiga,Shaf shaf ya rage kayan jikinshi ya faɗa cikin toilet,After some minutes ya fito waist ɗinshi ɗaure da towel,Yana tsaye agaban mirror yaji motsin mutun acikin falonshi,

   "Who's there"?yayi tambayar yana jiran amsa,

  "Sehrish ce,"

Ajiyar zuciya ya ɗan sauke tare da cewa"Come in,"

  Hannunta na ruƙe da tray na Lunch ɗinshi da ta shirya mashi,tana tafiya gabanta na faɗuwa rass rass 

  Sallama ta fara yi mashi ya amsa,kafin ta sanya ƙafa ta shiga ciki,sum sum ta lalla6a ta ajiye mashi tray asaman table,Jiki na rawa ta juya zata bar ɗakin,

  Zuba mata ido yayi ta cikin mirror yana kallonta,tana ƙoƙarin ɗaga ƙafarta tabar ɗakin taji ya Ambaci sunanta kai tsaye"JAHAD"

  DARAAAM!!!!!!Taji gabanta ya faɗi,sanƙamewa tayi atsaye,hankalinta a matukar tashe,tuni zufa ta shiga wanke mata fuskarta,Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya abakinta,Abun ya ɗaure mata kai,farat ɗaya Sgr ya gane cewa ba Sehrish bace,Hatta junaid yau bai ganeta ba,kowa ɗaukar sehrish yake yi mata,saboda sunsa ma ransu cewa da jahad aka tafi,Shiyasa basu natsu sun gane cewa itace ba,"

Download >>>> Daudar Gora book 2 complete Document

Download >>> A Rubuce Take (K'addarata) book 2 complete Document.


   Wata irin zufa ce ta shiga gangarowa asaman fuskarta,ƙiris ya rage ta saki fitsari a wando,

Slowly ya juyo tare da tunkararta,jikinta sae kerma yake yi,hannunta ya ruƙo tare da juyo da ita ta gabanshi ya kasance suna fuskantar juna,wuƙi wuƙi tayi mashi da idanu tana faman mazurai na rashin gaskiya,

   Abun ya ɗaure mashi kai,Wai harshi zasuyi wa wayau,kamar wani soko,An gaya masu cewa a banza yakai muƙamin da yake dashi a yanzu,

   goya hannayenshi yayi asaman wide chest ɗinshi,Ya zuba mata ido yana kallon Ikon Allah,

   Saboda tsabar rashin gaskiya tun kafin ma yayi mata magana,murya na kerma tace"Amm...um..babban..yaya pls dan Allah kayi haƙuri ka yafe mun,Wayyo Allahna na shiga uku,"a ruɗe tayi maganar,tana yarfa hannuwanta,tsoranta kada ya kwashe ta da mari,

  Ruke ha6arsa yayi cike da mamaki yake kallonta from head to toe,

   Hawaye ne suka soma shararowa akan fuskarta,tun kafin ma taji hukuncin da zai yanke mata,Zuciyarta sae bugawa take yi ba ƙaƙƙautawa,

   "Where's she"?fuskarshi a ɗaure yayi tambayar,

  Sunnar dakai tayi kamar munafuka,daƙyar ta iya buɗe baki tace"Wlh baban yaya ni bani nace ta tafi ba,yau ne dama da asuba,ta same ni cikin damuwa take tambayata lafiya shi ne na sanar da ita cewa Ni banso nabi Daddy kano,bansan zuwa garin saboda abunda ya faru damu acikinshi...."

  Tunkan ta ƙarasa maganar yace"What!tafiya tayi without My Permission,"ranshi a matuƙar 6ace yayi maganar,

  "Ya salam"ya furta hakan tare da zura hannunshi cikin sumar kanshi,

Ya runtse idanuwanshi,

"Am sorry,babban yaya bazan ƙara ba,"_

Jinjina kanshi yayi tare da ware idanuwanshi akan fuskarta,yana kallonta duk tabi ta susuce,

   "Kin iya frog jump ko"?

Waro ido tayi tana kallonshi,girgiza kai tashiga yi alamar a'a,

...ruko hannunta yayi ya fito da ita cikin falonshi,fuskarshi a daure yace"Oya,start from here,karki kuskura ki tsaya,if not zaki ga abunda zai biyo baya,"

   Jahad tamkar zata fashe da kuka,Zuƙunnawa tayi tare da kama kunnanta kamar ɗan kwaɗo haka tafara yin tsallan tana zagaye kujerun,tun a first round jikinta ya fara gaya mata,Komawa yayi cikin bedroom ɗinshi ya ɗauki wayarshi daya bari agaban Mirror,Numbar Uncle Abusufyan ya lalubo,ya danna mashi Call,


A lokacin Abusufyan,Na acikin kitchen ya tu6e rigarshi daga shi sai shorts,ya dage sai aikin goge goge yake yi da ƴan wanke wanke,ya gyara kitchen ɗin tsaf,

  Fitowa Sehrish tayi hannunta ruƙe da wayarshi,har tuntu6e take yi wurin yin sauri donta kai mashi wayar,tana baccinta mai daɗi ringing ɗin wayar shi ne ya tashe ta,


"Daddy,ana kira,"ta ƙarasa maganar yayin da take shiga kitchen ɗin,hannu abusufyan yasa ya kar6i wayar,duba screen din wayar ya fara yi,

   *My first in-Law* Shi ne sunan daya bayyana akan screen ɗin,Yayi mamakin ganin kiran Sgr,Picking call ɗin yayi ya kara wayar a kunnanshi,

   "Assalamu Alaikum"

On the other hand,Sgr ya amsa mashi"Wa'alaikum salaam,Uncle kun isa Lafiya"?

.  "lafiya Lou,ae tun ɗazu muka ƙaraso,"

   "Okey,inason magana da sehrish ne,tana a kusa"?

   Murmushi abusufyan yayi tare da cewa"Ae bada ita muka zo ba,ko ka manta ne?

   "Uncle,Da ita ka tafi bada Jahad ba,yanzu haka jahad tana a part dinta,Sunyi musaya ne,"

  Cike da mamaki abusufyan yace"Jahad tana a gida!"

  Gaban Sehrish ne ya faɗi rass,wuƙi wuƙi tayi da ido,ɗagowa abusufyan yayi tare da kallonta,Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,sai lokacin ya shaida cewa Sehrish ce,ya ɗauko amatsayin Jahad,Ko ya akai suka shirya Wannan batare da kowa ya ankara ba,

  Sunnar dakai ƙasa tayi,ganin irin kallon da daddynsu yake yi mata,

  Rai a6ace ya miƙa mata wayar"Kar6i nan,"

  Hannunta na kerma ta kar6i wayar,hankalinta a matuƙar tashe,ta sanya wayar a kunnanta,muryarta tamkar zata yi kuka tace"Ya rafayet........"

   Tunkan ta ƙarasa maganar ya daka mata tsawa"Shut up!"nan take ta shiga taitayinta,

    "da iznin wa kika bar garin nan"?_

  Idanuwanta ne suka cicciko da kwalla,Sae faman kallon uncle take yi,sam baiji daɗin abunda sehrish tayi ba,don yasan ƙarshe kanshi abun zai ƙare,

   "Am sorry ya rafayet,dan Allah kayi haƙuri,Bazan ƙara ba,"

  dogon tsoki yaja,Kafin yace"Come back home,In ba haka ba,Ranki zai 6aci,"yana faɗin hakan yayi rejecting kiran,

  Fashewa tayi da matsanancin kuka,

Hannu abusufyan yasa ya kar6e wayar,

  "Koma meya laifinki ne!Ashe baki da hankali Sehrishi!Why kike son Jamin ina zaman lafiyana?,Taya zaki kamo hanya batare da iznin Mijinki ba,?"

   Cikin shesshekar tace"dan Allah daddy,kayi haƙuri,na kwallafa raina ne akan son zuwa,nasan nayi laifi,Kuma nayi danasanin yin hakan,Amma dan Allah daddy,Ka roƙan mun alfarma a wurinshi,Yabarni in zauna,Saboda yace in koma gida yau ɗin nan,"ta ƙarasa magana tare da sanya hannu tana share hawayenta,

  "I can't Call him Sehrish,rafayet bazai saurari kowa ba a halin yanzu,Kawai kije ki shirya kayanki,in kaiki tasha ki hau mota,"

Jin haka yasa ta ƙara fashewa da matsanancin kuka,tana faɗin"dan Allah daddy,kada ka mayar dani,Nashiga ukuna,"

  Sosai take kuka,Shi kanshi ya tausaya mata,duk yadda take shakkar Sgr amma ta kama hanya ta baro gidan batare da izninshi ba,tabbas ba ƙaramin son zuwa takeyi ba,

   Muryarshi a sanyaye yace"Kiyi hakuri daughter,babu yadda zamuyi dole ki bi umarnin Mijinki,lokaci yana ƙurewa,ki je ki shirya kayanki,mu tafi tasha,"

  Juyawa tayi da gudun gaske,Ta koma ɗaki,Saman gadon ta faɗa tare da fashewa da wani sabon kukan,


Jikin abusufyan ba ƙaramin sanyi yayi ba,yaso ace akwai wata hanyar da zai iya taimaka mata,don ta zauna a kanon,Amma ba halin yin hakan,

  yana cikin wannan zancen zucin wayar shi ta shiga ruri,da sauri yakai idonshi kan wayar dake hannunshi don yaga mai kiran nashi,Sunan Yaya Hossein ne ya bayyana akan screen din wayar,

  Da sauri ya answer kiran ya kara wayar a kunnanshi"Assalamu Alaikum,Yayana na kaina"_

  On the other hand,Abba yace"wa'alaikum salam ƙanina na kaina,Ya kake fatan kun isa kanon lafiya,"

  Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Mun ƙaraso tun wuraren goma,"

  Abba yace"Madallah,naji daɗi sosai,kai dawa kuka tafi ne"?

   Shiru ya ɗanyi yana tunanin halin da sehrish take ciki,ranshi ne ya bashi cewar Ya sanar ma Yayan nashi,May be ya iya dakatar da Sgr ɗin,

   Calmly ya soma magana"Ya hossein,Wlh an samu matsala,Da jahad na shirya tafiya,bansan ya akai ba,su ka yi musaya ita da sehrish,dama ta kwallafa rai akan son zuwa kano,To yanzu haka zancen da nakeyi maka,Muna tare da Sehrish ɗin,Kuma Sgr ya gane cewa da ita muka zo kano,ya bada umarnin ta koma yau yau ɗinnan,baiwar Allah tana cikin damuwa,yanzu haka tana can tana kuka,"yaƙarasa jawabin yana jiran jin amsar da abba zai bashi,

   "Kada ka damu,Ka lallasheta ta kwantar da hankalinta,Ni zanyi mashi magana,duk yadda mukayi dashi,in sha Allah i will inform you,"_

  Ajiyar zuciya abusufyan ya sauke tare da cewa"Nagode sosai,Yayana nakaina Allah yabar zumunci atsakaninmu,"

   "Ameen Ameen,ƙanina,"abba ya amsa mashi before suyi sallama,

   Har hankalinshi ya ɗan kwanta duk da yana zullumin amsar da abban zai bashi,don yasan halin Sgr wani lokacin idan ya burkice,mai tankwarashi sae Allah,


A lokacin da kiran abban ya shiga wayarshi,Yana zaune asaman sofa,ya aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,Yana sanye cikin jeans da t~shirt,yayin da jahad ke zukunne agabanshi,Tayi kneel down fuskar nan tayi jaga jaga da ita,tasha kuka har ta gode wa Allah,

   Hannu yakai tare da ɗaukar wayar dake ajiye saman front table din gabanshi yayi picking call ɗin,tare da kara wayar a kunnanshi,Ya furta"assalamu alaikum,"

   Acan 6angaren abba ya amsa mashi"Wa'alaikum salaam,My son ya kake ya gida,ya kuma aiki"

   "Alhamdulliah"

Abba yace"Yawwa,Rafayet dama game da yarainyar nan ne,Sehrish,"tunda yaji ya ambaci sunanta,Ranshi ya bashi cewar sunkai ƙararsa ne,

    "Dan Allah rafayet,ka ƙyale yarinyar nan ta zauna,ba jimawa zasuyi acan ba,Yarinyar nan ta kwallafa rai akan son zuwa can shiyasa harta tsallake ta tafi ba tare da saninka ba,Amma kai shaida ne akan yarda takeyi maka biyayya sau da ƙafa,duk wani abu da zai 6ata maka rai,tana ƙoƙari don taga ta faranta maka rai,pls rafayet ta ci albarkacin wannan,"

  shiru yayi batare da yace komai ba,

  Har sai da abban ya sake cewa"Rafayet naji kayi shiru,"

  Ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa"its Okey daddy,na haƙura,"Yanayin yadda yayi maganar,bada son ranshi ba,

   Muryar abba ɗauke da farin ciki yace"Ko kaifa,Wlh har naji daɗi acikin raina,Allah yayi maka albarka "

"Ameen"daƙyar ya iya furta hakan,Sallama su kayi ya janye wayar daga kunnanshi,

  mayar da idanuwanshi yayi kan jahad yace"U can go" 

  Miƙewa tayi tana faman ɗangyasa ƙafarta,tabar falon nashi,ba ƙaramin jiki taji ba,Saukowa tayi downstairs tana cigaba da yin shessheƙar kukan,

  adai dai lokacin junaid ya faɗo cikin falon,Tsayawa yayi yana kallonta,ƙarasawa yayi da sauri wurinta yana faɗin"rishi lafiya meya faru"?

...ɗagowa tayi da idanuwanta waɗanda sukayi ja saboda kukan da tasha,Waro idonshi ya ɗanyi tare da ambaton sunanta"JAHAD"

   Cikin shesshekar kuka ta amsa mashi"Na,am"

   Hannu yasa ya tallabo fuskarta,"Dama bada ke aka tafi kano ba"?

  Jinjina mashi kai tayi alamar eh,sannan tace

"Tare da sehrish aka tafi,amma dani muka shirya tafiya,Shine mukayi musaya ni da sehrish,yaya rafayet ya gano ni,Shine ya hukunta ni Hada tsallan kwaɗi ya sani,"

   Hannuta ya ruko,tare da samun wuri saman sofa suka zauna,

   Ranshi aɗan 6ace yace"Allah dana son da haka bazan bari Babban yaya ya sanyaki yin tsallan kwaɗi ba,Meyasa zai sanya juliet ɗita,Aikin wahala,'?

   hannu yasa yana share mata hawayen dake sauka akan fuskarta,cikin lallashi yace"stop crying my juliet,Allah in baki daina zubar da hawayenki ba,Nima zan fara kukan,".  

  Cike da zolaya,ya sanya hannunshi yana murza idanuwanshi,kamar zaiyi kukan,

  Da sauri ta ruƙo hannunshi tana faman sauke ajiyar zuciya tace"Nadaina".

  murmushi ya saki tare da cewa"Yaushe zamu fita yawo?Da anjima ko gobe"?

  Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Mu bari sai gobe,Yanzu har la'asar tayi,Nafiso mu fita da wuri,mu zaga garin nan,"

   "Yadda kikeso haka za'ayi,"ya karasa maganar,tare da kai la66ansa zai sumbaci gefen fuskarta,Karaf idanuwanshi suka sauka akan na SGR dake ƙoƙarin saukowa downstairs,da sauri ya janye la66ansa,ya shiga ƴan kame kame,

  girgiza kai kawai sgr yayi don yaga abunda junaid ɗin ke ƙoƙarin yi,Fita yayi daga cikin falon batare daya tanka masu ba,


   

*Boss Bature*


*Sehrish*


hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba,jin cewa an barta ta zauna a kanon,taji daɗi sosai acikin ranta,duk da tana fargabar hukuncin da Sgr zai yanke mata idon suka koma gida,


Bayan sallar la'asar,Suka shirya tsaf domin zuwa hotoro,Unguwar da sukayi rayuwa a cikinta,Abusufyan ne ke driving ɗinsu,tana zaune a gefenshi tana latse latsen wayarta,Yayin da can ƙasan zuciyarta ke cike fal da fargabar zuwa anguwar,A hankali Motar ta shararowa da matsakaicin gudu,izuwa cikin unguwar bai direta a ko'ina ba sai a ƙofar gidansu,don bai manta da kwatancen gidan ba,duk da yaɗan so ya ruɗe saboda sabbin gine ginen dake a wurin,kasa fitowa sehrish tayi daga cikin motar,Saboda yanayin da tashiga,ta tsani yin toxali da unguwar,Saboda bata son duk wani abu da zai tuna mata rayuwarsu ta baya,


Fitowa abusufyan yayi daga cikin motar ya zagaya,ya bude mata ƙopar,"Daughter,mun ƙaraso fa,"jiki asanyaye ta fito daga cikin motar,yayin da idanuwanta ke cike tab da kwalla,A wani slow ta wurga kwayar idonta akan gidajensu,Ginin ya tsufa sosai,duk fentin ya ƙoƙe,ya gajarce,An garƙame gidan da ƙaton ƙwaɗo,duk yayi tsatsa,da alama anjima ba'ayi amfani da gidan ba,mayar da idanuwanta tayi akan gidansu maman sadeeq,A rufe yake gidan da makulli,Gidan ya tsufa shima Amma bai kai gidansu tsufa ba,saboda an canza mashi fenti,


Hawaye ne suka soma shararowa akan fuskarta,juyawa ta ɗanyi tare da kallon abusufyan dake tsaye,jikinshi duk yayi sanyi,Saboda tunawa da wasu abubuwa da suka faru a rayuwarshi,

  Mutanen dake kai komo acikin Layin nasu sai faman leƙensu sukeyi,musamman ƴan yaran anguwar,

  "Daddy,Kamar basu nan fa,naga gidan a rufe,"

  Uncle yace"Bari na samu yaro na tambayeshi,Muji ko sun tashi ne,"

  Yana ƙoƙarin rufe bakinshi,Yaji anyi mashi sallama ta bayanshi,Muryar wani dattijo ne,juyawa yayi tare da kallon mutumin,tsoho ne amma ba irin tukuf ɗinnan ba,jikinshi na sanye da koɗaɗɗen yadi,ƙafafunshi na sanye da wasu siɗaɗdun silifas duk sun fita hayyacinsu,kamar mahaukaci,

   Da sauri abusufyan ya miƙa mashi hannu donsu gaisa,

 Dattijon ya maƙe hannunshi tare da cewa"Haba Alhajin Allah,baka ga yadda hannuna yake ba duk datti a haka zaka gaisa dani,"

  Murmushi abusufyan ya sakar mashi,"dan Allah kada ka hanani gaisawa dakai,"

  Mika mashi hannun tsohon yayi suka gaisa,Sannan yace"bawan Allah,ban ta6a ganinka acikin unguwar nan ba,Kuma da alama kamar wani ku ke nema ko"?

  abusufyan yace"ƙwarai kuwa,wannan Ƴa tace,Munzo daga abuja ne,Muna neman..umm....."bai ƙarasa maganar ba,saboda ya manta da sunan mutumin,

  Sehrish ce ta ƙarasa mashi maganar"Malam nura muke nema,malamin makarantar islamiyya,"

  Dattijon yace"Ae nan ne gidan shi,Sae dai kash,Sunyi tafiya zuwa kankia wurin jana'izar Wani kawunshi daya rasu,"

  Jin haka yasa yanayin fuskar abusufyan ta ɗan canza,zuwa damuwa,

  "Amma,tun yaushe suka tafi"?

  Dattijon yace"tun makon daya gabata,Amma jiya munyi waya dashi ya sanar dani cewa Yau ko gobe zasu dawo,"

  Ba ƙaramin daɗi suka ji ba,don har sai da abusufyan ya ɗanyi murmushi,

  Hannu yasa cikin aljihunshi ya zaro kuɗi sababbin ƴan dubu dubu kusan dubu goma sha biyar ya miƙa ma dattijon,

Washe baki tsohon yayi tare da sanya hannu biyu ya kar6i kuɗin,tare da cewa"yalla6ai kamar ka sani wlh yau gidana da yunwa muka tashi,yara sai kuka sukeyi,Hakanan na gaji da zama cikin gidan, nace bari na fito na nemi na abinci,Ashe arziƙi ne ke kirana,Allah na gode maka,da ka haɗani da wannan bawan naka,Ya Allah kamar yadda ya farantamun rai,kaima ka faranta mashi nashi,ka biya mashi buƙatunshi na alkhairi,'yana addu'ar hada ƴar kwalla akan fuskarshi,

   Atare suka dinga haɗa baki suna Amsa mashi"ameen ameen,

  Abusufyan yace"baba taimakon da zakayi mana,idan sun dawo dan Allah ayi gaggawar sanar damu,Bari na baka lambar wayata,

  Ya ƙarasa maganar tare da zura hannunshi cikin aljihun wandonshi ya ɗauko wayarshi,

  Hannu dattijon yasa,a gaban aljihun rigarshi,Ya curo ƴar ƙaramar wayarshi tecno,taji jiki duk tafita hayyacinta,miƙa ma abusufyan wayar yayi"kar6inan yaro,sanya mun numbarka,kayi mun saving ɗinta da sunan Mai mutunci,Zanfi ganewa,Da zarar sun dawo in sha Allah,bi'iznil lahi,koda ƙarfe ɗayan dare ne zan kira in sanar dakai,"

  Murmushi suka saki gaba ɗayansu,kar6ar wayar abusufyan yayi,madannan jikinta duk sun nutse ciki,daƙyar ya samu ya rubuta mashi numbar,yayi mashi saving da Mai mutunci,Sanna ya mayar mashi da wayar"Gashi baba,mun gode sosai,Sai naji ka,Allah yasa adace,"

  Tsohon ya amsa mashi da ameen ameen,ae tunda ka farantamun raina,Kaima sai Allah ya faranta maka naka,har addu'a sai nayi maka idan nayi sallah,

  "Ina godiya sosai,"ya karasa maganar tare da ruƙo hannun sehrish suka shige cikin mota,key yayi ma motar,a hankali yayi reverse,tare da karya kwana,da gudun gaske ya fuce daga cikin unguwar,

  Nasarawa suka koma,a bakin gate din gidan ya sauke sehrish,Saboda zuwa masallaci,An fara kiran magrib,Miƙa mata key ɗin gidan yayi"kar6i nan,ki rufe gidan da kyau,Bazan dawo da wuri ba,Saboda inaso naje nayi mana siyayyar kayan abinci,dana amfani,"_

  "Toh daddy adawo lafiya"tasa hannu ta kar6i key din,kafin ta juya ta nufi cikin gidan,tsayawa yayi acikin motar yana kallonta,har saida ta 6ace ma ganinshi,ya tabbatar da ta rufe ƙopar gidan,Sannan ya tashi motar ya fuce,


   A 6angarensu Aunty babba kuwa,basu isa Enugu ba sai wuraren ƙarfe sha ɗaya na dare,Sunsha uwar tafiya,ba ƙaramin jiki suka ji ba,Acikin garin suka kama ɗaki a hotel,Tunda suka shiga ɗakin,kowaccensu ta baje saman gadon ɗakin,suka shiga sharar bacci kamar wasu matattu,Ga uwar yunwa na cinsu,sai da sukayi bacci mai isarsu,Kafin suka farka neman abunda zasu sama cikinsu,Oder sukayi aka kawo masu lafiyayyan abinci,kamar wasu kuraye haka suka tasarwa abincin suna Ci,Sai da suka ci suka ƙoshi,tukunna suka koma saman gadon,Suka dasa wani sabon baccin,ba tunanin yin sallah,a ƙagare suke washe gari yayi su wuce cikin dajin,

*Boss Bature*

   ❤🤍❤

Har Wuraren ƙarfe 12,Abusufyan bai dawo cikin gidan ba,gashi yabarta ita kaɗai,da farko bata damu ba,falo ta dawo ta zauna saman sofa,daya ke akwai nepa,hasken globe ya gauraye ko'ina,hannunta na ɗauke da littafin oummansu tana karantawa,Kalaman soyayya ne acikinshi,a cikin drawer ta samu littafin,Wani page ta buɗo acikin littafin Sunan oummansu ne akai dana Ya sayyadi,Aikuwa rai a6ace ta sanya hannu ta yage takardar tare da yin wurgi da ita,Mayar da hankalinta tayi sosai akan littafin tana karanta love messages ɗin dake aciki,da zarar taga wanda ke ɗauke da sunan ya sayyadi,jikinta har rawa yake yi wurin sanya hannu ta yage shi,

Tana cikin wannan karance karance,kwatsam!Aka ɗauke da wutar nepa,nan take duhu ya gauraye ko'ina,babu haske ko misƙala zarratin,gashi ta baro wayarta saman drawer cikin ɗakin,Sanin kanku ne sehrish muguwar matsoraciya ne,Tuni ido ya raina fata,Hankalinta yayi mugun tashi,jikinta ya shiga yin kerma,kamar gunki haka ta ƙame a zaune ta gaza motsawa,tana cikin wannan yanayin na tashin hankali,Tajiyo takun takalmin mutum,A matukar tsorace ta shiga ambaton sunan Daddynsu da ƙarfi"Daddy!daddy!dan Allah kana ina,nashiga uku,'

  Gabanta ne ya fadi lokacin da ta tuna cewa,daddynsu da Motarshi ya fita,da ace shine ya dawo cikin gidan to tabbas zata ji sautin ƙarar shigowar motarshi,

   Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,jin motsin mutumin na tunkarota,a razane ta saki littafin dake a hannunta,ta miƙe daga saman sofa ɗin tashiga ja da baya,tana tafiya saɗaf saɗaf,hawaye duk sun wanke mata fuskarta,zuƙunnawa tayi ta soma yin rarrafe a hankali tana ƙoƙarin gano ƙopar ɗakin oummansu,cikin rashin sani takai hannunta saman wani gwangwanin maltina,aikuwa ya bada wani irin sauti rakwakwas,a gigice sehrish ta miƙe,gudu gudu sauri sauri,ita kanta batasan inda zata tunkara ba,Unfortunately tayi tuntu6e da wani abu,gaba ɗaya ta tafi zata faɗi ƙasa,ta saki wata irin razananniyar ƙara,

  Sai dai kafin takai ƙasa,Taji an damƙi qugunta,kwakkwaran ruƙo akayi mata,kafin aka janyota da ƙarfi,ta faɗa saman ƙirjin mutumin,koma waye wannan ba ƙaramin mutun bane,ƙarƙarfan gaske,

  Tashin hankali domin son sanin wanene wannan mutumin,Mu haɗu gobe inda rai da lafiya,In Allah yasa muna da rabon ganinta kenan


Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post